Sashe 88
Furar Danko Part1 Compete Hausa Novel · about 5 min read
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 7️⃣1️⃣
........Tana fitowa ɗauke da dankali ya fuske kamar bashi ba ya cigaba da game ɗin yana satar kallonta ta gefen ido. Ganin ta fara firar dankalin ya sashi ajiye wayar tasa a table ɗin ya miƙe, gefenta ya tsaya kaɗan, ya ɗauka wuƙar data ajiye saman chopped board ya fara yanka wanda ta fere, bata kulashi ba, ba kuma tayi magana ba ta cigaba da ferewa tana ajiye masa. Shima sai baiyi magana ba ya cigaba da yankawa, idan ya ɗan tara sai ya zuba a cikin ruwan data ajiye a bowl. A haka har suka kammala, kasancewar ta rigashi gamawa ita ta fara barin wajen ta ɗakko preyn fan ta dawo inda yaken ta zuba ruwan sabulu kaɗan ta wankesa da soso ta ɗaureye duk yana satar kallonta. Komawa tai gaban gas ta kunna ta ɗora sannan ta zuba man data ɗakko. Dai-dai nan ya kammala, sai ya wanke mata dankalin ya sake masa ruwa ya tace sannan ya juyo yana miƙa mata robar. Sai da ta hararesa ta amsa, shi dai ya gimtse dariyarsa da ƙyar ya juya yana ɗauraye wuƙa da sauran abinda sukai amfanin. Lulu kam koda albasanta ya soyu ta zuba dankalin sai ta nufi frizzier, kifi tai ƙoƙarin cira sai dai sanyin da ya ratsa mata hannu ya sata faɗin, “Ouchh!!”. Juyawa yay yana kallonta, ganin yanda take yarfe hannun ya sashi nufarta, hannun ya riƙo ya saka cikin nashi ya rumtse ɗumin nasan ya ratsata, sai kuma ya jawota gaban fanfo ya kunna ruwa ya ɗauraye mata hannun, sannan ya jawo ƙaramin towel ya saka mata hannun ciki. Komawa yay ya ciro kifin har biyu masu ɗan girma ya dawo ya wanke su sannan ya dubeta, ɗauke kanta tai da ga kallon gefen ido da take masa. Shiko da ba lura yay ba ya ce mata “Yankawa zakiyi?”.
Ƙaramar harara ta sakar masa da tura baki gaba sannan tace e.
“Kai dai Aliyu kana shan harara wlhy abin tausayi”. Ya faɗa yana yanka kifin. Hararar tasa ta sake yi da matsawa gaban dankalinta ta da ke cikin mai......
Kusan a tare sukai aikin, sai dai itace ke girkin shi kuma yana taimaka mata da yanka miƙo, duk da dai ba itace ke cewa yayi ɗin ba. Ya shiga matuƙar mamakin ganin yanda take girkin dama yanda tayisan, dan harga ALLAH bai kawo ta iya abinci ba. (Sai dai abinda Smart bai sani ba girki yana cikin hubby ɗin Lulu, tana son girki kuma ta iya kalolin girki na zamani sai dai fa sai ta gadamar yi take yin, tamafi sakin jiki tayi idan taje gidan Dada (kakarta matar Alhaji Garko) amma idan kaga tai girki a gidansu ko gidan Uncle Yousuf lallai ƴan arziƙinne a kanta ko taso yima Daddy wani bazata ko Uncle Yousuf ɗin). Abinda tai ɗin ya sashi jin daɗi bai ji ƙyashin tayata suka gyara kitchen ɗin ba duk da ma ba wani ya ɓaci bane dan Lulu akwai iya ƙwaf-ƙwaf ɗin aiki komai aka taɓa ana wankesa ne da zarar an gama da shi, inda ko ruwa ya taɓa za'a goge, tana hakanne kuma saboda yanayin tsaftarta, hakan kuma sai ya sake bama Smart nutsuwa kasancewarsa mutum mai shegen tsantseni da tsantsami. Dining takai komai ta ajiye tai wucewarta bedroom batare da ajiye plate ko kofin da za'ayi amfani ba. Baiyi magana ba saboda kiran Uncle Yousuf da ke shigo masa. Kiran ya amsa ya koma falo ya zauna. Har ya kammala wayar bata fito ba, dan haka ya miƙe yabi bayanta. Samunta yay kwance a kan gado rufda ciki sai dai ta canja kayan jikinta zuwa wasu, a hankali ya sauke ajiyar zuciya tare da yin gyaran murya. Kamar bazata kulashi ba sai kuma ta buɗe idanun kaɗan a kansa. Cikin ido suka kalla juna, ta janye nata da wani yin gaba da lips kamar mai son yin zinɗe, ta ce, “Wlhy in ma da wani abun kazo bazanyi ba na gaji”.
Dariya taso bashi dan yanda tai maganar da iyakar gaskiyarta, amma sai ya dake da ƙyar ya ce, “Ni na isa na sake saka Madam aiki ai tsaurin idon nawa ma sai yayi yawa. Sannu nazo yi miki, da kuma ban haƙiri da bikon kizo kici abinci. Har dama tausa idan kina so ƙyauya”.
Cikin taɓe baki da harararsa akan zancensa na ƙarshe ta ce, “Kai ne handin burum kaje kaita ci”.
“To Aliyu Hydar ka ƙara samun cigaba kenan, da ga illiterate velleger ka koma Maye, yau kuma handin burum, ɗan Ammah baban Ammah mijin Mawadda....”
Filon da take kwance ta fisga kafin ma ya kai ƙarshen sunanta da taji ya kamo ta wulla masa. Da sauri ya cafe yana zaro idanu, ya ce, “Madam ina rabaki da halin jifar nan kar wataran ki ɓazge min hanci kamar yanda Iffah tai ma Uwa fa tom”.
Wasu ta sake fisga tana tashi zaune ta cigaba da jefa masa su, tun yana karewa har ya fita yana dariya dan ya kula dai fushin ake saukewa a haka. Ƙwafa tayi itama da ballama ƙofar harara kamar itace tai mata laifin.....
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 7️⃣1️⃣
........Tana fitowa ɗauke da dankali ya fuske kamar bashi ba ya cigaba da game ɗin yana satar kallonta ta gefen ido. Ganin ta fara firar dankalin ya sashi ajiye wayar tasa a table ɗin ya miƙe, gefenta ya tsaya kaɗan, ya ɗauka wuƙar data ajiye saman chopped board ya fara yanka wanda ta fere, bata kulashi ba, ba kuma tayi magana ba ta cigaba da ferewa tana ajiye masa. Shima sai baiyi magana ba ya cigaba da yankawa, idan ya ɗan tara sai ya zuba a cikin ruwan data ajiye a bowl. A haka har suka kammala, kasancewar ta rigashi gamawa ita ta fara barin wajen ta ɗakko preyn fan ta dawo inda yaken ta zuba ruwan sabulu kaɗan ta wankesa da soso ta ɗaureye duk yana satar kallonta. Komawa tai gaban gas ta kunna ta ɗora sannan ta zuba man data ɗakko. Dai-dai nan ya kammala, sai ya wanke mata dankalin ya sake masa ruwa ya tace sannan ya juyo yana miƙa mata robar. Sai da ta hararesa ta amsa, shi dai ya gimtse dariyarsa da ƙyar ya juya yana ɗauraye wuƙa da sauran abinda sukai amfanin. Lulu kam koda albasanta ya soyu ta zuba dankalin sai ta nufi frizzier, kifi tai ƙoƙarin cira sai dai sanyin da ya ratsa mata hannu ya sata faɗin, “Ouchh!!”. Juyawa yay yana kallonta, ganin yanda take yarfe hannun ya sashi nufarta, hannun ya riƙo ya saka cikin nashi ya rumtse ɗumin nasan ya ratsata, sai kuma ya jawota gaban fanfo ya kunna ruwa ya ɗauraye mata hannun, sannan ya jawo ƙaramin towel ya saka mata hannun ciki. Komawa yay ya ciro kifin har biyu masu ɗan girma ya dawo ya wanke su sannan ya dubeta, ɗauke kanta tai da ga kallon gefen ido da take masa. Shiko da ba lura yay ba ya ce mata “Yankawa zakiyi?”.
Ƙaramar harara ta sakar masa da tura baki gaba sannan tace e.
“Kai dai Aliyu kana shan harara wlhy abin tausayi”. Ya faɗa yana yanka kifin. Hararar tasa ta sake yi da matsawa gaban dankalinta ta da ke cikin mai......
Kusan a tare sukai aikin, sai dai itace ke girkin shi kuma yana taimaka mata da yanka miƙo, duk da dai ba itace ke cewa yayi ɗin ba. Ya shiga matuƙar mamakin ganin yanda take girkin dama yanda tayisan, dan harga ALLAH bai kawo ta iya abinci ba. (Sai dai abinda Smart bai sani ba girki yana cikin hubby ɗin Lulu, tana son girki kuma ta iya kalolin girki na zamani sai dai fa sai ta gadamar yi take yin, tamafi sakin jiki tayi idan taje gidan Dada (kakarta matar Alhaji Garko) amma idan kaga tai girki a gidansu ko gidan Uncle Yousuf lallai ƴan arziƙinne a kanta ko taso yima Daddy wani bazata ko Uncle Yousuf ɗin). Abinda tai ɗin ya sashi jin daɗi bai ji ƙyashin tayata suka gyara kitchen ɗin ba duk da ma ba wani ya ɓaci bane dan Lulu akwai iya ƙwaf-ƙwaf ɗin aiki komai aka taɓa ana wankesa ne da zarar an gama da shi, inda ko ruwa ya taɓa za'a goge, tana hakanne kuma saboda yanayin tsaftarta, hakan kuma sai ya sake bama Smart nutsuwa kasancewarsa mutum mai shegen tsantseni da tsantsami. Dining takai komai ta ajiye tai wucewarta bedroom batare da ajiye plate ko kofin da za'ayi amfani ba. Baiyi magana ba saboda kiran Uncle Yousuf da ke shigo masa. Kiran ya amsa ya koma falo ya zauna. Har ya kammala wayar bata fito ba, dan haka ya miƙe yabi bayanta. Samunta yay kwance a kan gado rufda ciki sai dai ta canja kayan jikinta zuwa wasu, a hankali ya sauke ajiyar zuciya tare da yin gyaran murya. Kamar bazata kulashi ba sai kuma ta buɗe idanun kaɗan a kansa. Cikin ido suka kalla juna, ta janye nata da wani yin gaba da lips kamar mai son yin zinɗe, ta ce, “Wlhy in ma da wani abun kazo bazanyi ba na gaji”.
Dariya taso bashi dan yanda tai maganar da iyakar gaskiyarta, amma sai ya dake da ƙyar ya ce, “Ni na isa na sake saka Madam aiki ai tsaurin idon nawa ma sai yayi yawa. Sannu nazo yi miki, da kuma ban haƙiri da bikon kizo kici abinci. Har dama tausa idan kina so ƙyauya”.
Cikin taɓe baki da harararsa akan zancensa na ƙarshe ta ce, “Kai ne handin burum kaje kaita ci”.
“To Aliyu Hydar ka ƙara samun cigaba kenan, da ga illiterate velleger ka koma Maye, yau kuma handin burum, ɗan Ammah baban Ammah mijin Mawadda....”
Filon da take kwance ta fisga kafin ma ya kai ƙarshen sunanta da taji ya kamo ta wulla masa. Da sauri ya cafe yana zaro idanu, ya ce, “Madam ina rabaki da halin jifar nan kar wataran ki ɓazge min hanci kamar yanda Iffah tai ma Uwa fa tom”.
Wasu ta sake fisga tana tashi zaune ta cigaba da jefa masa su, tun yana karewa har ya fita yana dariya dan ya kula dai fushin ake saukewa a haka. Ƙwafa tayi itama da ballama ƙofar harara kamar itace tai mata laifin.....