Sashe 65
Furar Danko Part1 Compete Hausa Novel · about 8 min read
A ɓangaren su Umma da aminiyarta masu tafiya garin Zuru da ƙyar ta samu Abba ya barta bayan ta lafta masa ƙaryar zuwa garin su duba Innarta, acewarta ƙanwarta tai kiranta da dare ta sanar mata jikin Innarsu ya motsa. Bai kawo komai a ransa ba tunda yasan Innar tasu dama jiyya take kusan shekara huɗu kenan. Ya jajanta mata da bata izninin tafiya dan haka ana sallame sallar asuba taima ƴan gidan sallama ta wuce. Duk da asubancin tafiyar da sukai basu iso garin Zuru ba sai bayan sallar azhar. Burinsu su kammala komai su koma garinsu Umma ɗin a yau su kwana. Sun koyi sa'ar samun Malam Na-zuru a gidan kamar ma su yay zaman jira kasancewar tun kan su taso sunyi kiransa sun sanar masa. Bayan gaisuwa da tambayar juna bayan rabuwa ya dubi Hajiya Naqiba dan ita kam bata rabo da zuwa inda yake har ma ta saba dan ta riga ta gama kama mijinta a hannu a sake take kamar akuyar fulani. Umma kam Abba bai kasance a ƙarƙashin ikon nata ba ɗari bisa ɗari shiyyasa zuwan ke mata wahala kai tsaye sai idan gagarumin abu ne ya faru.
“Hajjaju yau Aminiyar ki ta tuna damu kenan ko? Idan ban manta ba rabonta da nan kusan shekara uku kenan fa”. Cikin ƴar dariya Hajiya Naqiba ta ce, “Gaskiya za'ayi kam malam. Kasan ita akuyar ɗaure ce ganinta sai anyi sake ko tsautsayi ya gifta ta kufce”. Ta ƙare maganar tana kallon Umma. Dariya sukayi gaba ɗaya. Kafin Malam Na-zuru ya tsagaita da maida hankalinsa ga Umma yace, “Hajiya Yaha mike tafe da ke?”.
“Abubuwane da yawa kashi-kashi malam. Sai dai mafi girma a cikinsu aikin yaron nan ne mai shegen taurin kai ya ke neman buɗe min wlhy....”
“Tofa badai yaro mai tamaula ba ko?”.
“Wlhy shi kuwa malam. Dan jiya-jiya aka ɗaura masa aure da ƴar wani hamshaƙin attajiri”.
“Aure kuma? Ya akai haka ta faru Hajiya? Kina ina akai wannan babbar ta'asa bayan kin san da ƙyar muka samu yaron nan ya shiga hannun mu? Wannan kuma yana a cikin babban abinda muka ƙullesa da shi fa”.
“Wlhy malam nima ban san yaya akai hakan ta faru ba. Sai dai na lura tsabar munafunci ne na ubansu ya sa aka rufe mana komai sai ɗaurin aure kawai mukaji bayan an riga an ɗauro. Malam ka taimakeni dan ALLAH. Kai kanka ka sanar min yaron nan yanada taurari masu ƙarfin gaske da zasu iya disashe kaf ƴaƴan gidan nan ya zam babu hasken wanda ake gani sai shi, bayan kai malamai kusan huɗu sun sanar min hakan wasu ma sun kasa aiki a kansa sai kai ne da kayi akaci nasara. Gashi kuwa na fara gani dan aure fa akai masa, kuma da ƴar Alhaji Isma'il Jiƙamshi, wannan abu ya hanani samun barci sam a daren jiya”.
“Tirƙashi! Dolene ki kasa barci. Dan aurensa na ɗaya da ga cikin abinda muka ƙulle masa har sai ya tsufa a haka ta yanda babu mai ɗaukar ƴa ya bashi. Ba ƙaramin duka a ciki mijin nan yay mana ba gaskiya. Dan yaron nan yanada ƙarfin nacin ibada shiyyasa muka jima muna aiki yana tafiya a iska, na ƙarshen nan ma da ƙyar kina gani muka samu ya haushi da taimakon anfani da gashin mahaifansa da nashi.....”
“Na sani Malam, dan ALLAH ka taimakeni wannan aure ya watse kafin ma cikar sati ɗaya na tarewar wannan yarinya. Sannan a matse minsu waje guda su rasa gabas su rasa yamma akan wajen da zai zauna da abinda zasuyi hidimar biki. A sakama duk danginta tsanarsa a zuciya hatta da jaririn yaro. A birkitamin lissafin yarinyar ta ce bata son sa”.
“Aikin nan yana da wahala Yahanasu. Amma dai zaɓi ɗaya anan mu gwada mu gani”. Ya ƙare maganar da ajiye mata tazbaharsa gabanta. Da ƙyar ta iya tsaida nutsuwarta wajen ɗaukar ɗiyan tazbahar ɗaya ta miƙa masa. Amsa yay ya duba ya sake ajiye mata yace ta ɗauka. Sai da sukai haka sau uku sannan ya kalleta cikin jinjina kansa. “Gaskiya akwai babban aiki a gareki. Dan gaba ɗaya fa an riga an lalata aikin sai kaɗan ne bai bar jikinsa ba. Wanda kuma ya ƙulla wannan auren mutum ne mai nasibi matuƙa shima, dan komai yayisa ne da hikima kasancewar ya fahimci akwai ɓoyayyen al'amari akan rayuwar yaron......”
“Kenan babu yanda za'ai malam? Sannan waye shi wannan matsiyacin da ke tare da shi haka ba sani ba tun da wuri?”. Umma ta faɗa kamar zatayi kuka. Malam Na-zuru yay gyaran murya yana gyara zama. “Baza'a rasa yanda za'aiba kam. Sai dai dole za'a canja taku kuma. Shi wannan mutumin da kike tambaya yanada alaƙa da yarinyar matuƙa, sannan yana ƙaunar yaron da zuciya ɗaya, mutum ne kuma mai wayo da hikima gaskiya. Samun nasara a kansa kuma shima sai munyi yaƙi na gaske. Amma ita matar da aka ɗaura masa auren da ita mu maida akalar aikin namu ta hanyarta kawai inaga hakan zai taimaka mana”.
“To amma malam matar da ba'a bukatar ma ta tare miye amfanin kafa harsashin aiki kanta?”. Hajiya Naqiba ce yanzu tai masa tambayar dan Umma dai damuwar jin labarin waye Uncle Yousuf ya hanata magana ma. Amsa ya bata da faɗin, “Gaskiya in har kuna son cimma burinku akan yaron nan dole sai anbi ta hanyar ita wannan yarinya. Hakan na nufin kuma dole sai ta tare da shi sannan komai mu bisa a sannu.....”
Da sauri Umma ta ce, “Malam kana nufin ma har sai ya kusanceta a shimfiɗa kenan?”.
“A'a ba wannan nake nufi ba. Ko tarewa a gidansa tai matsayin mata to ya wadatar damu. Dan muna buƙatar kayan da aka kawota gidansa da shi a ranar, da wanda shi kuma zai shiga gareta da su. Sauran aikin ya rage namu mukuma”.
Jimmm Umma tai alamar tunani kafin ta sauke nannauyar ajiyar zuciya da faɗin, “Shike nan malam zanyi wannan ƙoƙarin. Sai kuma akan kishiyoyin nawa ina son a sabunta min aiki musamman uwar yaron nan. Dan na tsaneta fiye da kowa a gidan nan. Bana son koda ganinta matsiyaciyar. Yanda ta saka katanga tsakanina da masoyina har sai da ta fara zama matsayin matarsa na tsawon shekaru kafin ya kalleni bisa tirsasawar iyaye, wlhy itama sai na gunzuga mata baƙin cikin da har ta mutu bazata fita a cikinsa ba.”
“Burinki zai cika kuwa. Mudai je zuwa mataki-mataki zaki sha mamaki”.
Sosai farin ciki ya mamaye Umma, ta cigaba da zayyano ma Malam Na-zuru duk yanda take buƙata akan Ammah da zuri'arta. Suma sauran matan kowacce da kalar nata shirin da take so ai mata. Sai matar ɗanta Salim da itama ke neman zame mata ƙarfen ƙafa akan janye mata ra'ayin Salim ɗin. Basu dai baro garin Zuru ba sai bayan la'asar, a hakan ma ɗan basu tsaya yin koma ba. Sun jigatu kam gwargwadon iko sai kusan goma sha ɗaya na dare suka iso garin su Umma da nufin duba mahaifiyar Tata su kwana.......✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣1️⃣
.........Tunda suka baro gidan babu abinda Lulu keyi sai haɗiyar zuciya. Ko sau ɗaya bata tankama hirar da Uncle Yousuf ke mata ba, hijjab nema da ya tambayeta ina ta samo cikin takaicin da har yanzu yaƙi sakar mata maƙoshi ta amsa masa da, “Uncle You mutumin nan fa ni bazan tare ba na fasa ko zaman wata ɗayan. Shiko dai yanata danne dariyarsa har suka iso gida. Sai da yay parking ya dubeta cikin nutsuwa ya ce, “Saboda mi basai kin tare ba?”.
“Ni dai kawai nama fasa. Dama na gaya maka mutumin nan baida mutunci, to kaga tun kafin ma na fara shuka masa nawa kalar rashin mutuncin kawai mu tsaya iya hakan”.
“To banƙi ta taki ba, amma yaya kike tunanin duniya da Baba zasu kalla al'amarin? Dan Baba fa zai iya ɗaukar zafin da bamu taɓa zato ko tsammani ba. Ni dai da zakiji shawarata anan ki cigaba da kwantar da hankalinki ayi komai a yanda aka tsarashi. Shima kuma mu bisa a sannu a rabu lafiya batare da kowa yaji ko ya gani ba. Dama jira nake ya sake samun lafiya yazo muyi magana ma ta fahimta ok”.
Sosai yanda Uncle ɗin nata ke mata magana cikin kulawa da sanyi ya sata jin bazata iya bijire masa ba. Dan haka ta jinjina kanta tana sauke tagwayen ajiyar zuciya ta ce, “Shike nan Papa. Amma dan ALLAH ka masa magana ya kama kansa”.
“Zan masa kar ki damu”.
Ya bata amsa cike da kulawa. Wata ajiyar zuciyar ta sake saki sannan suka fita. Da ƙyar Uncle Yousuf ya iya danne dariyarsa shi dai yana binta da kallo, tausayi take bashi, ba kuma ya ganin kowa da laifi sama da Daddy, ya raunana rayuwar yarinyar matuƙa da sunan soyayya, ya kasa fahimtar tarbiyyar uwa ga ƴaƴa daban take da komai a wannan rayuwar musamman ma ɗiya mace, amma sam Mawaddat bata samu ba, shiyyasa abubuwa masu muhimmanci ma duk bata sani ba kuma bata ganesu da yaren fahimta.....
Koda ta shiga gidan ma aunty Saliha dake yanke ma Ra'is farce a falo sakin baki tai kawai tana kallonta. Ai ko sai ta sake tunzura fuuu aka shige ɗaki. Dai-dai nan Uncle Yousuf ya shigo shima. Da hannu ta nuna masa bayan Lulu. “Miya kunna ƴar taka? Ga shi naga an dawo da hijjab?”.
Ƙaramar dariya ya saki yana kaiwa zaune. Ƙasa-ƙasa ya ce, “Aikin surukinki ne”.
“Woow dan ALLAH fa?”.
“Sosai”.
Ya faɗa cikin gyaɗa kai da lumshe ido abin dariya. Sai kuma ya nuna mata Ra'is da ido. Murmushinta ne ya ƙara faɗaɗa. Sai dai bata sake cewa komai ba....
★★......
“Hajjaju yau Aminiyar ki ta tuna damu kenan ko? Idan ban manta ba rabonta da nan kusan shekara uku kenan fa”. Cikin ƴar dariya Hajiya Naqiba ta ce, “Gaskiya za'ayi kam malam. Kasan ita akuyar ɗaure ce ganinta sai anyi sake ko tsautsayi ya gifta ta kufce”. Ta ƙare maganar tana kallon Umma. Dariya sukayi gaba ɗaya. Kafin Malam Na-zuru ya tsagaita da maida hankalinsa ga Umma yace, “Hajiya Yaha mike tafe da ke?”.
“Abubuwane da yawa kashi-kashi malam. Sai dai mafi girma a cikinsu aikin yaron nan ne mai shegen taurin kai ya ke neman buɗe min wlhy....”
“Tofa badai yaro mai tamaula ba ko?”.
“Wlhy shi kuwa malam. Dan jiya-jiya aka ɗaura masa aure da ƴar wani hamshaƙin attajiri”.
“Aure kuma? Ya akai haka ta faru Hajiya? Kina ina akai wannan babbar ta'asa bayan kin san da ƙyar muka samu yaron nan ya shiga hannun mu? Wannan kuma yana a cikin babban abinda muka ƙullesa da shi fa”.
“Wlhy malam nima ban san yaya akai hakan ta faru ba. Sai dai na lura tsabar munafunci ne na ubansu ya sa aka rufe mana komai sai ɗaurin aure kawai mukaji bayan an riga an ɗauro. Malam ka taimakeni dan ALLAH. Kai kanka ka sanar min yaron nan yanada taurari masu ƙarfin gaske da zasu iya disashe kaf ƴaƴan gidan nan ya zam babu hasken wanda ake gani sai shi, bayan kai malamai kusan huɗu sun sanar min hakan wasu ma sun kasa aiki a kansa sai kai ne da kayi akaci nasara. Gashi kuwa na fara gani dan aure fa akai masa, kuma da ƴar Alhaji Isma'il Jiƙamshi, wannan abu ya hanani samun barci sam a daren jiya”.
“Tirƙashi! Dolene ki kasa barci. Dan aurensa na ɗaya da ga cikin abinda muka ƙulle masa har sai ya tsufa a haka ta yanda babu mai ɗaukar ƴa ya bashi. Ba ƙaramin duka a ciki mijin nan yay mana ba gaskiya. Dan yaron nan yanada ƙarfin nacin ibada shiyyasa muka jima muna aiki yana tafiya a iska, na ƙarshen nan ma da ƙyar kina gani muka samu ya haushi da taimakon anfani da gashin mahaifansa da nashi.....”
“Na sani Malam, dan ALLAH ka taimakeni wannan aure ya watse kafin ma cikar sati ɗaya na tarewar wannan yarinya. Sannan a matse minsu waje guda su rasa gabas su rasa yamma akan wajen da zai zauna da abinda zasuyi hidimar biki. A sakama duk danginta tsanarsa a zuciya hatta da jaririn yaro. A birkitamin lissafin yarinyar ta ce bata son sa”.
“Aikin nan yana da wahala Yahanasu. Amma dai zaɓi ɗaya anan mu gwada mu gani”. Ya ƙare maganar da ajiye mata tazbaharsa gabanta. Da ƙyar ta iya tsaida nutsuwarta wajen ɗaukar ɗiyan tazbahar ɗaya ta miƙa masa. Amsa yay ya duba ya sake ajiye mata yace ta ɗauka. Sai da sukai haka sau uku sannan ya kalleta cikin jinjina kansa. “Gaskiya akwai babban aiki a gareki. Dan gaba ɗaya fa an riga an lalata aikin sai kaɗan ne bai bar jikinsa ba. Wanda kuma ya ƙulla wannan auren mutum ne mai nasibi matuƙa shima, dan komai yayisa ne da hikima kasancewar ya fahimci akwai ɓoyayyen al'amari akan rayuwar yaron......”
“Kenan babu yanda za'ai malam? Sannan waye shi wannan matsiyacin da ke tare da shi haka ba sani ba tun da wuri?”. Umma ta faɗa kamar zatayi kuka. Malam Na-zuru yay gyaran murya yana gyara zama. “Baza'a rasa yanda za'aiba kam. Sai dai dole za'a canja taku kuma. Shi wannan mutumin da kike tambaya yanada alaƙa da yarinyar matuƙa, sannan yana ƙaunar yaron da zuciya ɗaya, mutum ne kuma mai wayo da hikima gaskiya. Samun nasara a kansa kuma shima sai munyi yaƙi na gaske. Amma ita matar da aka ɗaura masa auren da ita mu maida akalar aikin namu ta hanyarta kawai inaga hakan zai taimaka mana”.
“To amma malam matar da ba'a bukatar ma ta tare miye amfanin kafa harsashin aiki kanta?”. Hajiya Naqiba ce yanzu tai masa tambayar dan Umma dai damuwar jin labarin waye Uncle Yousuf ya hanata magana ma. Amsa ya bata da faɗin, “Gaskiya in har kuna son cimma burinku akan yaron nan dole sai anbi ta hanyar ita wannan yarinya. Hakan na nufin kuma dole sai ta tare da shi sannan komai mu bisa a sannu.....”
Da sauri Umma ta ce, “Malam kana nufin ma har sai ya kusanceta a shimfiɗa kenan?”.
“A'a ba wannan nake nufi ba. Ko tarewa a gidansa tai matsayin mata to ya wadatar damu. Dan muna buƙatar kayan da aka kawota gidansa da shi a ranar, da wanda shi kuma zai shiga gareta da su. Sauran aikin ya rage namu mukuma”.
Jimmm Umma tai alamar tunani kafin ta sauke nannauyar ajiyar zuciya da faɗin, “Shike nan malam zanyi wannan ƙoƙarin. Sai kuma akan kishiyoyin nawa ina son a sabunta min aiki musamman uwar yaron nan. Dan na tsaneta fiye da kowa a gidan nan. Bana son koda ganinta matsiyaciyar. Yanda ta saka katanga tsakanina da masoyina har sai da ta fara zama matsayin matarsa na tsawon shekaru kafin ya kalleni bisa tirsasawar iyaye, wlhy itama sai na gunzuga mata baƙin cikin da har ta mutu bazata fita a cikinsa ba.”
“Burinki zai cika kuwa. Mudai je zuwa mataki-mataki zaki sha mamaki”.
Sosai farin ciki ya mamaye Umma, ta cigaba da zayyano ma Malam Na-zuru duk yanda take buƙata akan Ammah da zuri'arta. Suma sauran matan kowacce da kalar nata shirin da take so ai mata. Sai matar ɗanta Salim da itama ke neman zame mata ƙarfen ƙafa akan janye mata ra'ayin Salim ɗin. Basu dai baro garin Zuru ba sai bayan la'asar, a hakan ma ɗan basu tsaya yin koma ba. Sun jigatu kam gwargwadon iko sai kusan goma sha ɗaya na dare suka iso garin su Umma da nufin duba mahaifiyar Tata su kwana.......✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣1️⃣
.........Tunda suka baro gidan babu abinda Lulu keyi sai haɗiyar zuciya. Ko sau ɗaya bata tankama hirar da Uncle Yousuf ke mata ba, hijjab nema da ya tambayeta ina ta samo cikin takaicin da har yanzu yaƙi sakar mata maƙoshi ta amsa masa da, “Uncle You mutumin nan fa ni bazan tare ba na fasa ko zaman wata ɗayan. Shiko dai yanata danne dariyarsa har suka iso gida. Sai da yay parking ya dubeta cikin nutsuwa ya ce, “Saboda mi basai kin tare ba?”.
“Ni dai kawai nama fasa. Dama na gaya maka mutumin nan baida mutunci, to kaga tun kafin ma na fara shuka masa nawa kalar rashin mutuncin kawai mu tsaya iya hakan”.
“To banƙi ta taki ba, amma yaya kike tunanin duniya da Baba zasu kalla al'amarin? Dan Baba fa zai iya ɗaukar zafin da bamu taɓa zato ko tsammani ba. Ni dai da zakiji shawarata anan ki cigaba da kwantar da hankalinki ayi komai a yanda aka tsarashi. Shima kuma mu bisa a sannu a rabu lafiya batare da kowa yaji ko ya gani ba. Dama jira nake ya sake samun lafiya yazo muyi magana ma ta fahimta ok”.
Sosai yanda Uncle ɗin nata ke mata magana cikin kulawa da sanyi ya sata jin bazata iya bijire masa ba. Dan haka ta jinjina kanta tana sauke tagwayen ajiyar zuciya ta ce, “Shike nan Papa. Amma dan ALLAH ka masa magana ya kama kansa”.
“Zan masa kar ki damu”.
Ya bata amsa cike da kulawa. Wata ajiyar zuciyar ta sake saki sannan suka fita. Da ƙyar Uncle Yousuf ya iya danne dariyarsa shi dai yana binta da kallo, tausayi take bashi, ba kuma ya ganin kowa da laifi sama da Daddy, ya raunana rayuwar yarinyar matuƙa da sunan soyayya, ya kasa fahimtar tarbiyyar uwa ga ƴaƴa daban take da komai a wannan rayuwar musamman ma ɗiya mace, amma sam Mawaddat bata samu ba, shiyyasa abubuwa masu muhimmanci ma duk bata sani ba kuma bata ganesu da yaren fahimta.....
Koda ta shiga gidan ma aunty Saliha dake yanke ma Ra'is farce a falo sakin baki tai kawai tana kallonta. Ai ko sai ta sake tunzura fuuu aka shige ɗaki. Dai-dai nan Uncle Yousuf ya shigo shima. Da hannu ta nuna masa bayan Lulu. “Miya kunna ƴar taka? Ga shi naga an dawo da hijjab?”.
Ƙaramar dariya ya saki yana kaiwa zaune. Ƙasa-ƙasa ya ce, “Aikin surukinki ne”.
“Woow dan ALLAH fa?”.
“Sosai”.
Ya faɗa cikin gyaɗa kai da lumshe ido abin dariya. Sai kuma ya nuna mata Ra'is da ido. Murmushinta ne ya ƙara faɗaɗa. Sai dai bata sake cewa komai ba....
★★......