← Book details Furar Danko Part1 Compete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 111

Sashe 23

Furar Danko Part1 Compete Hausa Novel · about 6 min read

_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥

*_ALLAH ya gafartama iyayenku😭🙏_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗

           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻

𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣8️⃣

.........A ɓangaren Lulu kam sosai ta haukacema ƙwaro ta waya da masifa shiko ya dinga rantsuwar ya saka mata. Har abokinsa da yay komai a gabansa ya bama wayar ya zame masa sheda amma taƙi yarda. Sai ma katse kiran tai da tabbatar masa sai ya san ita ya cuta wlhy... Gado ta faɗa zuciyarta na mata wani irin tafasa, babu abinda ke mata kai kawo a rai irin maganganun drivern ta, haka kawai zuciyarta ke ingizata akan son sanin ma'anarsu. Wayarta data yasar gefe ta jawo. Nadeeya ta kira, ana ɗagawa daga can Nadiya ta fara da faɗin, “Bastie dama fa yanzu zan kiraki, dan gama wayata da Gajere kenan yace za'a samu kaya a wajen ogansa kona mil. ake s.....”
       “Kinga ni ba wannan ba...”
    Ta faɗa cikin katse Nadeeyar.
“Oh to ina saurarenki, na jiki kamarma cikin ɓacin rai, miya faru kuma? Badai driver ɗin ba kuma?”.
      “Komai ma ya faru, har ma abinda banyi zaton faruwarsa ba ya faru. Wani Hausa nake son ki fassara min”.
   “Tofa! Wane Hausa kuma?”.
Batasan ta haddace abinda ya faɗa matan ba sai da ta zayyanosu tsaf a yanda ya faɗesu babu ko gargada. _“Duk macen data cika mace mai suturtawace akan kanta har akan muharramanta, hakan kansa ko bata kira daraja gareta ba, darajar kanzo ta risina mata a gaban wanda ya fita ma balle wanda ke a ƙarƙashin ikonta. Wannan gata da musulunci yayma mace har a lafazinta ana so ta zama mai ƙyautatawa akan harshe”._
     “Woow Madam irin wannan kalamai haka kamar wata mai tsara baitikan waƙe, dan ALLAH waya shiryasu haka....”
    “Mtsoww malam dilla fassararsu nake buƙata nace”.
    “Oh sorry, tab wlhy fa kalaman sunyi tsauri, ni kaina ban san yanda zan fassarasu ki gane ba dan hausan ba gama isata yay ba. Amma ina zuwa bari na tambaya”.
         Tana ƙoƙarin ajiye wayar cikin jan tsaki Suhaib na mata knocking. “Uwar miye?”. Ta faɗa cikin masifa. Cikin tunzura baki Suhaib da ke da ga ƙofa dan bai shiga ba ma ya ce, “Uncle Yousuf ne yazo, ya ce kizo” da ga haka yay wucewarsa.
      Tana son Uncle Yousuf matuƙa, tana kuma girmamashi saboda wasu dalilai nata na kanta. Dan haka tace ma Nadiya tana zuwa ta yanke wayar. Da mamaki mai nuna ɓacin rai take duban Smart da ke zaune a ƙayataccen falon nasu kusa da Uncle Yousuf. “Mi wannan abun yazo yimana nan Uncle You?”. Ta faɗa tana nuna Smart da ke zaune babu alamar ɗari-ɗarin nan irin na ma'aikaci da iyayen gidansa a tare da shi. “Ni na kirawoshi” Uncle Yousuf ya bata amsa cikin ɗaure fuska. “Uncle nifa bana buƙatar sake ganinsa” ta faɗa itama a harzuƙe.
      “Da yay miki mi?”.
   Baki ta tura gaba cikin kumbura fuska ta ce, “Wlhy na tsanesa, har ni wannan mutumin zai zaga. Korar ma da nai masa yanzu ba'ita kenan ba Uncle, ya jira hukuncin da zai biyo bayanta. Har ni zaima banza ina masa magana, sannan ya biyoni da baƙaƙen maganganu a gaban su maigadi, har shi waye? Mi yake jin kansa? Ɗan u......”
     Hannu Uncle Yousuf ya ɗaga mata, “Ya isa haka. Mawaddat wai yaushe zakiyi hankali ne dan ALLAH. Yanzu abinda kike yi ko su Suhaib ƙannenki zasu aikata ne? Ke kullum cikin korar mutane. Yanzu dai ina son ki nutsu ki kwantar min da hankalinki, dan shiyyasa ma na dawo da shi gidan a yanzu dan na haɗu da shi a hanya ne. Ban kawo Aliyu gidan nan dan ki koresa ba, zan ƙara jaddada miki a yanzu shi ɗin zai dinga kaiki duk inda kike so dan saboda ke kaɗai ma na ɗaukesa aiki. Zai zo ƙarfe bakwai da rabi saboda takwas kike fita aiki, zai dawo da ke ƙarfe biyar da rabi kamar yanda kike dawowa shike nan ya tashi sai kuma washe gari period na gama magana.”
       “Amma Uncle....”
Hannu ya ɗaga mata alamar baya buƙatar ta sake cewa komai, rai ɓace tabar wajen kamar zata fashe dan haushi. Da ga haka ya juya ga Smart da ke zaunensa a yanda ta shigo ta samesa batare da yabi takanta ba. “Wannan shine lokacin zuwanka aiki da tashin ka. Amma weekend zaka iya zuwa da ga goma zuwa huɗu sai ka tashi. Zan baka duka tsare-tsaren fitarta a rubuce, sai kuma idan zuwa wani waje ya kamata kasan aikinsu yana sakasu ɗan yinan-yinan koba shiri. Dan ALLAH ka ƙara hakuri, al'amarin Mawaddat sai addu'a, ga yanayin da take ciki na ƙara kangarar da ita. Kai tsakaninku ma akwai cigaba, dan naga alamar tana shakkar ka sosai”.
      Karan farko ya saki ɗan murmushi da shafa kansa. “Alhaji wane tsoro kullum ana zageni da kirana illiterate ko villager. Kawai dai zanyi haƙuri domin mutuncinku da ceto rayuwarta, dan koba komai nima inada ƙanne mata, ina son kuma ALLAH ya karemin su a duk inda suka shiga.”
     “Gaskiya ne wannan Aliyu. Ina godiya matuƙa a gareka da sake baka haƙurin di. Yanda ALLAH ya haɗa wannan zuminci a tsakaninmu ALLAH yasa muci moriyarsa har a gidan aljanna. Amma ina son naji wannan kalamai da aka faɗama yarinyata haka har suka harmutsa min ita, duk da nasan abu kaɗan ma fusata Mawaddat yake”.
    Murmushi Smart ya sake yi a karo na biyu da faɗin, “A Alhaji ai ba'ayi haka ba. Tunda ya wuce a barsa kawai sai na gaba idan ALLAH yasa za'ayi a gabanka, duk da ina tsoron kuma karta kwaɗa min mari dan yau ma dai da ƙyar na sha shiyyasa ma na gudu”.
       Dariya sosai Uncle Yousuf yake kwasa da faɗin, “A lallai ka tsira da ƙyar, dan a ma'aikatan gidan nan ɗai-ɗai ne basu sha marin Lulu ƙamshi ba kam”.
    “To kaji ko Alhaji. Bara nayi nan kafin ta sake fusatowa ma, nasan yanzu bai zama lallai na sha ba”.
Dariya Uncle Yousuf ɗin ya sake kwashewa da shi, shi kuma ya fice yana ɗan murmushinsa mai sanyi, har ga ALLAH yana ganin mutunci da kimar Uncle Yousuf, yaji kuma zai iya haƙuri da yarinyar kodan shi ɗin. Mutum ne da yasan daraja da kimar mutane, duk yanda kake baya wulaƙantaka ko nuna maka ɗagawar shi ɗin wani ne. Ya iske har lokacin su maigadi na gulmar Lulu, ganinsa baisa kuma sun daina ba sai ma kwarzantashi da suka shigayi akan abinda yaymata. Komai baice musu ba sai kansa da ya ɗan girgiza kawai ya ciro wayarsa ya fara sana'ar tasa, ba kuma wani abu yake a ciki ba face game ɗin ball.
Chapter 23 · 0% Book details