← Book details Furar Danko Part1 Compete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 60 OF 111

Sashe 60

Furar Danko Part1 Compete Hausa Novel · about 5 min read

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥

*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗

           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻

𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣7️⃣

.......*_WASHE GARI_* da asuba da ƙyar Lulu ta iya tashi sallar da Uncle Yousuf ya sa aunty Saliha ta tadata yi. Dan kuwa dai daren jiya suna gama hira da Aunty Saliha ta shige ɗaki sakamakon dawowar Uncle Yousuf gidan a gajiye ta samu sirof ɗin ta da wani ya kawo mata a gidan bayan sallar isha'i ta fita a sulale ta amso bada sanin aunty Saliha ba har kwalba uku tasha. Dan yanda kanta yau ya ɗauki zafin nan ta tabbatar sai tazo kwanciya komai zaita dawo mata a rai ta kwana cikin damuwa. Sam bata buƙatar hakan kuma. Ga shi dama abin yazo mata a dai-dai wato weekend. Dan dama fa duk weekend kusan sune ranakun da tafi ƙwalewa son ranta ta sha barcinta. Kafin a gane tana shaye-shaye sai aita ɗauka gajiyar aiki ce ke sata mahaukacin barcin da take sha. Balle ma Daddy kan hana a tadota  a cewarsa a barta ta huta. Hakan na bata dama ƙwarai da gaske ita kuma ta sha abinda take son batare da sun gane komai ba.
       Sabon barci ta sake dasawa har kusan sha ɗaya sai da Uncle Yousuf nan ma yasa Aunty Saliha tadata. Tun a yanda ta fito ya fahimci wani abu ta sha a jiyan, bai ce komai ba kan haka duk da zuciyarsa tayi babu daɗi sai cemata da yay ta koma ta shirya yana jiranta zata rakashi wani waje. Kai kawai ta gyaɗa masa da komawa ɗakinta dan tana da ɗaki dama a gidan. Ta jima a toilet ɗin kafin ta fito tanata ƙamshin shower gal mai ƙamshin tsiya, dan anan bata da turarrukan wanka duk ta ƙarar da su ta kuma manta ta kawo ta ajiye dan bata iya cikakken sati biyu batazo nan ta kwana ba ko yin weekend. Tana tsaka da shiryawa Deen ya shigo. “Akku mai bakin magana kenan”. Ta faɗa tana kallonsa. Ai ko yay zaman dirshan ya fara tsiyaya mata surutu itako tana biye masa dan kaf ƙannen nata tafi ƙaunar yaron fiye da kowa. Shima kuma yana son aunty Lu ɗinsa. Sai da ta gama shirinta tsaf cikin doguwar riga ta atamfa da tai masifar lafe mata a jiki kamar wadda akaima fenti. Dan Lulu koda ta saka kayan hausawa irinsu lass atamfa material zaka samesu dai babu wani ɗinkin mutunci a tare da su. Shiyyasa ma kayan basa wuce fitet gwan ne. Dan ko skert da riga ba sosai ta cika yi ba, inma tayin zaka samu suma dai sai sun mata ɗamm kamar zatai nishi su yage. Kasancewar kuma tana da ƙyaƙykyawar sura sai sukan mata ƙyau kamar an haliccesu a jikin nata ne. Dan telan nata kam ƙwarone wajen iya ɗinkin shegantaka. Ba kuma kowa ya haɗata da shi ba sai Nadiya. Yau ma ko takan ɗan kwali ba'abi ba dan dama Amrah ce a mafi yawan lokaci kan mata ɗauri idan tai irin wannan dress ɗin. Sirrin mayafi milk color da ya shiga da zanen atamfar ta yana kawai bisa kai aka ɗora ƙaton google tare da dogayen takalmanta. Dan ƙyau kam tayi ƙyau ga wani mahaukacin ƙamshi mai ɗaukar hankali na tashi. Uncle Yousuf bai fito ba harta kammala breakfast da ba wani na kirki taci ba. Dan shaye-shaye ya gama cinye Lulu ko abincin kirki bata iya ci a rayuwarta. Barta da son cin chocolate kamar shazumamu, dan ko a handbags nata baka rabata da su bayan ƙwayoyinta na shaye-shaye. A tare aunty Saliha da Uncle Yousuf suka sakko da ga sama. Dan haka su duka suka zuba mata ido. Aunty Saliha ce ta fara faɗin, “Babyn Uncle badai da kayan nan zaki fita ba musamman ma ɗan mayafin nan?”.
        Sosai mamakin furucin aunty Saliha ya sata waro idanunta manya da suka juye. Sai kuma ta kalla kanta. Dan tasan dai ba yau ta saba fita a kahaba ai. “Mamy miye laifin kayan nan kuma?”. Ta faɗa fuska a turɓune. Murmushin aunty Saliha tayi da faɗin, “Haba dai Mawaddat ai yau ba jiya bace. Ko kin manta yanzu ke matar aure ce”.
       Wani mugun yamutse fuska tayi dan ita tama manta da wani batun auren. Musamman da ya kasance abinda tasha a daren jiyan ya mantar da ita duk wata damuwarta. Kamar Zatai magana sai kuma tai shiru jin Uncle Yousuf yay gyaran murya da faɗin, “Kinga barta kawai muje ai a mota ne, kuma babu inda zata fita sai a can”.
     Sosai aunty Saliha ta zubama mijin nata ido da mamakin abinda ya faɗa. Dan abu ne da batai zaton ji daga garesan ba sam. Kasa sake magana tai har suka fice Lulu na mata bye ita da Deen da ya maƙale zai bita. Ta ja ajiyar zuciya da faɗin, “Ai masa sannu sai kun dawo”. Da kai kawai Uncle Yousuf ya amsa mata yana ficewa. Yasan abinda yay ɗinne ya ɗaure kanta. Sai dai shima yanada hikimarsa tayin hakan bawai bai san abinda yake yi bane.
Chapter 60 · 0% Book details