Sashe 6
Fadeelah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washegari da wuri Fadila ta yi shirin tafiya aiki , bayan ta gama shiryawa ne ta shiga d'akin mahaifinta, bayan sun gaisa ne ta ce"Baba, na shirya zan tafi" Za ki tafi ina ? " Cewar mahaifin Fadila .
Fadila cikin sanyi ta ce "Zan koma wajan aiki , jiya mama ta ke sanar da ni ka amince in koma"
Mahaifin Fadila shiru ya yi yana kallanta kamar ba zai bata amsa ba dan har ta cire rai ma sannan ya Kira sunanta ya ce"Fadila "
Fadila cikin sanyi ta amsa da "Na'am ,Baba"
Ya ci gaba da cewa"Fadila , dan Allah ki ci gaba da tafiya kamar yadda na sanki , kwanakin baya surutun mutane da kuma tsoron bakin mutane akanki ya sa na dakatar da ke aiki ba wai dan na yarda da abin da su ke cewa ba" Shiru mahaifin Fadila ya yi sannan ya ci gaba da cewa"Fadila , ki sani duk abin da za ki yi Allah na kallanki , tashi ki tafi Allah ya tsare "
Fadila cikin sanyi ta tashi tana mai amsawa da "Ameen ,Baba"
Misalin k'arfe takwas (8:00AM) Fadila ta shiga Rahama TV tana zuwa office din MD ta shiga.
Kamar a mafarki haka ya ga Fadila.Seat d'in da ke facing d'in shi ya nuna mata alamun ta zauna.
Bayan Fadila ta zauna ne ya ce"Fadila , me na yi miki kike son fasa zuciyata? Tun da kika bar zuwa aiki ban tab'a kiranki kika d'aga ba? "
Fadila ji ta yi kunya ta gamata, saboda kodan alfarmar da ya ke yi mata be cancanci ta yi mai haka ba , saidai ba daga ita bane daga zuciyarta ne ,zuciyarta ta ka sa aminta da shi bare kuma har ta yi waya da shi.
Fadila cikin alamun ban hak'uri ta had'a hannuwanta ta ce"Afuwa rankashi dad'e , kana kirana duk bana kusa da Wayar ne , kuma babu kati a wayar bare in biyoka "
Shiru ya yi sannan ya ce" Shi kenan Fadila za ki iya zuwa ki ci gaba da aikinki , saboda ganinki na sa zuciyata cikin damuwa "
Fadila ta shi ta yi ta ce"Shi kenan bari in tafi ba zan so in zama silar damuwarka ba,in da ganina damuwa ya ke saka"
Da sauri ya tashi ya sha gabanta ya ce"Tsaya mana, ba haka nake nufi ba, ke d'in ce kin kasance wani abu mai girma gaske a zuciyata ,da zaki yarda da sai in ce miki ban tab'a so wani abu kamar ki ba, dan Allah ki ban dama mana Fadila?"
Fadila tafe kai ta yi, dan dama tunaninta kenan na dawowa aiki daga ta dawo MD zai fara ta kura mata da maganganun shi da baya gajiya.
Fadila cikin k'osawa tabar Office d'in shi ta ce"Shi kenan, zan yi tunani"
Kai MD ya girgiza ya ce " A'a , Kullum haka kike ce min , ki ban amsa ta kawai ko zuciyata zata samu sukuni dan Allah "
Fadila tana tsoran ta furta mai kalmar k'i ta zo ta samu matsala a wajan aiki ga shi a halin yanzu tana buk'ar aikin sosai, hakan ya sa cikin sanyi ta ce"Shi kenan, zan ba Jamilu sak'o ya baka "
Tana fad'in haka ta fita office d'in da sauri kafin ya k'ara wata magana.
ADAMAWA STATE
Alhaji Sagir bayan sun dawo da Maryam Kiran mahaifinta ya yi ya sanar da shi masu zuwa ganin gidan amarya sai dai su bari in ta koma zuwa an jima yanzu tana gidan shi .
Mahaifin Muhammad yana gama wayar mai da kallan shi ga Muhammad ya yi ya ce " Muhammad, saboda masu zuwa ganin gidan amarya ka shirya yanzu ku tafi, kudin kar a zo bata nan "
Muhammad shiru ya yi baice komai ba .
Alhaji Sagir ya kuma cewa " Muhammad ba ka ji abin da na ce ba ne, ka tashi ka shirya kafin a fara zuwa ba kowa gidan "
Muhammad ba dan ya so ba sai danne zuciyarshi da ya yi gudin kar ya watsa ma mahaifinsa k'asa a ido ganin duk yana yin hakan ne dan farincikinsa , hakan ya sa cikin sanyi ya ce"Tom, Daddy "
Alhaji Sagir wayar shi ya ciro ya kira Usman abokin Muhammad ya sanar da shi ya zo yanzu.
Alhaji Sagir kallan Muhammad ya yi ya ce"Idan akwai abin da za ka yi na kira Usman ya zo ya kaiku ka yi kafin ya k'araso "
Muhammad kamar zai yi kuka ya ce"Babu abin da zan yi Daddy"
Sunanan zaune Usman ya yi sallama ya shigo.Bayan sun gaggaisa ne alhaji Sagir ya ce" Muhammad ka tashi ku tafi"
Muhammad d'ago kai ya yi yana mai zubar da hawaye ya ce"Daddy , da bakinka kake cewa in tashi in tafi in zauna da wata ba Hafsat ba , Daddy me ya sa ka yi saurin mantawa Hafsat ? Da ace Hafsat zata dawo duniya za ta yi mamakin hakan Daddy"
Kuka ne ya kwace ma Muhammad ,cikin kukan ya ci gaba da cewa "Daddy, ka yi hak'uri ba zan iya zama da kowa ba in ba Hafsat ba, ita kadai idaniyata ke gani,ita kad'ai zuciyata ta yarda ta so,haka ruhina da gangar jikina da ita kad'ai ta aminta za ta yi rayuwa.Haba Daddy me ya sa kuka dage sai kun tursasa ruhina zama da wata ba Hafsat ba? Bacin na yi mata alk'awarin ruhina ba zai taba rayuwa da ruhin wata ba in ba ita ba.Daddy dan Allah ka bar ni in yi rayuwa da Hafsat ita kad'ai"
Daga Hajiya Baturiya har Usman kallan Muhammad kawai suke, Alhaji Sagir ko ya ma rasa abin da zai ce masa.Inda Maryam ta fita d'akin da sauri tana kuka jin zantikan da Muhammad d'in ya ke yi.
Alhaji Sagir dafa Muhammad ya yi cikin damuwa ya ce " Muhammad , ka yi hak'uri Hafsat ta tafi, ta tafi har'abada ba za mu sake ganinta ba sai a mafarki, ka yi hak'uri ka amshi Maryam wadda mahaifinta ya baka ita dan samun kwanciyar hankalinka kaga baikamata mu zuba masa k'asa a ido ba, da Maryam da Hafsat duk kusan d'aya ne awajanja, yadda Hafsat take k'anwarka Maryam ma k'anwarka ce ahankali watarana za ka sota itama "
Haka dai suka taru suka yi ta ba Muhammad ba ki a haka suka samu ya tashi.Saidai ana dubawa kuma ba Maryam.
Alhaji Sagir kallan Hajiya Baturiya ya yi ya ce " Ina Maryam d'in fa? "
Hajiya Baturiya cikin mamaki ta ce"Muna nan tare da ita fa bari in dubata muga "
Hajiya Baturiya a falonta ta iske Maryam ta kifa kai a kan caution sai kuka take.
Hajiya Baturiya da sauri ta k'arasa wajan Maryam tana d'agota tana cewa "Haba Maryam ki yi hak'uri kin ji ki yi ma Muhammad uziri , har yanzu yana cikin damuwar rad'ad'in mutuwar Hafsat, kuma yadda abin ya yi kusa babu nisa tsakani dole sai kin yi hak'uri har ya fara mantawa, kin ji 'yata ? "
Maryam d'aga kai ta yi.
Hajiya Baturiya ta ce"Yauwa, ko ke fa , share hawayanki "
Hajiya Baturiya tana rik'e da hannun Maryam suka k'arasa har in da Usaman ya yi parking suna jiran Maryam.
Suna zuwa Maryam ta shiga suka yi musu sallama su ka tafi.
Suna zuwa k'ofar gidan masu gadin suka bud'e musu suka shiga tank'ameman falon amaryar wanda ya ji kayan alatu da abubuwan more rayuwa.
Maryam ko har yanzu ta kasa na tsuwa ta saki jikinta, dan ta gama furgita da jin kalaman angon nata akan marigayiyar amaryarshi .
Usman lura da hakan da ya yi ne, ya kalli Muhammad da ke kwance kan three seater kanshi a sama kamar wani sabon maraya ya ce"Muhammad, da farko dai ina son in ce maka ka ji tsoran Allah ka rik'e Maryam amana, Hafsat kuma a halin yanzu tana buk'atar addu'arka ne ta haka ne zaka nuna mata soyayyar da kake mata, amma kukan da kake yi mata azaba ne a gareta,Manza Alllah (S.A.W) Ya ce ana ma mamaci a zaba da kukan wanda yake da rai"
Shiru Usman ya yi sannan ya maida kallanshi gun Maryam ya ce" Maryam, na dawo gareki, da farko dai abun da nake son in ce miki , sai kin daure kinsa hak'uri da juriya kafin ki samu komai ya wuce, ki daure kar ki sa gajiyawa dan Allah. Ina mai yi miki albishir d'in za ki ji dad'in zama da abokina , Muhammad ba shi da wata matsala ga shi da tausayi da son fita hak'in duk wanda wata hurd'a ta had'a shi da shi, hakan ne ya sa nake mai kyakkyawan zaton adalci agareki , sboda shi d'in adaline mai tausan na k'asa da shi "
Usman sosai ya yi musu nasiha da jan hankali akan zaman aure sannan ya tafi.
KADUNA GARIN GWAMNA
Fadila cikin sanyi ta k'arasa office d'insu, kasan cewar Jamilu ya sanar da dawowar Fadila aiki babu wani mamaki da abokan aikinta su ka yi.
Bayan sun gaggaisa ne, Jamilu ya fara nuna ma Fadila shirin da za su tattauna yau akan shi.
Fadila na zama babu dad'ewa ,Jamilu ya kalleta ya ce"Lokaci fa ya yi mu je "
Kamar yadda kuka sani kuke kallo haka Fadila ta fara gabatar da Shirin da take aiki akai.
Zaune take ad'akin gabatar da Shirin nasu ga masu aikin d'aukar shirin, komai dai an shirya kamar dai yadda kuke kallo a TV.
Fadila ta fara magana kamar haka"Assalamu alaikum barkamu da sake saduwa da ku acikin shirinmu mai suna DARAJAR 'YA MACE, wanda ni Fadila Sani nake gabatar muku tare da Jamilu Hassan.DARAJAR 'Ya mace,in ji Hausawa suka ce aure "
Yau za mu yi bayanine akan ta yarda ake gane fiffofin mace mai daraja.
Fadila mai da kallanta ga Jamilu ta yi ta ci gaba da magana kamar haka, "Malam Jamilu, shin taya ake gane siffofin mace mai daraja? "
Fadila cikin sanyi ta ce "Zan koma wajan aiki , jiya mama ta ke sanar da ni ka amince in koma"
Mahaifin Fadila shiru ya yi yana kallanta kamar ba zai bata amsa ba dan har ta cire rai ma sannan ya Kira sunanta ya ce"Fadila "
Fadila cikin sanyi ta amsa da "Na'am ,Baba"
Ya ci gaba da cewa"Fadila , dan Allah ki ci gaba da tafiya kamar yadda na sanki , kwanakin baya surutun mutane da kuma tsoron bakin mutane akanki ya sa na dakatar da ke aiki ba wai dan na yarda da abin da su ke cewa ba" Shiru mahaifin Fadila ya yi sannan ya ci gaba da cewa"Fadila , ki sani duk abin da za ki yi Allah na kallanki , tashi ki tafi Allah ya tsare "
Fadila cikin sanyi ta tashi tana mai amsawa da "Ameen ,Baba"
Misalin k'arfe takwas (8:00AM) Fadila ta shiga Rahama TV tana zuwa office din MD ta shiga.
Kamar a mafarki haka ya ga Fadila.Seat d'in da ke facing d'in shi ya nuna mata alamun ta zauna.
Bayan Fadila ta zauna ne ya ce"Fadila , me na yi miki kike son fasa zuciyata? Tun da kika bar zuwa aiki ban tab'a kiranki kika d'aga ba? "
Fadila ji ta yi kunya ta gamata, saboda kodan alfarmar da ya ke yi mata be cancanci ta yi mai haka ba , saidai ba daga ita bane daga zuciyarta ne ,zuciyarta ta ka sa aminta da shi bare kuma har ta yi waya da shi.
Fadila cikin alamun ban hak'uri ta had'a hannuwanta ta ce"Afuwa rankashi dad'e , kana kirana duk bana kusa da Wayar ne , kuma babu kati a wayar bare in biyoka "
Shiru ya yi sannan ya ce" Shi kenan Fadila za ki iya zuwa ki ci gaba da aikinki , saboda ganinki na sa zuciyata cikin damuwa "
Fadila ta shi ta yi ta ce"Shi kenan bari in tafi ba zan so in zama silar damuwarka ba,in da ganina damuwa ya ke saka"
Da sauri ya tashi ya sha gabanta ya ce"Tsaya mana, ba haka nake nufi ba, ke d'in ce kin kasance wani abu mai girma gaske a zuciyata ,da zaki yarda da sai in ce miki ban tab'a so wani abu kamar ki ba, dan Allah ki ban dama mana Fadila?"
Fadila tafe kai ta yi, dan dama tunaninta kenan na dawowa aiki daga ta dawo MD zai fara ta kura mata da maganganun shi da baya gajiya.
Fadila cikin k'osawa tabar Office d'in shi ta ce"Shi kenan, zan yi tunani"
Kai MD ya girgiza ya ce " A'a , Kullum haka kike ce min , ki ban amsa ta kawai ko zuciyata zata samu sukuni dan Allah "
Fadila tana tsoran ta furta mai kalmar k'i ta zo ta samu matsala a wajan aiki ga shi a halin yanzu tana buk'ar aikin sosai, hakan ya sa cikin sanyi ta ce"Shi kenan, zan ba Jamilu sak'o ya baka "
Tana fad'in haka ta fita office d'in da sauri kafin ya k'ara wata magana.
ADAMAWA STATE
Alhaji Sagir bayan sun dawo da Maryam Kiran mahaifinta ya yi ya sanar da shi masu zuwa ganin gidan amarya sai dai su bari in ta koma zuwa an jima yanzu tana gidan shi .
Mahaifin Muhammad yana gama wayar mai da kallan shi ga Muhammad ya yi ya ce " Muhammad, saboda masu zuwa ganin gidan amarya ka shirya yanzu ku tafi, kudin kar a zo bata nan "
Muhammad shiru ya yi baice komai ba .
Alhaji Sagir ya kuma cewa " Muhammad ba ka ji abin da na ce ba ne, ka tashi ka shirya kafin a fara zuwa ba kowa gidan "
Muhammad ba dan ya so ba sai danne zuciyarshi da ya yi gudin kar ya watsa ma mahaifinsa k'asa a ido ganin duk yana yin hakan ne dan farincikinsa , hakan ya sa cikin sanyi ya ce"Tom, Daddy "
Alhaji Sagir wayar shi ya ciro ya kira Usman abokin Muhammad ya sanar da shi ya zo yanzu.
Alhaji Sagir kallan Muhammad ya yi ya ce"Idan akwai abin da za ka yi na kira Usman ya zo ya kaiku ka yi kafin ya k'araso "
Muhammad kamar zai yi kuka ya ce"Babu abin da zan yi Daddy"
Sunanan zaune Usman ya yi sallama ya shigo.Bayan sun gaggaisa ne alhaji Sagir ya ce" Muhammad ka tashi ku tafi"
Muhammad d'ago kai ya yi yana mai zubar da hawaye ya ce"Daddy , da bakinka kake cewa in tashi in tafi in zauna da wata ba Hafsat ba , Daddy me ya sa ka yi saurin mantawa Hafsat ? Da ace Hafsat zata dawo duniya za ta yi mamakin hakan Daddy"
Kuka ne ya kwace ma Muhammad ,cikin kukan ya ci gaba da cewa "Daddy, ka yi hak'uri ba zan iya zama da kowa ba in ba Hafsat ba, ita kadai idaniyata ke gani,ita kad'ai zuciyata ta yarda ta so,haka ruhina da gangar jikina da ita kad'ai ta aminta za ta yi rayuwa.Haba Daddy me ya sa kuka dage sai kun tursasa ruhina zama da wata ba Hafsat ba? Bacin na yi mata alk'awarin ruhina ba zai taba rayuwa da ruhin wata ba in ba ita ba.Daddy dan Allah ka bar ni in yi rayuwa da Hafsat ita kad'ai"
Daga Hajiya Baturiya har Usman kallan Muhammad kawai suke, Alhaji Sagir ko ya ma rasa abin da zai ce masa.Inda Maryam ta fita d'akin da sauri tana kuka jin zantikan da Muhammad d'in ya ke yi.
Alhaji Sagir dafa Muhammad ya yi cikin damuwa ya ce " Muhammad , ka yi hak'uri Hafsat ta tafi, ta tafi har'abada ba za mu sake ganinta ba sai a mafarki, ka yi hak'uri ka amshi Maryam wadda mahaifinta ya baka ita dan samun kwanciyar hankalinka kaga baikamata mu zuba masa k'asa a ido ba, da Maryam da Hafsat duk kusan d'aya ne awajanja, yadda Hafsat take k'anwarka Maryam ma k'anwarka ce ahankali watarana za ka sota itama "
Haka dai suka taru suka yi ta ba Muhammad ba ki a haka suka samu ya tashi.Saidai ana dubawa kuma ba Maryam.
Alhaji Sagir kallan Hajiya Baturiya ya yi ya ce " Ina Maryam d'in fa? "
Hajiya Baturiya cikin mamaki ta ce"Muna nan tare da ita fa bari in dubata muga "
Hajiya Baturiya a falonta ta iske Maryam ta kifa kai a kan caution sai kuka take.
Hajiya Baturiya da sauri ta k'arasa wajan Maryam tana d'agota tana cewa "Haba Maryam ki yi hak'uri kin ji ki yi ma Muhammad uziri , har yanzu yana cikin damuwar rad'ad'in mutuwar Hafsat, kuma yadda abin ya yi kusa babu nisa tsakani dole sai kin yi hak'uri har ya fara mantawa, kin ji 'yata ? "
Maryam d'aga kai ta yi.
Hajiya Baturiya ta ce"Yauwa, ko ke fa , share hawayanki "
Hajiya Baturiya tana rik'e da hannun Maryam suka k'arasa har in da Usaman ya yi parking suna jiran Maryam.
Suna zuwa Maryam ta shiga suka yi musu sallama su ka tafi.
Suna zuwa k'ofar gidan masu gadin suka bud'e musu suka shiga tank'ameman falon amaryar wanda ya ji kayan alatu da abubuwan more rayuwa.
Maryam ko har yanzu ta kasa na tsuwa ta saki jikinta, dan ta gama furgita da jin kalaman angon nata akan marigayiyar amaryarshi .
Usman lura da hakan da ya yi ne, ya kalli Muhammad da ke kwance kan three seater kanshi a sama kamar wani sabon maraya ya ce"Muhammad, da farko dai ina son in ce maka ka ji tsoran Allah ka rik'e Maryam amana, Hafsat kuma a halin yanzu tana buk'atar addu'arka ne ta haka ne zaka nuna mata soyayyar da kake mata, amma kukan da kake yi mata azaba ne a gareta,Manza Alllah (S.A.W) Ya ce ana ma mamaci a zaba da kukan wanda yake da rai"
Shiru Usman ya yi sannan ya maida kallanshi gun Maryam ya ce" Maryam, na dawo gareki, da farko dai abun da nake son in ce miki , sai kin daure kinsa hak'uri da juriya kafin ki samu komai ya wuce, ki daure kar ki sa gajiyawa dan Allah. Ina mai yi miki albishir d'in za ki ji dad'in zama da abokina , Muhammad ba shi da wata matsala ga shi da tausayi da son fita hak'in duk wanda wata hurd'a ta had'a shi da shi, hakan ne ya sa nake mai kyakkyawan zaton adalci agareki , sboda shi d'in adaline mai tausan na k'asa da shi "
Usman sosai ya yi musu nasiha da jan hankali akan zaman aure sannan ya tafi.
KADUNA GARIN GWAMNA
Fadila cikin sanyi ta k'arasa office d'insu, kasan cewar Jamilu ya sanar da dawowar Fadila aiki babu wani mamaki da abokan aikinta su ka yi.
Bayan sun gaggaisa ne, Jamilu ya fara nuna ma Fadila shirin da za su tattauna yau akan shi.
Fadila na zama babu dad'ewa ,Jamilu ya kalleta ya ce"Lokaci fa ya yi mu je "
Kamar yadda kuka sani kuke kallo haka Fadila ta fara gabatar da Shirin da take aiki akai.
Zaune take ad'akin gabatar da Shirin nasu ga masu aikin d'aukar shirin, komai dai an shirya kamar dai yadda kuke kallo a TV.
Fadila ta fara magana kamar haka"Assalamu alaikum barkamu da sake saduwa da ku acikin shirinmu mai suna DARAJAR 'YA MACE, wanda ni Fadila Sani nake gabatar muku tare da Jamilu Hassan.DARAJAR 'Ya mace,in ji Hausawa suka ce aure "
Yau za mu yi bayanine akan ta yarda ake gane fiffofin mace mai daraja.
Fadila mai da kallanta ga Jamilu ta yi ta ci gaba da magana kamar haka, "Malam Jamilu, shin taya ake gane siffofin mace mai daraja? "