Sashe 4
Fadeelah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Muhammad na zaune hajiya baturiya ta tasa shi kamar za ta yi kuka tana lallab'arshi akan ya daure ya ci abinci,ana cikin haka ne mahaifinshi alhaji Sagir da abokin shi suka shigo falon.
Alhaji Bala abokin Alhaji Sagir ,zama ya yi gefan Muhammad ya na dafa shi cikin alamun tausayawa ya ce"Muhammad, ka yi hak'uri ka ji ka saki ranka ka dawo rayuwa kamar da,Hafsat lokacin ta ne ya yi In ba haka ba babu wanda ya isa ya d'auki rayuwarta.
Haka alhaji Bala da mahaifin Muhammad suka ta sa Muhammad sai na siha da lallashi suke mai,amma har suka yi su ka gama Muhammad bai d'auki abinciccikin da aka aje mai a gaban shi ba ko d'aya.Haka suka gaji suka tashi suka barshi.
Falon Alhaji Sagir suka koma suka zauna,bacin sun zauna ne alhaji Bala ya kalli alhaji Sagir ya ce"Alhaji, ni fa ina ganin aima Muhammad wani auran cikin satin nan,kila a samu kwanciyar hankalinsa,dan gaskiya yanda na ga Muhammad abin ya ta da min hankali"
Shiru alhaji Sagir ya yi sannan zuwa can ya ce "Ni ma na yi tunanin haka? Amma wa zan aura wa Muhammad shi ne abun tunanin? " Maryam yarinyar wajena ita za a aura mai ✍🏻
📚 FADEELAH 📚
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
_{Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen Hausa
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=337435884671992&id=103920888023494&sfnsn=mo
💪🏻J.A.W 💪🏻
Na
Fadila Sani Bakori
SANARWA: Masu tambaya akan gyaran jiki akwai hanyoyi kala daban-daban da zan kawo muku na gyaran jiki a cikin wannan littafi mai suna FADEELAH.
Page 3
Falon alhaji Sagir Suka koma suka zauna ,bacin sun zauna ne alhaji Bala ya kalli alhaji Sagir ya ce"Alhaji,ni fa ina ganin a yi ma Muhammad wani auran cikin satin nan ,kila a samu kwanciyar hankalinsa,dan gaskiya yanda na ga Muhammad abin ya tadamin hankali sosai"
Shiru alhaji Sagir ya yi sannan zuwa can ya ce"Ni ma na yi tunanin haka ,amma wa zan aura wa Muhammad ?Shi ne abun tunanin"
Maryam,yarinyar wajena ita za a aura mai cikin satin nan kuwa in sha Allah"
Mahaifin Muhammad hanun alhaji Bala ya kamo ya na cewa"Na gode sos...."Dakatar da shi alhaji Bala ya yi ta hanyar cewa"Haba ai yi ma kaine,babu godiya tsakaninmu dan na yi ma Muhammad wani abu"
KADUNA GARIN GWAMNA
Bikin Fadila yanzu saura sati shida inda har yanzu ta na kan bakarta na ba za ta auri Jamilu ba.Mahaifin Fadila ko ya ce babu gudu babu ja da baya aure kamar ma an yi sa ne.Haka aka ci gaba da shirye-shiryan biki.
Yau kwananan Jamilu goma kenan rabanshi da zuwa wajan Fadila,inda ko ya je shi ke kid'ansa shi ke rawar shi,Fadila ba ta tankamai.
Fadila na zaune ta yi shiru kamar kullum,k'anwarta ta zo ta sanar da ita Jamilu na d'akin Babansu wai ta zo. Tun da aka tsaida ranar auransu Mahaifin Fadila ya ce su rika shiga d'akinshi suna fira.
Fadila tashi ta yi ta sa hijab dinta ta nufi d'akin mahaifinta.
Fadila zama ta yi ba tare da ta tankamai ba.
Jamilu kallanta ya yi ya ce"Barka da zuwa malama Fadila,da fatan kina lafiya? Ina Kiran wayarki amma baki d'agawa,hankakina ya tashi na ce bari in zo in ji lafiya,daga nan inga kyakkyawar fuskarki"Ba na kusa ne"Fadila ta ba shi amsa a tak'aice,sannan ta d'ora da cewa"Jamilu,ina son in fallasamaka abin da ke cikin zuciyata,saidai babu lallai ba dole ka aminta da abin da zan ce,amma kuma duk abin da ya biyo baya ban yaudareka ba,kuma ban d'auki alhakinka ba.Magana guda d'aya ta gaskiya ita ce,Zuciyata ta kasa aminta da taka zuciyar,na yi iya k'ok'arin ganin na tursasata amma abin ya ci tura,atakaice har rauni na yi mata wajan jajircewa da bujire mata akan aminta da kai amma ta k'i,ina had'aka da girman Allah ka yi hak'uri ka hak'ura da zuciyar da ta kasa aminta da kai ka janye maganar da ke tsakaninmu,saboda ko ka aure ni zai zamana gangar jikina kadai zaka aura"
Jamilu shiru ya yi zufa na keto mai kota ina,daga k'arshe ma ba tare da ya tanka ba ya tashi ya tafi.
Yau sati d'aya kenan da Fadila ta sanar da Jamilu akan ya janye maganar auranta,saidai har yanzu ba ta ji wata magana ba mai kama da an janye
,saidai tun daga ranar Jamilu bai kuma kiranta a waya ba,saidai akwai abu d'aya da ta lura da shi mahaifinta kwana uku kenan baya amsa gaisuwarta,yau ne kuma ta k'udirci tuntub'ar mahaifiyarta dan jin ko ta yi ma mahaifinta wani laifi ne.
Mahaifiyar Fadila da daddare bayan ta idar da sallar magriba ta na zaune kan sallaya Fadila ta zo ta zauna gefan mahaifiyar tata,shiru-shiru kamar mai tunanin ta in da za ta fara,sannan ta ce"Mama,kwana biyu idan na gaida baba baya amsawa dan Allah ko na yi mai wani laifi ne Wanda ni ban sani ba?"
Mahaifiyar Fadila d'ago kai ta yi tana kallan Fadila,sannan ta girgiza kai ta ce"Tom,Fadila ni in kin yi mai wani abu ma ban sani ba,dan bai fad'amin ba,saidai in ya dawo ki je ki tambaye shi ki ji"
Fadila cikin marairaicewa ta kalli mahaifiyarta ta ce"Mama,dan Allah ki mai magana da kanki kin ga ni ba zan iya yi mai ba"Tom,shi kenan sai ki hak'ura ,dan nima ba zan iya yi mai ba."
Fadila haka ta hak'ura ta tashi.
Haka rayuwa ta ci gaba da tafiya,in da ya rage har saura sati d'aya d'aurin auran Fadila kamar yadda mahaifinta ya sa.
Fadila ko yanzu abin da ke damunta bai wuce na gaisuwarta da mahaifinta ya bar amsamata ba.
Jamilu ko har yanzu tun da ta yi mai maganar nan bai kuma kiranta a waya ba.
Fadila har ya kama saura kwana uku biki bata ga ana wani shirye-shirye shirye na biki ba,haka ya tabbatar mata da babu bakin kenan,kuma dama ta dad'e tana zargin hakan.
Yau ne ya kama ranar da za'a daura auran Fadila kamar yadda mahaifinta ya tsaida,amma kuma shiru ka ke ji.
Fadila sosai ta yi murna da hakan,amma b'angare d'aya na zuciyarta cikin fargabar mahaifinta ta ke.
Da daddare Fadila na kwance mahaifinta ya aiko kiranta.
Fadila koda ta je ta dad'e a tsuk'unne ba tare da ya tanka mata ba,kamar ba zai tanka mata ba sai zuwa can ya ce"Fadila, kin maida ni karamin mutum, mutumin banza mai k'aramar magana,dama mutane na namin kallan wanda baisan abin da ya ke ba na je kamar ki a gida ba aure,idan an ce rashin mijine yanzu gashi mijin ya zo kin korai.Yanzu fad'amin me ye nufinki in ji?"
Fadila shiru ba amsa.Mahaifinta ko ya ci gaba da cewa"Fadila,Allah ya sa ni na fita hak'inki,na baki ilimin na addini da na zamani,na had'aki da mijin aure har uku duk kin k'i kin nuna min ke wayayyiyace ba aure ba ne a gabanki,dan haka ga mahaifiyarki nan ta zama shaida"Mahaifin Fadila dakatawa ya yi ya na kallan mahaifiyar Fadila,sannan ya ci gaba da cewa"Watan uku muke ko?"Kai mahaifiyar Fadila ta d'aga alamun haka ne. Ya ce "Kafin nan da k'arshan shekarar nan in dai Fadila ba ta kawo wanda take jin zata iya aura ba,Wallahi Allah d'aya na gama zama da ita acikin gidan nan,saidai ta san in da zata zauna amma ta gama zamam min a gida in dai wannan wa'adin ya cika"
Fadila shuru ta yi kanta a k'asa.Mahaifin Fadila kallanta ya yi ya ce"Idan har muka kai watan sha biyu ba tare da kin kawo daidai da ke din da kike jin za ki aura ba,karki kuskura in zo in iskeki a gidana ,ba dai gidana ba Wallahi saidai ki naimi wajan zama"
Mahaifin Fadila sai da ya kuma nanata ma Fadila akan karka kuskura ta k'are shekarar nan ba tare da wata magana ba,sannan ya ce ta tashi ta bashi waje.
ADAMAWA STATE
Alhaji Bala yana komawa gida ya sanar da matarsa hajiya Halima maganar ba da Maryam da ya yi ga Muhammad.
Hajiya Halima sosai ta ji dad'in maganar ,dan Alhaji Sagir mai shadda abin alfahari ne ka had'a iri da shi.
B'angaran Maryam ma ko da mahaifiyarta ta tareta da maganar take ta amince babu ja.
Mahaifin Muhammad ko da ya sanar da hajiya baturiya ta ji dad'in hakan,dan acewarta k'ila hakan ya kwantar ma Muhammad da hankali.
Da daddare alhaji Sagir ya samu Muhammed da maganar.Amma har ya yi maganar shi ya gama Muhammad bai tankamai ba.Hajiya baturiya ta ce"Muhammad,ba ka ji abin da daddynka ya ce bane,sun yanke shawarar had'aka da Maryam yarinyar alhaji Bala aure,saboda tunanin hakan ko zai sa ka kwantar da hankalinka"
Muhammad da ya rasa abin cewa,kuma baya son gwalishe mahaifinsa hakan ya sa ya ce"Tom,mommy"
Hajiya baturiya za ta sake magana alhaji Sagir ya d'aga mata hannu alamun ta yi shiru.
Kwana goma suka tsaida auran,hakan ya sa b'angaran amaryar suka ci gaba da shirye-shiryan biki,inda b'angaran alhaji Sagir babu wani shiri da su ke yi.Maganar lefe ma alhaji Sagir kud'i ya ba su ya ce su yi komai.
B'angaran Muhammad ko yama manta da maganar wani aure da za a yi mai.
Ranar da ta kama d'aurin aure ba wani taro a ka yi ba,garama gidan su Maryam d'in sosai su ke shirin auran.
Ranar Juma'a da safe aka d'aura auran Maryam da Muhammad,in da ba wani taro a ka yi ba na ku zo ku gani.
Lokacin da labarin d'aurin auran ya isa kunnan Muhammad,sosai abin ya d'aga mai hankali ,dan sai da a ka Kira alhaji Sagir aka sanar da shi halin da Muhammad d'in ya ke ciki.
Alhaji Sagir sosai hankalinshi ya tashi ganin yarda Muhammad ya ke kuka.Babu irin lallashin da alhaji Sagir bai yi mai ba,amma kamar ma ba da shi ya ke ba.
Alhaji Sagir ganin yadda Muhammad ya ke kuka ko ranar da Hafsat ta rasu ma bai yi kuka haka ba,hakan ya sa cikin tashin hankali da damuwa ya ce"Muhammad, ko auran ne ba ka so?"
Muhammad cikin kuka ya d'aga ma mahaifinshi kai ya ce"Daddy ,bana son auran nan dan Allah,mu yi alk'awari da Hafsat ba zan tab'a auran wata in ba ita b..." Muhammad ya karashe maganar cikin tsantsar kuka da bayyanar tsantsar ta shin hankali a tare da shi.
Alhaji Bala abokin Alhaji Sagir ,zama ya yi gefan Muhammad ya na dafa shi cikin alamun tausayawa ya ce"Muhammad, ka yi hak'uri ka ji ka saki ranka ka dawo rayuwa kamar da,Hafsat lokacin ta ne ya yi In ba haka ba babu wanda ya isa ya d'auki rayuwarta.
Haka alhaji Bala da mahaifin Muhammad suka ta sa Muhammad sai na siha da lallashi suke mai,amma har suka yi su ka gama Muhammad bai d'auki abinciccikin da aka aje mai a gaban shi ba ko d'aya.Haka suka gaji suka tashi suka barshi.
Falon Alhaji Sagir suka koma suka zauna,bacin sun zauna ne alhaji Bala ya kalli alhaji Sagir ya ce"Alhaji, ni fa ina ganin aima Muhammad wani auran cikin satin nan,kila a samu kwanciyar hankalinsa,dan gaskiya yanda na ga Muhammad abin ya ta da min hankali"
Shiru alhaji Sagir ya yi sannan zuwa can ya ce "Ni ma na yi tunanin haka? Amma wa zan aura wa Muhammad shi ne abun tunanin? " Maryam yarinyar wajena ita za a aura mai ✍🏻
📚 FADEELAH 📚
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
_{Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen Hausa
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=337435884671992&id=103920888023494&sfnsn=mo
💪🏻J.A.W 💪🏻
Na
Fadila Sani Bakori
SANARWA: Masu tambaya akan gyaran jiki akwai hanyoyi kala daban-daban da zan kawo muku na gyaran jiki a cikin wannan littafi mai suna FADEELAH.
Page 3
Falon alhaji Sagir Suka koma suka zauna ,bacin sun zauna ne alhaji Bala ya kalli alhaji Sagir ya ce"Alhaji,ni fa ina ganin a yi ma Muhammad wani auran cikin satin nan ,kila a samu kwanciyar hankalinsa,dan gaskiya yanda na ga Muhammad abin ya tadamin hankali sosai"
Shiru alhaji Sagir ya yi sannan zuwa can ya ce"Ni ma na yi tunanin haka ,amma wa zan aura wa Muhammad ?Shi ne abun tunanin"
Maryam,yarinyar wajena ita za a aura mai cikin satin nan kuwa in sha Allah"
Mahaifin Muhammad hanun alhaji Bala ya kamo ya na cewa"Na gode sos...."Dakatar da shi alhaji Bala ya yi ta hanyar cewa"Haba ai yi ma kaine,babu godiya tsakaninmu dan na yi ma Muhammad wani abu"
KADUNA GARIN GWAMNA
Bikin Fadila yanzu saura sati shida inda har yanzu ta na kan bakarta na ba za ta auri Jamilu ba.Mahaifin Fadila ko ya ce babu gudu babu ja da baya aure kamar ma an yi sa ne.Haka aka ci gaba da shirye-shiryan biki.
Yau kwananan Jamilu goma kenan rabanshi da zuwa wajan Fadila,inda ko ya je shi ke kid'ansa shi ke rawar shi,Fadila ba ta tankamai.
Fadila na zaune ta yi shiru kamar kullum,k'anwarta ta zo ta sanar da ita Jamilu na d'akin Babansu wai ta zo. Tun da aka tsaida ranar auransu Mahaifin Fadila ya ce su rika shiga d'akinshi suna fira.
Fadila tashi ta yi ta sa hijab dinta ta nufi d'akin mahaifinta.
Fadila zama ta yi ba tare da ta tankamai ba.
Jamilu kallanta ya yi ya ce"Barka da zuwa malama Fadila,da fatan kina lafiya? Ina Kiran wayarki amma baki d'agawa,hankakina ya tashi na ce bari in zo in ji lafiya,daga nan inga kyakkyawar fuskarki"Ba na kusa ne"Fadila ta ba shi amsa a tak'aice,sannan ta d'ora da cewa"Jamilu,ina son in fallasamaka abin da ke cikin zuciyata,saidai babu lallai ba dole ka aminta da abin da zan ce,amma kuma duk abin da ya biyo baya ban yaudareka ba,kuma ban d'auki alhakinka ba.Magana guda d'aya ta gaskiya ita ce,Zuciyata ta kasa aminta da taka zuciyar,na yi iya k'ok'arin ganin na tursasata amma abin ya ci tura,atakaice har rauni na yi mata wajan jajircewa da bujire mata akan aminta da kai amma ta k'i,ina had'aka da girman Allah ka yi hak'uri ka hak'ura da zuciyar da ta kasa aminta da kai ka janye maganar da ke tsakaninmu,saboda ko ka aure ni zai zamana gangar jikina kadai zaka aura"
Jamilu shiru ya yi zufa na keto mai kota ina,daga k'arshe ma ba tare da ya tanka ba ya tashi ya tafi.
Yau sati d'aya kenan da Fadila ta sanar da Jamilu akan ya janye maganar auranta,saidai har yanzu ba ta ji wata magana ba mai kama da an janye
,saidai tun daga ranar Jamilu bai kuma kiranta a waya ba,saidai akwai abu d'aya da ta lura da shi mahaifinta kwana uku kenan baya amsa gaisuwarta,yau ne kuma ta k'udirci tuntub'ar mahaifiyarta dan jin ko ta yi ma mahaifinta wani laifi ne.
Mahaifiyar Fadila da daddare bayan ta idar da sallar magriba ta na zaune kan sallaya Fadila ta zo ta zauna gefan mahaifiyar tata,shiru-shiru kamar mai tunanin ta in da za ta fara,sannan ta ce"Mama,kwana biyu idan na gaida baba baya amsawa dan Allah ko na yi mai wani laifi ne Wanda ni ban sani ba?"
Mahaifiyar Fadila d'ago kai ta yi tana kallan Fadila,sannan ta girgiza kai ta ce"Tom,Fadila ni in kin yi mai wani abu ma ban sani ba,dan bai fad'amin ba,saidai in ya dawo ki je ki tambaye shi ki ji"
Fadila cikin marairaicewa ta kalli mahaifiyarta ta ce"Mama,dan Allah ki mai magana da kanki kin ga ni ba zan iya yi mai ba"Tom,shi kenan sai ki hak'ura ,dan nima ba zan iya yi mai ba."
Fadila haka ta hak'ura ta tashi.
Haka rayuwa ta ci gaba da tafiya,in da ya rage har saura sati d'aya d'aurin auran Fadila kamar yadda mahaifinta ya sa.
Fadila ko yanzu abin da ke damunta bai wuce na gaisuwarta da mahaifinta ya bar amsamata ba.
Jamilu ko har yanzu tun da ta yi mai maganar nan bai kuma kiranta a waya ba.
Fadila har ya kama saura kwana uku biki bata ga ana wani shirye-shirye shirye na biki ba,haka ya tabbatar mata da babu bakin kenan,kuma dama ta dad'e tana zargin hakan.
Yau ne ya kama ranar da za'a daura auran Fadila kamar yadda mahaifinta ya tsaida,amma kuma shiru ka ke ji.
Fadila sosai ta yi murna da hakan,amma b'angare d'aya na zuciyarta cikin fargabar mahaifinta ta ke.
Da daddare Fadila na kwance mahaifinta ya aiko kiranta.
Fadila koda ta je ta dad'e a tsuk'unne ba tare da ya tanka mata ba,kamar ba zai tanka mata ba sai zuwa can ya ce"Fadila, kin maida ni karamin mutum, mutumin banza mai k'aramar magana,dama mutane na namin kallan wanda baisan abin da ya ke ba na je kamar ki a gida ba aure,idan an ce rashin mijine yanzu gashi mijin ya zo kin korai.Yanzu fad'amin me ye nufinki in ji?"
Fadila shiru ba amsa.Mahaifinta ko ya ci gaba da cewa"Fadila,Allah ya sa ni na fita hak'inki,na baki ilimin na addini da na zamani,na had'aki da mijin aure har uku duk kin k'i kin nuna min ke wayayyiyace ba aure ba ne a gabanki,dan haka ga mahaifiyarki nan ta zama shaida"Mahaifin Fadila dakatawa ya yi ya na kallan mahaifiyar Fadila,sannan ya ci gaba da cewa"Watan uku muke ko?"Kai mahaifiyar Fadila ta d'aga alamun haka ne. Ya ce "Kafin nan da k'arshan shekarar nan in dai Fadila ba ta kawo wanda take jin zata iya aura ba,Wallahi Allah d'aya na gama zama da ita acikin gidan nan,saidai ta san in da zata zauna amma ta gama zamam min a gida in dai wannan wa'adin ya cika"
Fadila shuru ta yi kanta a k'asa.Mahaifin Fadila kallanta ya yi ya ce"Idan har muka kai watan sha biyu ba tare da kin kawo daidai da ke din da kike jin za ki aura ba,karki kuskura in zo in iskeki a gidana ,ba dai gidana ba Wallahi saidai ki naimi wajan zama"
Mahaifin Fadila sai da ya kuma nanata ma Fadila akan karka kuskura ta k'are shekarar nan ba tare da wata magana ba,sannan ya ce ta tashi ta bashi waje.
ADAMAWA STATE
Alhaji Bala yana komawa gida ya sanar da matarsa hajiya Halima maganar ba da Maryam da ya yi ga Muhammad.
Hajiya Halima sosai ta ji dad'in maganar ,dan Alhaji Sagir mai shadda abin alfahari ne ka had'a iri da shi.
B'angaran Maryam ma ko da mahaifiyarta ta tareta da maganar take ta amince babu ja.
Mahaifin Muhammad ko da ya sanar da hajiya baturiya ta ji dad'in hakan,dan acewarta k'ila hakan ya kwantar ma Muhammad da hankali.
Da daddare alhaji Sagir ya samu Muhammed da maganar.Amma har ya yi maganar shi ya gama Muhammad bai tankamai ba.Hajiya baturiya ta ce"Muhammad,ba ka ji abin da daddynka ya ce bane,sun yanke shawarar had'aka da Maryam yarinyar alhaji Bala aure,saboda tunanin hakan ko zai sa ka kwantar da hankalinka"
Muhammad da ya rasa abin cewa,kuma baya son gwalishe mahaifinsa hakan ya sa ya ce"Tom,mommy"
Hajiya baturiya za ta sake magana alhaji Sagir ya d'aga mata hannu alamun ta yi shiru.
Kwana goma suka tsaida auran,hakan ya sa b'angaran amaryar suka ci gaba da shirye-shiryan biki,inda b'angaran alhaji Sagir babu wani shiri da su ke yi.Maganar lefe ma alhaji Sagir kud'i ya ba su ya ce su yi komai.
B'angaran Muhammad ko yama manta da maganar wani aure da za a yi mai.
Ranar da ta kama d'aurin aure ba wani taro a ka yi ba,garama gidan su Maryam d'in sosai su ke shirin auran.
Ranar Juma'a da safe aka d'aura auran Maryam da Muhammad,in da ba wani taro a ka yi ba na ku zo ku gani.
Lokacin da labarin d'aurin auran ya isa kunnan Muhammad,sosai abin ya d'aga mai hankali ,dan sai da a ka Kira alhaji Sagir aka sanar da shi halin da Muhammad d'in ya ke ciki.
Alhaji Sagir sosai hankalinshi ya tashi ganin yarda Muhammad ya ke kuka.Babu irin lallashin da alhaji Sagir bai yi mai ba,amma kamar ma ba da shi ya ke ba.
Alhaji Sagir ganin yadda Muhammad ya ke kuka ko ranar da Hafsat ta rasu ma bai yi kuka haka ba,hakan ya sa cikin tashin hankali da damuwa ya ce"Muhammad, ko auran ne ba ka so?"
Muhammad cikin kuka ya d'aga ma mahaifinshi kai ya ce"Daddy ,bana son auran nan dan Allah,mu yi alk'awari da Hafsat ba zan tab'a auran wata in ba ita b..." Muhammad ya karashe maganar cikin tsantsar kuka da bayyanar tsantsar ta shin hankali a tare da shi.