Sashe 19
Fadeelah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kadija bin bayan Muhammad ta yi da kallo ta ce " Wayyo dace kan dace gaskiya na shigo duniya a sa'a , kyakkyawa ne mai daddadar murya , dole ma in bisa yadda yake so kodan in samu damar mallake zuciyarsa "
Kadija ta dad'e tana sambatunta akan Muhammad sannan ta d'akko ledar da Muhammad ya aje mata . Tana gama lashe -lashenta barci ya kwasheta a wajan.
Muhammad cikin barci ya jiyo gurnanin mutum , tashi ya yi yana fitowa falon da sauri .
Kadija ya gani kwance sai haure - haure take .
Muhammad da sauri ya idasa inda take saidai take ya zazzaro idanunsa ganin Kadija kwance cikin jini an mata yankar rago amma har yanzu ran bai gama fita ba .
Muhammad cikin furgita ya ke nanata " Innalillahi wa inna ilaihirraj'un ! "
Muhammad na nan tsaye kan Kadija har ranta ya fita ya bar gangar jikinta . Muhammad da gaba d'aya tsoro ya fita ranshi da sauri ya bud'e k'ofar falon ya fita , wajan masu gadin gidan ya je hankali tashi , ya na tambayar su waye suka shigomai gida . Sai dai Muhammad a lurar da ya yi gaba d'aya masu gadin basa cikin hayyacinsu , hakan ya sa bai bi takansu ba ya bud'e get d'in ya fita.
Saidai unguwar shiru bai ga komai ba bai ga kowa ba. Ahaka tsabar rud'ewa Muhammad ya kama hanya cikin daran ya isa gidansu a k'afa , Muhammad na zuwa ya yi ta bubbuga get d'in gidan amma shiru sai da ya dade yana yi sannan aka ce " Waye ? " Muhammad ne ku bud'e " Jin muryar Muhammad da sauri suka bud'e get d'in ya shiga.
Da mamaki suka bi Muhammad da kallo dan daga gani ma kamar ba a hayyacinsa ya ke ba . Hakan ya sa kafin Muhammad ya idasa shiga gidan d'aya daga cikin masu gadin da yake na hannun damar Alhaji Sagir ne ya kirashi awaya ya sanar shi ga Muhammad ya zo kuma da alama a furgice ya ke .
Alhaji Sagir cikin tsoro da jin Muhammad ya zo cikin tsakiyar daran nan ya tashi ya fita ya biyoshi . Gaf k'ofar da zata sada Muhammad da falon Alhaji Sagir suka had'e .
Muhammad na ganin mahaifinshi ya ce " Daddy , ka ga ni ko abun da nake tsoro kenan itama sun kasheta , Daddy , an mata yankar rago kamar wa incan "
Iya furgita alhaji Sagir ya furgita da kalaman Muhammad , kama Muhammad d'in ya yi ya zaunar da shi dan ganin kamar ba ya cikin hayyacinsa .
Atakaice dai cikin daran Alhaji Sagir suka je da motar 'yan sanda suka taho da gawar Kadija . Haka dai aka yi duk wasu binciken da za ai akan gawar .
Sosai mahaifin Kadija ya furgita lokacin da sakon mutuwar Kadija ya isarmai . Haka dai ita ma Kadija aka sallaci gawarta aka kaita gidanta na gaskiya .
KADUNA GARIN GWAMNA
Mahaifiyar Fadila haka ta sama kanta hak'uri da dangana dan yanzu har daukar Ahmad take . Yanzu dai atakaice kusan duk sun saki ransu sun dawo rayuwarsu kamar da . Abu d'aya ke damun mahaifiyar Fadila shi ne surutun 'yan unguwa , dan haka nan tana zaune sai taga an shigo gidan wai an zo gaidata da wayan aga dan da Fadila ta haifa .
BAYAN WATA D'AYA
Yanzu watan Fadila d'aya kenan da dawowa gida . Yau Fadila ta samu mahaifiyarta da maganar zata koma aiki.
Maifiyar Fadila shiru ta yi sannan ta ce " Tom , Fadila Allah ya tsareki dan Allah ki kula sosai " Fadila cikin kwantar ma mahaifiyarta da hankali ta ce " Karki damu Mama , babu abin da zai faru dani in sha Allah "
Yau Fadila ta koma aiki , in da MD ya amsheta babu yabo ba fallasa , dan abun da ya ba Fadila mamaki gaisuwarta ma ciki - ciki ya amsa , ta zaci ma zai dakatar da ita aikin ne amma sai ta ji ya ce " Ta je ta samu Jamilu su yi magana " Fadila ta juya zata tafi ne , MD ya ce " Ahmad fa ? " Fadila kamar karta bashi amsa amma sai cewa ta yi " Ahmad yana gida " Kina nufin acan zaki barshi ? In yana kukan abinci fa ?, Gaskiya ba zai yuwu ba sai dai ko ki rik'a zuwa da shi ko kuma ki bar aikin "
Fadila kallan MD kawai ta yi bata tanka mai ba ta fita.
Koda taje ta samu Jamilu take ya sanar da ita akwai aikin da za su yi yanzu haka . Haka Jamilu ya yi ta nuna ma Fadila tsare - tsaran da suka canza . Bayan ya gama nuna mata ne suka gabatar da Shirin da suke gabatarwa tare in da rashin Fadila ya sa suke yi da Ummi .
Bayan sun gama kabatar da shirin ne suka bada damar aiko da sak'onni ta waya ko ta Gmail address nasu . Bayan sun dawo hutun takaitaccan lokaci da suka je ne Fadila ta fara karanto sak'onin kamar haka , ta ce " Mai sakon farko Hassana Sani ta ce " Shin macan da ta haihu agida za'a iya kiranta da sunan mace mai daraja itama ? " Fadila ta gama fad'in sak'on tana kallan Jamilu wanda tasan duk wanda ya yi tambayar nan da ita yake kuma dan ita aka yi .
Jamilu ma ya gane hakan , hakan ya sa ya bada amsa kamar haka " Eh , sosai ma kuwa za'a iya kiranta mace mai daraja itama idan har ya kasance ta hanyar tsautsayine ta same shi "
Abun mamaki tambaya ta biyu ma suna kamancece niya da ta faro , haka dai ita ma Jamilu ya bada amsa a ilimance .
Haka dai suka gama shirin Fadila ranta yana mata duk ba dad'i .
Fadila ta tashi aiki zata tafi gida MD ya tareta ya ce " Fadila, kamar yadda nace miki kodai ki rik'a zuwa da Ahmad aiki dan bai isa barshi a gida ba ko kuma ki dakata da zuwa aikin har ya yi kwari ✍🏻
📚 FADEELAH 📚
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
_{Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=337435884671992&id=103920888023494&sfnsn=mo
💪🏻J.A.W 💪🏻
Na
Fadila Sani Bakori
SANARWA : Masu tambaya akan gyaran jiki akwai hanyoyi kala daban - daban da zan kawo muku na gyaran jiki acikin wannan littafi mai suna FADEELAH .
*🤝 SDEENDTM DATA SERVICES🤝*
*MTN* . *Airtel*
1GB = ₦300. 1GB = ₦300
2GB = ₦600. 2GB = ₦600
3GB = ₦900. 3GB = ₦900
4GB = ₦1200. 4GB = ₦1200
5GB = ₦1500. 5GB = ₦1500
*GLO* . *9MOBILE*
1GB = ₦350. 500Mb ₦250
2GB = ₦700. 1GB ₦500
3GB = ₦1050. 2GB ₦1000
4GB = ₦1400. 3GB ₦1500
5GB = ₦1750. 4GB ₦2000
*VALIDITY: 30DAYS/1MONTH*
For cable subscription or sell recharge card
Call this number or whatsapp
👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽
*🪀08066268951*
Page 12
Fadila ta tashi aiki zata tafi gida , MD ya tare ta ya ce " Fadila , Kamar yadda kika ji na ce miki kodai ki rik'a zuwa da Ahmad aiki ko kuma ki dakata da zuwa aiki har ya yi k'wari "
Fadila juyawa ta yi ta fita ba tare da ta tanka ma MD ba .
Fadila koda ta koma gida bata b'oye ma mahaifiyarta yadda su ka yi da MD ba . Mahaifiyar Fadila shiru ta yi Sannan ta ce " Fadila , kodai MD shi ne mahaifin Ahmad ?" Tom , mama ni ma ban sani ba , amma ni ma ina zargin hakan " Cewar Fadila .
Aisha da ke zaune kusa da su ta ce " Nifa mama da za ku bi ta tawa Wallahi d'aukar yaran nan za'ai akai mai abinsa , dan babu ma makawa d'ansa ne Wallahi " A'a Aisha har yanzu ba mu da wata k'wak'k'warar hujjar da za mu yi haka , amma idan mu ka yi hak'uri Allah zai kawo mana hujjar da za mu kamashi da ita "
Da daddare Fadila tana hau Facebook, anan ta ci karo da posting d'in Usman abokin Muhammad yana cewa " Assalamu alaikum. Jama'a dan Allah ku taya mu addu'a Allah ya kawo ma abokin Muhammad Sagir mai shadda mafita akan halin rayuwar da ya tsinci kansa . Muhammad Sagir auranshi uku kenan , amma daga ankai matan gidansa washegari zai farka aga anyi musu yankar rago , gashi duk wani bincike da kuka sani babu wanda ba mu yi ba , amma har yanzu dai Allah bai bayyana mana wanda suke haka ba . Dan Allah kusa Muhammad Sagir a addu'a Allah ya toni asirin duk mai akatamai haka, idan kuma iskace Allah ya yi mai maganinta "
Fadila haka taita bin comments din jama'a , inda mutane da dama sukan ce " K'ilama al'jana ce ta aurai take ta mai ta'asan nan " Haka dai jama'a kowa da abin da yake cewa .
Fadila shiru ta yi , dan tabbas idan bata manta sunan wanda aka ce ya yi mata aiki ya ciro mata Ahmad ba shi ne , dan tabbas haka ya gabatar da sunan shi ga jama'a ranar taron bikin cikar shekara goma da RAHAMA TV ya yi . " Muhammad Sagir mai Shadda tabbas haka sunan ya ke"
Fadila dan ta cire ma kanta kokwanto Jamilu ta kira , bayan sun gaisa ta ce " Jamilu , dan Allah ko zaka iya tuna min sunan wanda ya yi min theater ya ciro min Ahmad ? " Eh , sunansa Muhammad Sagir mai shadda " Fadila shiru ta yi sanan ta ce " Shi kenan, na gode sai anjima "
Fadila bayan ta kashe wayarta number Muhammad ta kira acewarta ya cancanci ta yi mai gaisuwa . Abun mamaki kira d'aya Muhammad ya d'aga .
Kadija ta dad'e tana sambatunta akan Muhammad sannan ta d'akko ledar da Muhammad ya aje mata . Tana gama lashe -lashenta barci ya kwasheta a wajan.
Muhammad cikin barci ya jiyo gurnanin mutum , tashi ya yi yana fitowa falon da sauri .
Kadija ya gani kwance sai haure - haure take .
Muhammad da sauri ya idasa inda take saidai take ya zazzaro idanunsa ganin Kadija kwance cikin jini an mata yankar rago amma har yanzu ran bai gama fita ba .
Muhammad cikin furgita ya ke nanata " Innalillahi wa inna ilaihirraj'un ! "
Muhammad na nan tsaye kan Kadija har ranta ya fita ya bar gangar jikinta . Muhammad da gaba d'aya tsoro ya fita ranshi da sauri ya bud'e k'ofar falon ya fita , wajan masu gadin gidan ya je hankali tashi , ya na tambayar su waye suka shigomai gida . Sai dai Muhammad a lurar da ya yi gaba d'aya masu gadin basa cikin hayyacinsu , hakan ya sa bai bi takansu ba ya bud'e get d'in ya fita.
Saidai unguwar shiru bai ga komai ba bai ga kowa ba. Ahaka tsabar rud'ewa Muhammad ya kama hanya cikin daran ya isa gidansu a k'afa , Muhammad na zuwa ya yi ta bubbuga get d'in gidan amma shiru sai da ya dade yana yi sannan aka ce " Waye ? " Muhammad ne ku bud'e " Jin muryar Muhammad da sauri suka bud'e get d'in ya shiga.
Da mamaki suka bi Muhammad da kallo dan daga gani ma kamar ba a hayyacinsa ya ke ba . Hakan ya sa kafin Muhammad ya idasa shiga gidan d'aya daga cikin masu gadin da yake na hannun damar Alhaji Sagir ne ya kirashi awaya ya sanar shi ga Muhammad ya zo kuma da alama a furgice ya ke .
Alhaji Sagir cikin tsoro da jin Muhammad ya zo cikin tsakiyar daran nan ya tashi ya fita ya biyoshi . Gaf k'ofar da zata sada Muhammad da falon Alhaji Sagir suka had'e .
Muhammad na ganin mahaifinshi ya ce " Daddy , ka ga ni ko abun da nake tsoro kenan itama sun kasheta , Daddy , an mata yankar rago kamar wa incan "
Iya furgita alhaji Sagir ya furgita da kalaman Muhammad , kama Muhammad d'in ya yi ya zaunar da shi dan ganin kamar ba ya cikin hayyacinsa .
Atakaice dai cikin daran Alhaji Sagir suka je da motar 'yan sanda suka taho da gawar Kadija . Haka dai aka yi duk wasu binciken da za ai akan gawar .
Sosai mahaifin Kadija ya furgita lokacin da sakon mutuwar Kadija ya isarmai . Haka dai ita ma Kadija aka sallaci gawarta aka kaita gidanta na gaskiya .
KADUNA GARIN GWAMNA
Mahaifiyar Fadila haka ta sama kanta hak'uri da dangana dan yanzu har daukar Ahmad take . Yanzu dai atakaice kusan duk sun saki ransu sun dawo rayuwarsu kamar da . Abu d'aya ke damun mahaifiyar Fadila shi ne surutun 'yan unguwa , dan haka nan tana zaune sai taga an shigo gidan wai an zo gaidata da wayan aga dan da Fadila ta haifa .
BAYAN WATA D'AYA
Yanzu watan Fadila d'aya kenan da dawowa gida . Yau Fadila ta samu mahaifiyarta da maganar zata koma aiki.
Maifiyar Fadila shiru ta yi sannan ta ce " Tom , Fadila Allah ya tsareki dan Allah ki kula sosai " Fadila cikin kwantar ma mahaifiyarta da hankali ta ce " Karki damu Mama , babu abin da zai faru dani in sha Allah "
Yau Fadila ta koma aiki , in da MD ya amsheta babu yabo ba fallasa , dan abun da ya ba Fadila mamaki gaisuwarta ma ciki - ciki ya amsa , ta zaci ma zai dakatar da ita aikin ne amma sai ta ji ya ce " Ta je ta samu Jamilu su yi magana " Fadila ta juya zata tafi ne , MD ya ce " Ahmad fa ? " Fadila kamar karta bashi amsa amma sai cewa ta yi " Ahmad yana gida " Kina nufin acan zaki barshi ? In yana kukan abinci fa ?, Gaskiya ba zai yuwu ba sai dai ko ki rik'a zuwa da shi ko kuma ki bar aikin "
Fadila kallan MD kawai ta yi bata tanka mai ba ta fita.
Koda taje ta samu Jamilu take ya sanar da ita akwai aikin da za su yi yanzu haka . Haka Jamilu ya yi ta nuna ma Fadila tsare - tsaran da suka canza . Bayan ya gama nuna mata ne suka gabatar da Shirin da suke gabatarwa tare in da rashin Fadila ya sa suke yi da Ummi .
Bayan sun gama kabatar da shirin ne suka bada damar aiko da sak'onni ta waya ko ta Gmail address nasu . Bayan sun dawo hutun takaitaccan lokaci da suka je ne Fadila ta fara karanto sak'onin kamar haka , ta ce " Mai sakon farko Hassana Sani ta ce " Shin macan da ta haihu agida za'a iya kiranta da sunan mace mai daraja itama ? " Fadila ta gama fad'in sak'on tana kallan Jamilu wanda tasan duk wanda ya yi tambayar nan da ita yake kuma dan ita aka yi .
Jamilu ma ya gane hakan , hakan ya sa ya bada amsa kamar haka " Eh , sosai ma kuwa za'a iya kiranta mace mai daraja itama idan har ya kasance ta hanyar tsautsayine ta same shi "
Abun mamaki tambaya ta biyu ma suna kamancece niya da ta faro , haka dai ita ma Jamilu ya bada amsa a ilimance .
Haka dai suka gama shirin Fadila ranta yana mata duk ba dad'i .
Fadila ta tashi aiki zata tafi gida MD ya tareta ya ce " Fadila, kamar yadda nace miki kodai ki rik'a zuwa da Ahmad aiki dan bai isa barshi a gida ba ko kuma ki dakata da zuwa aikin har ya yi kwari ✍🏻
📚 FADEELAH 📚
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
_{Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=337435884671992&id=103920888023494&sfnsn=mo
💪🏻J.A.W 💪🏻
Na
Fadila Sani Bakori
SANARWA : Masu tambaya akan gyaran jiki akwai hanyoyi kala daban - daban da zan kawo muku na gyaran jiki acikin wannan littafi mai suna FADEELAH .
*🤝 SDEENDTM DATA SERVICES🤝*
*MTN* . *Airtel*
1GB = ₦300. 1GB = ₦300
2GB = ₦600. 2GB = ₦600
3GB = ₦900. 3GB = ₦900
4GB = ₦1200. 4GB = ₦1200
5GB = ₦1500. 5GB = ₦1500
*GLO* . *9MOBILE*
1GB = ₦350. 500Mb ₦250
2GB = ₦700. 1GB ₦500
3GB = ₦1050. 2GB ₦1000
4GB = ₦1400. 3GB ₦1500
5GB = ₦1750. 4GB ₦2000
*VALIDITY: 30DAYS/1MONTH*
For cable subscription or sell recharge card
Call this number or whatsapp
👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽
*🪀08066268951*
Page 12
Fadila ta tashi aiki zata tafi gida , MD ya tare ta ya ce " Fadila , Kamar yadda kika ji na ce miki kodai ki rik'a zuwa da Ahmad aiki ko kuma ki dakata da zuwa aiki har ya yi k'wari "
Fadila juyawa ta yi ta fita ba tare da ta tanka ma MD ba .
Fadila koda ta koma gida bata b'oye ma mahaifiyarta yadda su ka yi da MD ba . Mahaifiyar Fadila shiru ta yi Sannan ta ce " Fadila , kodai MD shi ne mahaifin Ahmad ?" Tom , mama ni ma ban sani ba , amma ni ma ina zargin hakan " Cewar Fadila .
Aisha da ke zaune kusa da su ta ce " Nifa mama da za ku bi ta tawa Wallahi d'aukar yaran nan za'ai akai mai abinsa , dan babu ma makawa d'ansa ne Wallahi " A'a Aisha har yanzu ba mu da wata k'wak'k'warar hujjar da za mu yi haka , amma idan mu ka yi hak'uri Allah zai kawo mana hujjar da za mu kamashi da ita "
Da daddare Fadila tana hau Facebook, anan ta ci karo da posting d'in Usman abokin Muhammad yana cewa " Assalamu alaikum. Jama'a dan Allah ku taya mu addu'a Allah ya kawo ma abokin Muhammad Sagir mai shadda mafita akan halin rayuwar da ya tsinci kansa . Muhammad Sagir auranshi uku kenan , amma daga ankai matan gidansa washegari zai farka aga anyi musu yankar rago , gashi duk wani bincike da kuka sani babu wanda ba mu yi ba , amma har yanzu dai Allah bai bayyana mana wanda suke haka ba . Dan Allah kusa Muhammad Sagir a addu'a Allah ya toni asirin duk mai akatamai haka, idan kuma iskace Allah ya yi mai maganinta "
Fadila haka taita bin comments din jama'a , inda mutane da dama sukan ce " K'ilama al'jana ce ta aurai take ta mai ta'asan nan " Haka dai jama'a kowa da abin da yake cewa .
Fadila shiru ta yi , dan tabbas idan bata manta sunan wanda aka ce ya yi mata aiki ya ciro mata Ahmad ba shi ne , dan tabbas haka ya gabatar da sunan shi ga jama'a ranar taron bikin cikar shekara goma da RAHAMA TV ya yi . " Muhammad Sagir mai Shadda tabbas haka sunan ya ke"
Fadila dan ta cire ma kanta kokwanto Jamilu ta kira , bayan sun gaisa ta ce " Jamilu , dan Allah ko zaka iya tuna min sunan wanda ya yi min theater ya ciro min Ahmad ? " Eh , sunansa Muhammad Sagir mai shadda " Fadila shiru ta yi sanan ta ce " Shi kenan, na gode sai anjima "
Fadila bayan ta kashe wayarta number Muhammad ta kira acewarta ya cancanci ta yi mai gaisuwa . Abun mamaki kira d'aya Muhammad ya d'aga .