Sashe 18
Fadeelah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Fadila a d'akinsu ta iske mahaifiyarta da Aisha da sauran k'annanta suna zaune jigun - jigun kamar masu zaman makoki.
Mahaifiyar Fadila da sauran k'annanta da dukkansu da kallo suka bi Fadila. Fadila ko koda taga bata ga Ahmad a gidan ba tunaninta ya bata tabbas MD ya gudu da Ahmad, hakan ya sa Fadila ta d'ad'e da kuka .
Aisha da sauri ta nufi inda Fadila take tana tambayarta lafiya , inda mahaifiyarsu ta bi ta da ido .
Aisha cikin sanyi jin Fadila bata tanka mata ba kuma ta ci gaba da kuka ta kuma cewa " Aunty Fadila , lafiya ? Ina yaron fa ? " Sai sannan Fadila ta bud'e baki ta ce cikin kuka " MD ya gudu da shi " Aisha a zuciyarta ta ce " Alhamdulillah " Amma a fili sai cewa ta yi " Lafiya ya gudu da shi ? " Nima ban sani ba " Fadila ta bata amsa.
Suna a haka ne Kira ya shigo wayar Fadila , koda ta duba ta ga number MD da sauri ta d'aga kiran .
MD sanar da Fadila ya yi yana k'ofar gidansu .
Fadila fita ta yi da sauri. MD na ganinta ya fito cikin motar rungume da Ahmad a hannun shi ya mik'a ma Fadila shi . Fadila amsar Ahmad ta yi tana sauke sanyayyar ajiyar zuciya , Sannan ta kalli MD ta ce " Me ka sa min a yoghurt d'in da ka kawo min ? " Fadila ta fad'i maganar tana kure MD da ido .
MD cikin mamaki ya ce " Me na sa miki kuma ? Ni dai na kawo miki yoghurt ina jiran ki sha mu tafi in kawo ki gidanku amma abun mamaki kina sha ko da ma barci kike ji ne ban sani ba ,daga kina zuwa kika je kika kwanta kika kama barci , nima ganin haka sai ban tasheki ba na d'auki Ahmad muka fita " Fadila shiru ta yi sannan kamar za ta yi kuka ta ce " MD , dan Allah ka ji tausayina ka sanar da ni abun da ban sani ba , dan Allah ka cireni a kokonto ka sanar dani ? " Wata magana kike yi ne haka Fadila ? , Me ye biki sani ba ? Me ye ya shige miki duhu wanda biki sani ba kike son sani ? , Yi min bayani yadda zan gane ? " Cewar MD ya k'ure Fadila da ido.
Fadila cikin sanyi ta ce " MD me kasa min a cikin yoghurt d'in da ka ban ? " Oh ! Ya Allah , Fadila me zansa miki ? Wata magana ce kike yi haka ? " Fadila kallan MD ta yi da raunannun idanunta ta ce " Baka samin komai ba kace ? , Tom na ji baka samin komai ba , amma ka sani kafin ganina da jina ya d'auke naji lokacin da ka rungume ni , sannan na farka na ji jikina ba yadda nake ba " Fadila ta idasa maganar cikin kuka ta ce " Ta ya hakan ta faru ? " Shiru MD ya yi , sannan cikin sanyi ya ce " Fadila , atakaice dai idan na fahimceki kina zargina na yi miki wani abun ne . Haba Fadila ki tuna fa ko gidan nan bana zuwa in ba yauba da shima ke kika bukaci in zo in kawo ki gidanku na zo shi ne daga k'arshe abun da zaki sakamin dashi kenan , sannan Fadila ki tuna fa ko kafin Baba Lami ta tafi idan na zo ko dakinki bana shiga hasalima bana dadewa nake tafiya . Amma ki yi hak'uri sai yanzu na gano dalilin da ya sa kike zargina, yoghurt din da na baki kika sha a daidai lokacin kina jin barci kika sha, kika yi barci acikin barcin kika yi mafarkin an rungumeki kina ganin duhu - duhu kamar yadda kika ce , amma kuma yanzu kika dawo da mafarkinki gaba d'aya akaina " Fadila kallan MD ta yi yadda ya ke ta kawo mata hujjojin kare kai ta ce " Shi kenan , na yadda duhun da na gani da rungumata da aka yi duk a mafarki ne , tom amma da na tashi na ji jikina babu dadi bacin lafiya lau nake jin jikina kafin in sha yoghurt din da ka ban shi kuma fa? " Fadila kenan , to so nawa mutum zai kwanta barci ya tashi da zazzab'i ko ciwan kai ? "
Fadila da taga duk inda ta bulloma MD yana k'ok'arin kare kan shi hakan ya sa ta ce " Shi kenan MD Allah ya na tare da mai gaskiya idan har ka zalinceni na barka da Allah " Fadila na fadin haka ta shige gida da sauri ta bar MD nan tsaye.
MD na kiranta amma bata saurare shi ba. Yara ya samu ya basu kayan Fadila da na Ahmad da ya kwaso musu ya ce a shigar mata da su cikin gidan , sai kayan abinci Taliya , makaroni , cous -cous sai buhun shinkafa . Siyayya ce sosai ya yi musu .
Mahaifiyar Fadila ita kanta da mamaki take bin kayan da kallo , sai da aka gama shigo da su tas sannan ta kalli Fadila ta ce " Kin je kin sake saida mutunci naki ne ? Baku da abinci shi ne aka kawo mana ? Tom ki tattara da ke da duk kayan nan ki koma inda kika fito ! "
Mahaifiyar Fadila ta fara cilli da kayan da aka kawo ma Fadilar tana ta fitar mata gida ba zata zauna da karuwa ba , kuma ba zata ci abincin da aka samai ta hanyar sab'on Allah ba .
Mahaifiyar Fadila bayan ta gama cilli da duk kayan da zata iya d'agawa ta koma tura Fadila dake rungume da Ahmad cikin hijab tana cewa " Fita ! ba zan zauna da karuwa ba "
Aisha ganin mahaifiyarsu na niyyar tara musu jama'a rik'eta ta yi tana kuka ta ce " Mama, dan Allah ki bar furta mata kalmar karuwa , Aunty Fadila ta sanar da ni ainihin abun da ke faruwa da ita . Mama , naje wajan Aunty Fadila , kuma ta yi min rantsuwa da al'qur'ani mai girma akan bata tab'a kusantar abun da muke zarginta da aikatawa ba , mama , ke kika haifemu na tabbata ke kanki har yanzu zuciyarki ta kasa amince miki da abun da idanunki ke ganin hak'ik'anin gaskiyarshi , Mama , kinsan Aunty Fadila ba za tab'a rantse min da al'qur'ani ba akan k'arya dan kawai a yadda da ita , sannan ke da kanki kina shaidar fad'in gaskiyarta komai d'acinta . Me ya sa yanzu ba zaki yi mata uziri ba ki zauna ki tattauna da ita kamar yadda kika saba yi abaya , haba Mama, ke Uwace fa me ya sa ba zaki rungumi 'yarki ba zaki watsi da ita taje ta idasa lallacewa kenan ? Haba Mama kar yi abun da zaki zo kina danasani "
Allah Sarki mahaifiyarsu Fadila sakin Fadila ta yi tana kuka .Aisha kuma zuwa ta yi duk ta gyara kayan da mahaifiyarta ta yi watsi da su.
Mahaifiyar Fadila kuma take jikinta ya yi sanyi ta kuma tuna wacece 'yartata abaya , tabbas ta yadda da maganar Aisha cikin Fadila k'addararsu ce inda ida kanta duk da yaron da take gani zuciyarta ta k'i aminta mata da Fadila zata aikata zina .
Fadila da ta kasa jure kukan mahaifiyar tata zuwa ta yi ta tsugunna kusa da ita ta ce " Mama , dan Allah ki bar kukan nan ina tsoran fushin Allah ya sauka akaina , dan ni ce silar kukan naki " Mahaifiyar Fadila kai ta d'aga da jajayan idanunta tana kallan Fadila ta ce " Fadila, abu d'aya nake so ki sanar da ni yanzu waye mahaifin yaron nan ? " Mama , Wallahi tallahi ! Ban sani ba nima , dan Allah ki yafe min ki bar fushi dani ko zan samu sununin zuciya " Cewar Fadila tana kuka.
Mahaifiyar Fadila tashi ta yi tana tada Fadila ta ce " Na yafe miki Fadila , ni kuma Allah ya sa mun dangana "
ADAMAWA STATE
Muhammad da kan shi ya tuk'a kan shi har zuwa sabon gidan shi . Bai shiga ba sai da ya yi addu'o'i sannan .
Ango d'an kwalisa kad'an ya rage da ka zo kaga wayam , dan da amarya za mu tafi . Muhammad murmushin yak'e ya yi ya ce " Haba , kun isa ma "
Nan dai suka yi ta tsokanar Muhammad sannan su ka yi musu fatan alkairi suka tafi .
Muhammad bacin abokanshi sun tafi kallan Kadija ya yi wanda har ga zuciyarshi yake jin bata yi mai ba , amma dai ya yi alk'awarin zama da ita saboda mahaifinsa .
Muhammad ledar da ya shigo da ita ya mik'a ma Kadija ya ce " Bismillah " Na yi fushi gaskiya , tun dazu baka zo baka barni da abokanka suka ci kani da surutu " Muhammad bai k'ara jin baya son Kadija ba sai da ta yi magana ya ji baki d'aya ma ba ta yi mai ba , dan shi yana d'aya daga cikin abuwan da yake son mace dasu , yana son mace mai murya , amma wannan baki d'ayanta ba ta yi mai ba , ga shi da alama ma tana da surutu .
Kadija ko jin Muhammad ya yi shiru ta ce " Baka ji abin da nace ba ne ? Ba zan ci ba na yi fushi idan kana so in ci to ka kallasheni "
Muhammad kallan Kadija ya yi ya ce " Saina lallasheki zaki ci ? " Wayyo Kadija muryar Muhammad ta tafi da ita , kasa bud'e baki ta yi ta yi magana sai d'aga ma Muhammad kai ta yi .
Muhammad kallanta ya yi ya ce " Ki yi hak'uri ki ci kin ji amarya kwana da yunwa babu dadi " Muhammad na fad'in haka ya yi shigewarsa ciki ya barta anan zaune .
Mahaifiyar Fadila da sauran k'annanta da dukkansu da kallo suka bi Fadila. Fadila ko koda taga bata ga Ahmad a gidan ba tunaninta ya bata tabbas MD ya gudu da Ahmad, hakan ya sa Fadila ta d'ad'e da kuka .
Aisha da sauri ta nufi inda Fadila take tana tambayarta lafiya , inda mahaifiyarsu ta bi ta da ido .
Aisha cikin sanyi jin Fadila bata tanka mata ba kuma ta ci gaba da kuka ta kuma cewa " Aunty Fadila , lafiya ? Ina yaron fa ? " Sai sannan Fadila ta bud'e baki ta ce cikin kuka " MD ya gudu da shi " Aisha a zuciyarta ta ce " Alhamdulillah " Amma a fili sai cewa ta yi " Lafiya ya gudu da shi ? " Nima ban sani ba " Fadila ta bata amsa.
Suna a haka ne Kira ya shigo wayar Fadila , koda ta duba ta ga number MD da sauri ta d'aga kiran .
MD sanar da Fadila ya yi yana k'ofar gidansu .
Fadila fita ta yi da sauri. MD na ganinta ya fito cikin motar rungume da Ahmad a hannun shi ya mik'a ma Fadila shi . Fadila amsar Ahmad ta yi tana sauke sanyayyar ajiyar zuciya , Sannan ta kalli MD ta ce " Me ka sa min a yoghurt d'in da ka kawo min ? " Fadila ta fad'i maganar tana kure MD da ido .
MD cikin mamaki ya ce " Me na sa miki kuma ? Ni dai na kawo miki yoghurt ina jiran ki sha mu tafi in kawo ki gidanku amma abun mamaki kina sha ko da ma barci kike ji ne ban sani ba ,daga kina zuwa kika je kika kwanta kika kama barci , nima ganin haka sai ban tasheki ba na d'auki Ahmad muka fita " Fadila shiru ta yi sannan kamar za ta yi kuka ta ce " MD , dan Allah ka ji tausayina ka sanar da ni abun da ban sani ba , dan Allah ka cireni a kokonto ka sanar dani ? " Wata magana kike yi ne haka Fadila ? , Me ye biki sani ba ? Me ye ya shige miki duhu wanda biki sani ba kike son sani ? , Yi min bayani yadda zan gane ? " Cewar MD ya k'ure Fadila da ido.
Fadila cikin sanyi ta ce " MD me kasa min a cikin yoghurt d'in da ka ban ? " Oh ! Ya Allah , Fadila me zansa miki ? Wata magana ce kike yi haka ? " Fadila kallan MD ta yi da raunannun idanunta ta ce " Baka samin komai ba kace ? , Tom na ji baka samin komai ba , amma ka sani kafin ganina da jina ya d'auke naji lokacin da ka rungume ni , sannan na farka na ji jikina ba yadda nake ba " Fadila ta idasa maganar cikin kuka ta ce " Ta ya hakan ta faru ? " Shiru MD ya yi , sannan cikin sanyi ya ce " Fadila , atakaice dai idan na fahimceki kina zargina na yi miki wani abun ne . Haba Fadila ki tuna fa ko gidan nan bana zuwa in ba yauba da shima ke kika bukaci in zo in kawo ki gidanku na zo shi ne daga k'arshe abun da zaki sakamin dashi kenan , sannan Fadila ki tuna fa ko kafin Baba Lami ta tafi idan na zo ko dakinki bana shiga hasalima bana dadewa nake tafiya . Amma ki yi hak'uri sai yanzu na gano dalilin da ya sa kike zargina, yoghurt din da na baki kika sha a daidai lokacin kina jin barci kika sha, kika yi barci acikin barcin kika yi mafarkin an rungumeki kina ganin duhu - duhu kamar yadda kika ce , amma kuma yanzu kika dawo da mafarkinki gaba d'aya akaina " Fadila kallan MD ta yi yadda ya ke ta kawo mata hujjojin kare kai ta ce " Shi kenan , na yadda duhun da na gani da rungumata da aka yi duk a mafarki ne , tom amma da na tashi na ji jikina babu dadi bacin lafiya lau nake jin jikina kafin in sha yoghurt din da ka ban shi kuma fa? " Fadila kenan , to so nawa mutum zai kwanta barci ya tashi da zazzab'i ko ciwan kai ? "
Fadila da taga duk inda ta bulloma MD yana k'ok'arin kare kan shi hakan ya sa ta ce " Shi kenan MD Allah ya na tare da mai gaskiya idan har ka zalinceni na barka da Allah " Fadila na fadin haka ta shige gida da sauri ta bar MD nan tsaye.
MD na kiranta amma bata saurare shi ba. Yara ya samu ya basu kayan Fadila da na Ahmad da ya kwaso musu ya ce a shigar mata da su cikin gidan , sai kayan abinci Taliya , makaroni , cous -cous sai buhun shinkafa . Siyayya ce sosai ya yi musu .
Mahaifiyar Fadila ita kanta da mamaki take bin kayan da kallo , sai da aka gama shigo da su tas sannan ta kalli Fadila ta ce " Kin je kin sake saida mutunci naki ne ? Baku da abinci shi ne aka kawo mana ? Tom ki tattara da ke da duk kayan nan ki koma inda kika fito ! "
Mahaifiyar Fadila ta fara cilli da kayan da aka kawo ma Fadilar tana ta fitar mata gida ba zata zauna da karuwa ba , kuma ba zata ci abincin da aka samai ta hanyar sab'on Allah ba .
Mahaifiyar Fadila bayan ta gama cilli da duk kayan da zata iya d'agawa ta koma tura Fadila dake rungume da Ahmad cikin hijab tana cewa " Fita ! ba zan zauna da karuwa ba "
Aisha ganin mahaifiyarsu na niyyar tara musu jama'a rik'eta ta yi tana kuka ta ce " Mama, dan Allah ki bar furta mata kalmar karuwa , Aunty Fadila ta sanar da ni ainihin abun da ke faruwa da ita . Mama , naje wajan Aunty Fadila , kuma ta yi min rantsuwa da al'qur'ani mai girma akan bata tab'a kusantar abun da muke zarginta da aikatawa ba , mama , ke kika haifemu na tabbata ke kanki har yanzu zuciyarki ta kasa amince miki da abun da idanunki ke ganin hak'ik'anin gaskiyarshi , Mama , kinsan Aunty Fadila ba za tab'a rantse min da al'qur'ani ba akan k'arya dan kawai a yadda da ita , sannan ke da kanki kina shaidar fad'in gaskiyarta komai d'acinta . Me ya sa yanzu ba zaki yi mata uziri ba ki zauna ki tattauna da ita kamar yadda kika saba yi abaya , haba Mama, ke Uwace fa me ya sa ba zaki rungumi 'yarki ba zaki watsi da ita taje ta idasa lallacewa kenan ? Haba Mama kar yi abun da zaki zo kina danasani "
Allah Sarki mahaifiyarsu Fadila sakin Fadila ta yi tana kuka .Aisha kuma zuwa ta yi duk ta gyara kayan da mahaifiyarta ta yi watsi da su.
Mahaifiyar Fadila kuma take jikinta ya yi sanyi ta kuma tuna wacece 'yartata abaya , tabbas ta yadda da maganar Aisha cikin Fadila k'addararsu ce inda ida kanta duk da yaron da take gani zuciyarta ta k'i aminta mata da Fadila zata aikata zina .
Fadila da ta kasa jure kukan mahaifiyar tata zuwa ta yi ta tsugunna kusa da ita ta ce " Mama , dan Allah ki bar kukan nan ina tsoran fushin Allah ya sauka akaina , dan ni ce silar kukan naki " Mahaifiyar Fadila kai ta d'aga da jajayan idanunta tana kallan Fadila ta ce " Fadila, abu d'aya nake so ki sanar da ni yanzu waye mahaifin yaron nan ? " Mama , Wallahi tallahi ! Ban sani ba nima , dan Allah ki yafe min ki bar fushi dani ko zan samu sununin zuciya " Cewar Fadila tana kuka.
Mahaifiyar Fadila tashi ta yi tana tada Fadila ta ce " Na yafe miki Fadila , ni kuma Allah ya sa mun dangana "
ADAMAWA STATE
Muhammad da kan shi ya tuk'a kan shi har zuwa sabon gidan shi . Bai shiga ba sai da ya yi addu'o'i sannan .
Ango d'an kwalisa kad'an ya rage da ka zo kaga wayam , dan da amarya za mu tafi . Muhammad murmushin yak'e ya yi ya ce " Haba , kun isa ma "
Nan dai suka yi ta tsokanar Muhammad sannan su ka yi musu fatan alkairi suka tafi .
Muhammad bacin abokanshi sun tafi kallan Kadija ya yi wanda har ga zuciyarshi yake jin bata yi mai ba , amma dai ya yi alk'awarin zama da ita saboda mahaifinsa .
Muhammad ledar da ya shigo da ita ya mik'a ma Kadija ya ce " Bismillah " Na yi fushi gaskiya , tun dazu baka zo baka barni da abokanka suka ci kani da surutu " Muhammad bai k'ara jin baya son Kadija ba sai da ta yi magana ya ji baki d'aya ma ba ta yi mai ba , dan shi yana d'aya daga cikin abuwan da yake son mace dasu , yana son mace mai murya , amma wannan baki d'ayanta ba ta yi mai ba , ga shi da alama ma tana da surutu .
Kadija ko jin Muhammad ya yi shiru ta ce " Baka ji abin da nace ba ne ? Ba zan ci ba na yi fushi idan kana so in ci to ka kallasheni "
Muhammad kallan Kadija ya yi ya ce " Saina lallasheki zaki ci ? " Wayyo Kadija muryar Muhammad ta tafi da ita , kasa bud'e baki ta yi ta yi magana sai d'aga ma Muhammad kai ta yi .
Muhammad kallanta ya yi ya ce " Ki yi hak'uri ki ci kin ji amarya kwana da yunwa babu dadi " Muhammad na fad'in haka ya yi shigewarsa ciki ya barta anan zaune .