Sashe 1
Fadeelah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
📚 FADEELAH 📚
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
_{Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=337435884671992&id=103920888023494&sfnsn=mo
💪🏻J.A.W 💪🏻
Daga
Fadila Sani Bakori
Marubuciyar 👇🏻
1) Oga Habib
2) Abdurrahim matukin jirgin ruwa ne
3) Meenalyn daddy
4) In da rai
5) Rayuwar Haidar
6) So ne sila
7) Daga Allah ko d'orawa kai And now Fadeelah
GARGAD'I: Ban laminta ayi min amfani ko a juyamin littafi ba tare da izinina ba, dan haka a kiyaye.
08063
830828
SANARWA" Masu tambayata akan gyaran jiki ,akwai hanyoyi daban-daban da zan kawo muku na gyaran jiki acikin wannan littafi mai suna Fadeela.
GODIYA: Ina godiya da Allah Ubangijin talikai da ya ba ni lafiyar rubuta wannan littafi.Yadda na fara lafiya Allah ka sa in gama lafiya cike da nasarori.
SADAUKARWA" Wannan shafin sadaukarwa ne ga jaruman marubuta masu aiki da jarumta wajan fadakarwa, ilimantarwa ,tare da nishad'antar da jama'a abisa harshen Hausa,wato Jarumai writers association 👍🏻
Littafin Fadeela na kud'i ne Auntyna, za ki same shi akan farashi mai sauki #300 kacal .
Page 1
Bismillahir rahmanir rahim.
KADUNA GARIN GWAMNA
Tafiya take yi ahankali da alama dai kamar agajiye take.Sanye take da jalbab Hijab brown har kasa sai madai-daiciyar hand bag da ta rataya a kafad'arta. Yanayin tafiyarta kawai zaka kalla kasan ma'abociyar hankali da tunani ce,dan duk da tafiyar da sauri take yinta,hakan be hana fitowar natsuwarta ba, akwai isassar natsuwa a tare da ita.Wani madai-daicin gida ta shiga wanda daga ganin gidan kasan mutanan cikinsa suna rayuwa a takura ne acikinsa,dan gidan k'arami ne kwarai, kuma gaba d'aya d'akuna biyu ne acikinsa,sai bayi da d'an k'aramin dak'in girkinsu (kitchen).
Da sallama ciki-ciki ta shiga gidan.
Wata dattijuwar matace ta fito daga kicin d'in , wadda ba zata haura shekaru arba'in ba, da gani girki take dan idonta sun cika da hayak'i ,jin sallamar Fadeelah ne ta fito.Kallan mai sallamar ta yi ta ce"Fadeela,yauma sai yanzu kika samu damar dawowa? " Wadda aka Kira da Fadeela cikin sanyi alamun dakyar ma take maganar ta ce"Yi hakuri Mama ,da fatan dai Baba bai dawo ba ?" Matar banza ta yi da Fadeelah ta koma kicin d'in ta ci ga da girkinta.
Fadila ko guri ta samu ta zauna tana mai yaye Hijab din jikinta,tana nan zaune wata yarinya daga gani dai k'anwarta ce ta zo ta ce"Aunty kin dawo?"Fadila kai ta d'aga ma yarinyar,yarinyar kuma ta ci gaba da cewa"Aunty ,Baba d'azu da ya dawo gida sai fad'a ya ke wai har yanzu biki dawo ba,kuma ya ce daga yau kin gama zuwa aiki"Fadeelah cikin furgici da jin abin da k'anwar tata ta ce ta d'ago manya-manyan idanunta tana kallan k'anwar tata da su ,tama kasa cewa komai,sannan dai zuwa can ta ce"Husna, an
b'ata ma Baba rai ne ? Inda ko da zan fita aiki mun gaisa da shi" Husna da yake irin yaran nan ne masu gulma da shaigen surutu, ta ce"Wallahi Aunty, ji na yi yana cewa wai daga y...."Bige bakin Husna da mahaifiyarsu ta yi ne ya sa ta yi shiru.
Fadeelah cikin damuwa ta kalli mahaifiyarta ta ce"Mama,abin da Husna ta ce da gaske ne ko?"Ban sani ba,idan Baban naku ya zo kin ji daga bakin shi,"
Fadila da a Duniya in dai kana so ka ga furgicinta tom ayi mata maganar dakatar da ita daga aikin da take yi a Rahama TV.
Ji tayi gaba daya ma yunwar da take ji ta koma,hakan ya sa ta shiga d'akinsu ta kwanta ,tana tunanin me za ta yi ko tace ma mahaifinta idan ya tunkareta da maganar,dan shekararta d'aya kenan da fara aikin amma kusan koda yaushe haka suke da mahaifinta,kusan kullum dai maganar kenan,har ta fara tunanin aje musu aikin su ta huta.
Fadila na nan kwance ta ji shigowar mahaifinta.Ya shigo ba jimawa aka kira sallar magriba,ana Kira ya tashi ya fita,hakan ya ba Fadeela damar fitowa tsakar gidan ta yi alwallah da sauri ta koma d'aki dan tana gudin had'uwarta da mahaifin nata.
Fadeelah bacin ta idar da sallar magriba ne ta aiki k'anwarta Husna ta zubo mata tuwo ta ci
Tana nan zaune tana jiran Kiran mahaifin nata amma shiru har barci ya kwasheta.
Washegari dama kullum k'arfe bakwai ( 7:00 AM) Fadeelah ke fita aiki, bayan ta idar da Sallah ta yi azakar kamar yadda ta saba duk safiya, ta yi wanka ta shirya ta d'akko Jakarta ta lallab'a tana tafiya,so take ta fita a hankali gudin kar mahaifinta ya ji motsinta,ta kama k'ofar gidan zata bude kenan sai jin muryar mahaifin nata ta yi yana cewa"Fadeelah, zo nan"gabanta na faduwa alamun tsorata da ganinta da mahaifin nata ya yi ta k'arasa inda yake.
Tana zuwa ta zuk'unna kanta k'asa,cikin rawar baki ta ce"Ina kwana Baba"Maimakon ya amsa gaisuwarta sai cewa ya yi"Ina za ki kike sand'o haka?"Cikin rawar baki Fadeelah ta ce"Aiki"Lafiya kike sand'o?" To nan fa ba amsa,shiru ne ya biyo baya.
Mahaifin Fadila cikin d'aga murya alamun ya fusata ya ce"Na ce lafiya kike sand'o? Hakan ya tabbatar min da kin ji sak'ona kenan ?"Fadila dai kanta kasa ta kasa cewa komai.Mahaifin Fadila ko ya ci gaba da cewa"Fadila,daga yau na hanaki wannan aiki dan bashi da amfanin komai gareki illah zagi da kike jawo min wajan jama'a, sannan zan baki zabi guda biyu zaki iya daukar duk wanda ya yi miki ko dai ki kawo min wanda kike so ko kuma ni in zab'a miki ,dan in Allah ya yarda ba zaki k'ara min wata uku agida ba,dan naga abin naki bana k'are ba ne!"Mahaifin Fadila na gama fadin abin da yake fada ya bar Fadila nan zuk'unne ya shige dak'in shi.
Fadila dakyar ta samu ta lallab'a ta tashi ,sannan ta Kira abokin aikinta. Bacin sun gaisa ne ta ce"Jamilu,Baba fa ya yi yadda ya saba,yau ma ya hanani zuwa aiki,ko kuma in ce maka ma yau ya fi na koyaushe, dan bana jin zai kuma barina k'ara zuwa aiki ,ina ganin Jamilu zan hak'ura in aje aiki kawai "
Wanda Fadila ta Kira da Jamila ya ce"A'a,Fadila kar ki yi haka, ni shawarar da zan baki ki yi auran mana, idan kina son aikin Wanda za ki aura in ya amince sai ki ci gaba da aikinki"Jamilu,kasan dai bana maka boye-boye ko? ko kuma ince kasan komai dan gane dani,wa zan aura in kace haka?" Daga can b'angaran Jamilu ya ce"Ina, M'd fa?, Allah Fadila da gaske yake son ki,ko aiki kina ganin sai ki kwana nawa biki zo ba amma ba zai ce miki komai ba,hakan kad'ai ya isa ya sa ki yarda yana sonki so na aur.."Fadila dakatar da Jamilu ta yi ta hanyar cewa"Dan Allah mu yi magana mai amfani kabar wannan maganar ina zan kai tunbin mutumin nan Allah bana son shi"Dariya Jamilu ya yi ya ce"Tom ,shi kenan zan tayaki addu'a, zan zo gidan in na tashi aiki in yi magana da Mama"
Sallama su ka yi ta kashe wayarta ta tashi ta koma d'akin su.Cire hijb din dake jikinta ta yi ta share dan madaidaicin gidan nasu,ta yi wanke-wanke, bacin ta gama ne ta samu mahaifiyarta ad'akin mahaifinta shi kuma lokacin ya fita.
Bacin sun gaisa ne Fadila ta kalli mahaifiyar tasu ta ce"Mama,dama nace inda yanzu Baba kasuwar sai a hankaki ,dan Allah kisa baki ya barni na ci gaba da aikina, albashin zai taimakamana"Mahaifiyar Fadila ta dade tana kallan Fadila bata tanka mata ba ,sannan zuwa can cikin sanyi ta ce"Fadila,mahaifinki fa shi ya biya miki kud'in da kika yi karatu har kika kai haka,kuma da amincewar shi da taimakonshi kika fara aikin nan,sai dai Fadila, tunda kika fara aikin nan k'ananun maganganu suka yi yawa akanki wa mutane,kowa da abin da yake cewa ,tom mahaifinki ya kasa jure maganar mutane dan acewarshi duk abin da aka ciki yawan magana akan shi baya albarka, saboda wasu bakinsu ba mai kyau bane, ni da mahaifinki munsan wacece ke ,tom amma futane sun sa ma aikin nan naki ido ana ganin kamar mun dogara da aikinne kina yawace-yawacanki kina cida mu in da yanzu kowa yasan mahaifinki ba kamar da ba ,dan haka ni yanzu shawarar da zan baki ki yi hakuri da aikin nan idan akwai wanda kuka yi wata magana ki fito da shi ki yi auranki, alabashi idan mijinki ya amince sai ki ci gaba da aikinki a d'akinki"Shiru Fadila ta yi,sannan zuwa can bacin ta ja doguwar ajiyar zuciya ta ce"Tom, Mama na ji na yarda, amma abin da nake so ki fahimta koda da fa na aje aiki a yanzu bani da wanda mu ka yi maganar aure"
Atakaice dai Fadila babu yadda ba ta yi ba ganin ta shawo kan mahaifiyarta akan mahaifinta ya janye kudirinsa akanta ,amma taki fahimta,dole ta hakura ta tashi.
Abu kamar wasa yau satin Fadila biyu kenan da daina zuwa aiki har ma ta hakura.
ADAMAWA STATE
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
_{Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=337435884671992&id=103920888023494&sfnsn=mo
💪🏻J.A.W 💪🏻
Daga
Fadila Sani Bakori
Marubuciyar 👇🏻
1) Oga Habib
2) Abdurrahim matukin jirgin ruwa ne
3) Meenalyn daddy
4) In da rai
5) Rayuwar Haidar
6) So ne sila
7) Daga Allah ko d'orawa kai And now Fadeelah
GARGAD'I: Ban laminta ayi min amfani ko a juyamin littafi ba tare da izinina ba, dan haka a kiyaye.
08063
830828
SANARWA" Masu tambayata akan gyaran jiki ,akwai hanyoyi daban-daban da zan kawo muku na gyaran jiki acikin wannan littafi mai suna Fadeela.
GODIYA: Ina godiya da Allah Ubangijin talikai da ya ba ni lafiyar rubuta wannan littafi.Yadda na fara lafiya Allah ka sa in gama lafiya cike da nasarori.
SADAUKARWA" Wannan shafin sadaukarwa ne ga jaruman marubuta masu aiki da jarumta wajan fadakarwa, ilimantarwa ,tare da nishad'antar da jama'a abisa harshen Hausa,wato Jarumai writers association 👍🏻
Littafin Fadeela na kud'i ne Auntyna, za ki same shi akan farashi mai sauki #300 kacal .
Page 1
Bismillahir rahmanir rahim.
KADUNA GARIN GWAMNA
Tafiya take yi ahankali da alama dai kamar agajiye take.Sanye take da jalbab Hijab brown har kasa sai madai-daiciyar hand bag da ta rataya a kafad'arta. Yanayin tafiyarta kawai zaka kalla kasan ma'abociyar hankali da tunani ce,dan duk da tafiyar da sauri take yinta,hakan be hana fitowar natsuwarta ba, akwai isassar natsuwa a tare da ita.Wani madai-daicin gida ta shiga wanda daga ganin gidan kasan mutanan cikinsa suna rayuwa a takura ne acikinsa,dan gidan k'arami ne kwarai, kuma gaba d'aya d'akuna biyu ne acikinsa,sai bayi da d'an k'aramin dak'in girkinsu (kitchen).
Da sallama ciki-ciki ta shiga gidan.
Wata dattijuwar matace ta fito daga kicin d'in , wadda ba zata haura shekaru arba'in ba, da gani girki take dan idonta sun cika da hayak'i ,jin sallamar Fadeelah ne ta fito.Kallan mai sallamar ta yi ta ce"Fadeela,yauma sai yanzu kika samu damar dawowa? " Wadda aka Kira da Fadeela cikin sanyi alamun dakyar ma take maganar ta ce"Yi hakuri Mama ,da fatan dai Baba bai dawo ba ?" Matar banza ta yi da Fadeelah ta koma kicin d'in ta ci ga da girkinta.
Fadila ko guri ta samu ta zauna tana mai yaye Hijab din jikinta,tana nan zaune wata yarinya daga gani dai k'anwarta ce ta zo ta ce"Aunty kin dawo?"Fadila kai ta d'aga ma yarinyar,yarinyar kuma ta ci gaba da cewa"Aunty ,Baba d'azu da ya dawo gida sai fad'a ya ke wai har yanzu biki dawo ba,kuma ya ce daga yau kin gama zuwa aiki"Fadeelah cikin furgici da jin abin da k'anwar tata ta ce ta d'ago manya-manyan idanunta tana kallan k'anwar tata da su ,tama kasa cewa komai,sannan dai zuwa can ta ce"Husna, an
b'ata ma Baba rai ne ? Inda ko da zan fita aiki mun gaisa da shi" Husna da yake irin yaran nan ne masu gulma da shaigen surutu, ta ce"Wallahi Aunty, ji na yi yana cewa wai daga y...."Bige bakin Husna da mahaifiyarsu ta yi ne ya sa ta yi shiru.
Fadeelah cikin damuwa ta kalli mahaifiyarta ta ce"Mama,abin da Husna ta ce da gaske ne ko?"Ban sani ba,idan Baban naku ya zo kin ji daga bakin shi,"
Fadila da a Duniya in dai kana so ka ga furgicinta tom ayi mata maganar dakatar da ita daga aikin da take yi a Rahama TV.
Ji tayi gaba daya ma yunwar da take ji ta koma,hakan ya sa ta shiga d'akinsu ta kwanta ,tana tunanin me za ta yi ko tace ma mahaifinta idan ya tunkareta da maganar,dan shekararta d'aya kenan da fara aikin amma kusan koda yaushe haka suke da mahaifinta,kusan kullum dai maganar kenan,har ta fara tunanin aje musu aikin su ta huta.
Fadila na nan kwance ta ji shigowar mahaifinta.Ya shigo ba jimawa aka kira sallar magriba,ana Kira ya tashi ya fita,hakan ya ba Fadeela damar fitowa tsakar gidan ta yi alwallah da sauri ta koma d'aki dan tana gudin had'uwarta da mahaifin nata.
Fadeelah bacin ta idar da sallar magriba ne ta aiki k'anwarta Husna ta zubo mata tuwo ta ci
Tana nan zaune tana jiran Kiran mahaifin nata amma shiru har barci ya kwasheta.
Washegari dama kullum k'arfe bakwai ( 7:00 AM) Fadeelah ke fita aiki, bayan ta idar da Sallah ta yi azakar kamar yadda ta saba duk safiya, ta yi wanka ta shirya ta d'akko Jakarta ta lallab'a tana tafiya,so take ta fita a hankali gudin kar mahaifinta ya ji motsinta,ta kama k'ofar gidan zata bude kenan sai jin muryar mahaifin nata ta yi yana cewa"Fadeelah, zo nan"gabanta na faduwa alamun tsorata da ganinta da mahaifin nata ya yi ta k'arasa inda yake.
Tana zuwa ta zuk'unna kanta k'asa,cikin rawar baki ta ce"Ina kwana Baba"Maimakon ya amsa gaisuwarta sai cewa ya yi"Ina za ki kike sand'o haka?"Cikin rawar baki Fadeelah ta ce"Aiki"Lafiya kike sand'o?" To nan fa ba amsa,shiru ne ya biyo baya.
Mahaifin Fadila cikin d'aga murya alamun ya fusata ya ce"Na ce lafiya kike sand'o? Hakan ya tabbatar min da kin ji sak'ona kenan ?"Fadila dai kanta kasa ta kasa cewa komai.Mahaifin Fadila ko ya ci gaba da cewa"Fadila,daga yau na hanaki wannan aiki dan bashi da amfanin komai gareki illah zagi da kike jawo min wajan jama'a, sannan zan baki zabi guda biyu zaki iya daukar duk wanda ya yi miki ko dai ki kawo min wanda kike so ko kuma ni in zab'a miki ,dan in Allah ya yarda ba zaki k'ara min wata uku agida ba,dan naga abin naki bana k'are ba ne!"Mahaifin Fadila na gama fadin abin da yake fada ya bar Fadila nan zuk'unne ya shige dak'in shi.
Fadila dakyar ta samu ta lallab'a ta tashi ,sannan ta Kira abokin aikinta. Bacin sun gaisa ne ta ce"Jamilu,Baba fa ya yi yadda ya saba,yau ma ya hanani zuwa aiki,ko kuma in ce maka ma yau ya fi na koyaushe, dan bana jin zai kuma barina k'ara zuwa aiki ,ina ganin Jamilu zan hak'ura in aje aiki kawai "
Wanda Fadila ta Kira da Jamila ya ce"A'a,Fadila kar ki yi haka, ni shawarar da zan baki ki yi auran mana, idan kina son aikin Wanda za ki aura in ya amince sai ki ci gaba da aikinki"Jamilu,kasan dai bana maka boye-boye ko? ko kuma ince kasan komai dan gane dani,wa zan aura in kace haka?" Daga can b'angaran Jamilu ya ce"Ina, M'd fa?, Allah Fadila da gaske yake son ki,ko aiki kina ganin sai ki kwana nawa biki zo ba amma ba zai ce miki komai ba,hakan kad'ai ya isa ya sa ki yarda yana sonki so na aur.."Fadila dakatar da Jamilu ta yi ta hanyar cewa"Dan Allah mu yi magana mai amfani kabar wannan maganar ina zan kai tunbin mutumin nan Allah bana son shi"Dariya Jamilu ya yi ya ce"Tom ,shi kenan zan tayaki addu'a, zan zo gidan in na tashi aiki in yi magana da Mama"
Sallama su ka yi ta kashe wayarta ta tashi ta koma d'akin su.Cire hijb din dake jikinta ta yi ta share dan madaidaicin gidan nasu,ta yi wanke-wanke, bacin ta gama ne ta samu mahaifiyarta ad'akin mahaifinta shi kuma lokacin ya fita.
Bacin sun gaisa ne Fadila ta kalli mahaifiyar tasu ta ce"Mama,dama nace inda yanzu Baba kasuwar sai a hankaki ,dan Allah kisa baki ya barni na ci gaba da aikina, albashin zai taimakamana"Mahaifiyar Fadila ta dade tana kallan Fadila bata tanka mata ba ,sannan zuwa can cikin sanyi ta ce"Fadila,mahaifinki fa shi ya biya miki kud'in da kika yi karatu har kika kai haka,kuma da amincewar shi da taimakonshi kika fara aikin nan,sai dai Fadila, tunda kika fara aikin nan k'ananun maganganu suka yi yawa akanki wa mutane,kowa da abin da yake cewa ,tom mahaifinki ya kasa jure maganar mutane dan acewarshi duk abin da aka ciki yawan magana akan shi baya albarka, saboda wasu bakinsu ba mai kyau bane, ni da mahaifinki munsan wacece ke ,tom amma futane sun sa ma aikin nan naki ido ana ganin kamar mun dogara da aikinne kina yawace-yawacanki kina cida mu in da yanzu kowa yasan mahaifinki ba kamar da ba ,dan haka ni yanzu shawarar da zan baki ki yi hakuri da aikin nan idan akwai wanda kuka yi wata magana ki fito da shi ki yi auranki, alabashi idan mijinki ya amince sai ki ci gaba da aikinki a d'akinki"Shiru Fadila ta yi,sannan zuwa can bacin ta ja doguwar ajiyar zuciya ta ce"Tom, Mama na ji na yarda, amma abin da nake so ki fahimta koda da fa na aje aiki a yanzu bani da wanda mu ka yi maganar aure"
Atakaice dai Fadila babu yadda ba ta yi ba ganin ta shawo kan mahaifiyarta akan mahaifinta ya janye kudirinsa akanta ,amma taki fahimta,dole ta hakura ta tashi.
Abu kamar wasa yau satin Fadila biyu kenan da daina zuwa aiki har ma ta hakura.
ADAMAWA STATE