Sashe 9
Dan Sarkin Sauban Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A na hakan Sauban suka kammala jarabawarsu ta primary aka had'a masu biki na musamman,
Wanda harda sarki da Abdullah tare da Hajjah suka halarci bikin yayewarsu makarantar primary."
Hakan Jamila itama tazo domin tana da labarin cewa harda Sauran classic za'a Bawa d'alibai kyauta wad'anda sukayi na d'aya Dan tana da yak'i nin har da yaranta a ciki saboda tana kiran malaman a bayan fage tana basu kud'i Dan su rik'a Bawa yaranta na d'aya ako WANNE k'arshen zango kamar yanda taga Sauban Yana d'aukar na d'aya,
Domin ta fahimci Sageer da SADEEQ ba wani k'ok'ari ne dasuba musamman Sadeeq, Dan har k'ara Sageer Wani lokacin Sauban yakan zaunar dashi ya koya Masa karatu idan suna makaranta." Sab'anin Sadeeq da ba abinda yasani sai mungunta dason nuna mulki da Isa tin Yana k'aramunsa sak halin uwarsa👌🏻"
Biki akeyi kowa sai murna yakeyi musamman Maimartaba da Abdullah da sukaga Ankira Sauban ya bud'e taro da Addu'a cikin harshen larabci, cikin natsuwarsa da kamalarsa tare da k'asaitarsa Mai fitar da kwarjininsa na jinin sarauta,
Bayan ya gama Addu'ar bud'e taro cikin harshen larabci snn ya koma magana cikin harshen turanci irin turancin Nan Mai kyau irin na mutanan England, tamkar ba'a bakinsa harafin turanci yake fitowaba,
Dad'i tamkar ya kashe duk wani masoynki sauban dake wurin
,
Amma Banda Jamila da takeji Ina wuta ta jefashi Dan bak'in ciki sai fad'i take a ranta tsinanne Mai halin uwarsa kaima ka kusan zuwa Ina tsinanniyar uwarka tatafi"
Bayan ankammala komai aka Fara bada kyaututtuka, inda Sauban ya samu kyauta ta musamman. Domin duk wani Mai fad'a aji Wanda ya halarci taron sai da yabawa Sauban kyautar ban girma tare da burgewa."
A nan aka zo Sauran classic duk d'alibin da yayi na d'aya, a ka shiga Kiran sunansa d'aya bayan d'aya ana basu kyauta, Jamila sai murmushi takeyi tana gyara hannu tana jiran Akira yaranta taje da kanta ta k'arb'ar masu Dan Bata buk'atar wani yaje ya amso masu." _halinki ba kyau jamila_ 🤔
Sai da aka kammala Bawa ko wanne class taga ba'a Kira yarantaba haushi da takaici ya k'umeta,
Wayyo Allah kuxo kuga fuskar Jamila ganin ba'a Kira yarantaba bak'in ciki kamar ya kasheta ganin ko wanne yaro sai d'aga kyautarsa Yakeyi Yana Bawa mahaifiyarsa Amma Banda yaranta,
Lura da hakan da Sauban yayi yasa yasaki murmushi ya tako yazo wurin k'annensa ya janyo hannunsu zuwa jikinsa ya rungumesu Yana lallashinsu tare da cewa kuyi hakurin kunji k'annena,
Wani time d'in kuyi k'ok'ari, ku daina Wasa a karatu ,
Kuma za'a baku kamar hakan kunji."
Sadeeq ya fisge jikinsa daga jikin Sauban ya nufi wurin mahaifiyarsa Yana sharar hawaye,
Sunan Sauban akaji ana Kira cikin abar magana Wanda tasaka kowa natsuwa,
Cikin takunsa yanufi wurin da ake kiransa a gaban governor yaje ya tsugunna Wanda shine yasaka akirashi,
Governor yana murmushi Yana kallon Sauban ya d'auki wata kyauta Mai girman gaske Wacce aka lullub'eta a cikin wata Leda Mai haske da kyalli,ya mik'awa Sauban."
Hannu biyu Sauban yasaka ya amsa cike da girmamawa Yana godiya, ai Kuwa aka shiga yi masu hotona,
_wayyo mutuwa kozo kuga idon jamila_😂
Idon kowa Akan Sauban ya mik'e a gaban governor Yana tafiyarsa cikin natsuwa yana d'auke da kyautarsa a hannu kowa sai kallonsa yakeyi Kai tsaye wurin Jamila yanufa ya durk'usa gabanta ya mik'a Mata kyautar
don ta Sanya Masa Albarka,
Ido kansu kowa sai kallonsu yakeyi cike da burgewa
Wad'anda suka San komai sun zuba Ido domin ganin yanda zata karb'eshi,
Ganin Ido kanta snn ga Abdullah da sarki Suma kallonta sukeyi suna murmushi,
yasa tasaki dariya ta k'arb'i kyautar tana murmushin Yak'e Wanda yafi kuka ciwo ta dafa kansa tana fad'in, d'ana kayi k'ok'ari sosai Allah ya taimaka."
ai Kuwa aka shiga d'aukarsu hotona sai murmushin takeyi tana k'ara rungumo Sauban zuwa jikinta, a can cikin zuciyarta kuma jitakeyi kamar ta kurma ihu akan bak'in ciki,
Ganin idanu sun janye kansu Sauban ya koma wurin maimartaba ana hotona yasa tana ganin hakan tayi saurin mik'ewa tsaye tabar wurin tare da Jan yaranta suka shiga mota tanufi gida."
Murmushi manyan Hajjah tasaki domin Sauban ya matuk'ar burgeta da yayiwa Jamila hakan,
Don ko yanzun zata gane idan Rana tafito tafin hannu baya rufeta."
Ana hakan taro ya watse sarki ya dawo gida cike da farin ciki da annashawa, hakan Abdullah sai dai Jin zafinsa d'aya Banda Sadeeq da Sageer Wurin bada kyauta kamar yanda yaga ana Bawa Sauran d'aliban da sukazo na d'aya, yashiga tinanin
Kodai basa karatun ne?"
Hakan yasa suna sauka a mota ya nufi b'angaren Jamila,
Sageer da SADEEQ kwance a kan jikinta tana lallashinsu Sadeeq Yana fad'in Muguntace Sauban ya masu shine ya Hana a basu kyauta a makaranta Wanda Sageer yake cewa ba laifin Yaya Sauban bane laifin uncle ne,
Jamila ta dakawa sageer tsawa tare da zare masa Ido tana fad'in wnn yaron da a asibity na haifeka da nace anyi mun canjenka domin na lura gaba d'aya baka biyo halina ba,
Da zarar anfad'i laifin Sauban yi kakeyi kamar kafashe da kuka, ko ka dakemu,
To bara kaji ka bud'e kunnenka da kyau kaji Sauban ba masoyinku bane Dan ba d'ana bane banice na nahaifeshe ba, kaga ku biyun Nan ku kad'ai na haifa,
Sauban d'an ubane abokin gabarku ne, ko kashesa kukayi ba abinda zai faru, domin idan Baku kashesa ba kunaji Kuna gani zai hau kujerar sarauta,
ku Kuna gefe kuna kallo sai yanda yayi daku kun Zama 'yan kallon kenan."
Sallamar Abdullah yasa taja bakinta tayi shuru illah ta had'e fuska domin Bata ga alamar Wasa a tare dashi ba."
Wuri ya samu ya zauna cikin d'aure fuska tace "barka da shigowa,
"Yawwa yace snn kuyangi suka zagayeshi da kayan motsa baki."
Kallonsa Sadeeq da Sageer sukeyi domin ba'a koya masu gaisuwa ba, shima bai damuba domin yasan irin tasu tarbiyar kenan,
Wanda yayi fad'a har ya gaji ba wani sauyi a tare dasu,
Kallonsu yayi snn ya d'aga masu hannu alamar su zo wurinsa, cikin sauri Sageer ya riga Sadeeq zuwa suka zauna a gefensa."
Kallonsa Jamila tayi ta d'anyi murmushin tace yarona Sauban yayi k'ok'ari sosai."
Shima murmushi yayi ya Kuma had'e fuska ya kalli sadig da sagir yace "meyasa bakuzo na d'aya aka Baku kyauta ba Kuma makaranta kamar yanda aka Bawa kowa?"
Ashe dama ba karatu kukeyi ba?"
Baza kuyi koyi da yayanku Sauban ba?"
Sageer yace munaso Abba,
Sadeeq yace "Ni nafison nafishi ta ko Ina."
Murmushin Abdullah yasaki domin ya dad'e da fahimtar duk halin mahaifiyarsa sadeeq ya d'auko,
Yace "tayaya zakafishi bayan baka mayar da hankali a karatu ba,
Gargad'i na k'arshe da zan Kuma yimaku shine duk kuka kuskura hakan ta Kuma kasancewa sai na d'aukar maku mataki."
Jamila tayi karaf tace "tayaya?"
A'a nifa bana son hakan, duk abinda ya faru da akwai wata a k'asa,
Kai kutashi kushiga daga ciki Allah ya rayamunku domin Ni ka d'ai ke sonku a cikin gidan Nan."
Suka tashi cikin sauri suka nufi d'akinsu,
Ido kawai Abdullah ya zuba Mata baice da ita komai ba ya tashi ya fita Yana tir da Hali irin nata."
Fitarsa b'angaren Hajjah yanufa ya d'auki Sauban ya fita dashi yanufi Gidan gonar mahaifiyarsa, Wanda ya lura da Sauban Yana matuk'ar son zuwa wurin Yana Jin dad'in KASANCEWARsa a cikin gidan gonar Koda yaushe tamkar mahaifiyarsa bintu
Sai kusan k'arfe bakwai suka dawo gida,
BaYan ya Kai Sauban b'angaren Hajjah snn yawuce masallaci sukayi sallar magariba tare da maimartaba suna cikin masallacin akayi Isha'i kamar yanda suka Saba a kullum,
bayan sun kammala yin sallar ne suka fito a tare suna tafiya dogarai na biye dasu a baya
Sarki yake cewa "Abdullah ya kamata kayi aure ka maye gurbin Bintu Wacce ta mutu,
Murmushi kawai Abdullah yayi bai tankawa mahaifin nasaba,
Sarki yaci gaba da cewa idan ka shirya ko a gobe zan d'aura maka aure, sai dai wnn karon mata biyu zaka aura a lokaci d'aya domin inason lokacin da zan sauka a kan kujerar mulki idan za'a d'oraka akai ya zamana kana da Mata hud'u kamar yanda aka San ko wanne sarki,
idan ka cireni daga ciki koni akwai dalilina nayin Mata d'aya."
Murmushi Abdullah yasaki baiyi magana ba domin koshi Yana da buk'atar k'arin auren koba komai ya dinga samun kulawa ya Kuma dinga samun natsuwa idan buk'atarsa ta motsa domin Jamila yanzun Bata da lokacin komai sai mulki dasaka a gaba da hidimar yaranta."
Sarki yace Kai nake saurare meye ra'ayinka ko baka buk'ata ne?"
Girgiza Kai Abdullah yayi cike da girmamawa yace "duk abinda kace shine dai dai,
Bana da zab'i sai naka a kullum burina nayi maka biyayya na faranta maka nasaka ka farin ciki, ko yanzun ka shirya Nima a shirye nake za'a iya d'auramun auren da ko wacce macce kake so zan karb'eta hannu biyu."
Sarki yaji dad'in furucin Abdullah Wanda sai murmushi yakeyi Yana girgiza kai,
Ba Wanda ya sake yin magana a cikinsu har Abdullah ya Kai maimartaba d'akinsa kamar yanda yasaba idan suka dawo sallar, sai ya kaisa har d'akinsa snn yayi Masa sallama yafito yanufi d'akin Hajjah itama yayi Mata sallama snn yanufi nashi d'akin domin ya kwanta,
Wnn karon bayan ya Kai maimartaba d'akin nasa wuri yasamu a gefensa ya zauna tare da sunkuyar da Kai Yana jiran ya Sanya Masa Albarka kamar yanda yasaba snn yatashi yafita."
Sarki ya juyo ya dafa kansa kamar yanda yasaba yashiga "fad'in Abdullah Allah yayi maka Albarka Allah ya sanyawa rayuwarka hak''ika wnn biyayya da kakeyimun Allah yabaka d'anda zai lunka maka fiye da hakan , snn kazama cikin shiri gobe za'a d'aura maka aure da wasu tsala tsalan bayi wad'an da Aka 'yanta Naga sun dace da Kai Allah yabaku zuri'a Mai Albarka."
'Ameen Abdullah yace Yana murmushi Mai cike da jin dad'i."
Wayarsa tayi ringing yayi kamar bazai d'aukaba sarki yayi murmushi yace ka d'auki wayar Mana."
Cikin sauri ya Sanya hannu a Aljihu ya d'auko wayar,
Ganin sunan Abokinsa ne Wanda suka tashi a tare wato sarkin Bauchi Wanda mahaifinsa ya rasu aka d'orashi a kan kujerar mulkin,
Yana murmushin ya d'aga wayar tare da karawa a kunnensa da sallama a bakinsa, cike da tsokana Yake fad'in ranka ya dad'e sarki Allah ya k'ara maka lafiya ya kake?"
Wanda harda sarki da Abdullah tare da Hajjah suka halarci bikin yayewarsu makarantar primary."
Hakan Jamila itama tazo domin tana da labarin cewa harda Sauran classic za'a Bawa d'alibai kyauta wad'anda sukayi na d'aya Dan tana da yak'i nin har da yaranta a ciki saboda tana kiran malaman a bayan fage tana basu kud'i Dan su rik'a Bawa yaranta na d'aya ako WANNE k'arshen zango kamar yanda taga Sauban Yana d'aukar na d'aya,
Domin ta fahimci Sageer da SADEEQ ba wani k'ok'ari ne dasuba musamman Sadeeq, Dan har k'ara Sageer Wani lokacin Sauban yakan zaunar dashi ya koya Masa karatu idan suna makaranta." Sab'anin Sadeeq da ba abinda yasani sai mungunta dason nuna mulki da Isa tin Yana k'aramunsa sak halin uwarsa👌🏻"
Biki akeyi kowa sai murna yakeyi musamman Maimartaba da Abdullah da sukaga Ankira Sauban ya bud'e taro da Addu'a cikin harshen larabci, cikin natsuwarsa da kamalarsa tare da k'asaitarsa Mai fitar da kwarjininsa na jinin sarauta,
Bayan ya gama Addu'ar bud'e taro cikin harshen larabci snn ya koma magana cikin harshen turanci irin turancin Nan Mai kyau irin na mutanan England, tamkar ba'a bakinsa harafin turanci yake fitowaba,
Dad'i tamkar ya kashe duk wani masoynki sauban dake wurin
,
Amma Banda Jamila da takeji Ina wuta ta jefashi Dan bak'in ciki sai fad'i take a ranta tsinanne Mai halin uwarsa kaima ka kusan zuwa Ina tsinanniyar uwarka tatafi"
Bayan ankammala komai aka Fara bada kyaututtuka, inda Sauban ya samu kyauta ta musamman. Domin duk wani Mai fad'a aji Wanda ya halarci taron sai da yabawa Sauban kyautar ban girma tare da burgewa."
A nan aka zo Sauran classic duk d'alibin da yayi na d'aya, a ka shiga Kiran sunansa d'aya bayan d'aya ana basu kyauta, Jamila sai murmushi takeyi tana gyara hannu tana jiran Akira yaranta taje da kanta ta k'arb'ar masu Dan Bata buk'atar wani yaje ya amso masu." _halinki ba kyau jamila_ 🤔
Sai da aka kammala Bawa ko wanne class taga ba'a Kira yarantaba haushi da takaici ya k'umeta,
Wayyo Allah kuxo kuga fuskar Jamila ganin ba'a Kira yarantaba bak'in ciki kamar ya kasheta ganin ko wanne yaro sai d'aga kyautarsa Yakeyi Yana Bawa mahaifiyarsa Amma Banda yaranta,
Lura da hakan da Sauban yayi yasa yasaki murmushi ya tako yazo wurin k'annensa ya janyo hannunsu zuwa jikinsa ya rungumesu Yana lallashinsu tare da cewa kuyi hakurin kunji k'annena,
Wani time d'in kuyi k'ok'ari, ku daina Wasa a karatu ,
Kuma za'a baku kamar hakan kunji."
Sadeeq ya fisge jikinsa daga jikin Sauban ya nufi wurin mahaifiyarsa Yana sharar hawaye,
Sunan Sauban akaji ana Kira cikin abar magana Wanda tasaka kowa natsuwa,
Cikin takunsa yanufi wurin da ake kiransa a gaban governor yaje ya tsugunna Wanda shine yasaka akirashi,
Governor yana murmushi Yana kallon Sauban ya d'auki wata kyauta Mai girman gaske Wacce aka lullub'eta a cikin wata Leda Mai haske da kyalli,ya mik'awa Sauban."
Hannu biyu Sauban yasaka ya amsa cike da girmamawa Yana godiya, ai Kuwa aka shiga yi masu hotona,
_wayyo mutuwa kozo kuga idon jamila_😂
Idon kowa Akan Sauban ya mik'e a gaban governor Yana tafiyarsa cikin natsuwa yana d'auke da kyautarsa a hannu kowa sai kallonsa yakeyi Kai tsaye wurin Jamila yanufa ya durk'usa gabanta ya mik'a Mata kyautar
don ta Sanya Masa Albarka,
Ido kansu kowa sai kallonsu yakeyi cike da burgewa
Wad'anda suka San komai sun zuba Ido domin ganin yanda zata karb'eshi,
Ganin Ido kanta snn ga Abdullah da sarki Suma kallonta sukeyi suna murmushi,
yasa tasaki dariya ta k'arb'i kyautar tana murmushin Yak'e Wanda yafi kuka ciwo ta dafa kansa tana fad'in, d'ana kayi k'ok'ari sosai Allah ya taimaka."
ai Kuwa aka shiga d'aukarsu hotona sai murmushin takeyi tana k'ara rungumo Sauban zuwa jikinta, a can cikin zuciyarta kuma jitakeyi kamar ta kurma ihu akan bak'in ciki,
Ganin idanu sun janye kansu Sauban ya koma wurin maimartaba ana hotona yasa tana ganin hakan tayi saurin mik'ewa tsaye tabar wurin tare da Jan yaranta suka shiga mota tanufi gida."
Murmushi manyan Hajjah tasaki domin Sauban ya matuk'ar burgeta da yayiwa Jamila hakan,
Don ko yanzun zata gane idan Rana tafito tafin hannu baya rufeta."
Ana hakan taro ya watse sarki ya dawo gida cike da farin ciki da annashawa, hakan Abdullah sai dai Jin zafinsa d'aya Banda Sadeeq da Sageer Wurin bada kyauta kamar yanda yaga ana Bawa Sauran d'aliban da sukazo na d'aya, yashiga tinanin
Kodai basa karatun ne?"
Hakan yasa suna sauka a mota ya nufi b'angaren Jamila,
Sageer da SADEEQ kwance a kan jikinta tana lallashinsu Sadeeq Yana fad'in Muguntace Sauban ya masu shine ya Hana a basu kyauta a makaranta Wanda Sageer yake cewa ba laifin Yaya Sauban bane laifin uncle ne,
Jamila ta dakawa sageer tsawa tare da zare masa Ido tana fad'in wnn yaron da a asibity na haifeka da nace anyi mun canjenka domin na lura gaba d'aya baka biyo halina ba,
Da zarar anfad'i laifin Sauban yi kakeyi kamar kafashe da kuka, ko ka dakemu,
To bara kaji ka bud'e kunnenka da kyau kaji Sauban ba masoyinku bane Dan ba d'ana bane banice na nahaifeshe ba, kaga ku biyun Nan ku kad'ai na haifa,
Sauban d'an ubane abokin gabarku ne, ko kashesa kukayi ba abinda zai faru, domin idan Baku kashesa ba kunaji Kuna gani zai hau kujerar sarauta,
ku Kuna gefe kuna kallo sai yanda yayi daku kun Zama 'yan kallon kenan."
Sallamar Abdullah yasa taja bakinta tayi shuru illah ta had'e fuska domin Bata ga alamar Wasa a tare dashi ba."
Wuri ya samu ya zauna cikin d'aure fuska tace "barka da shigowa,
"Yawwa yace snn kuyangi suka zagayeshi da kayan motsa baki."
Kallonsa Sadeeq da Sageer sukeyi domin ba'a koya masu gaisuwa ba, shima bai damuba domin yasan irin tasu tarbiyar kenan,
Wanda yayi fad'a har ya gaji ba wani sauyi a tare dasu,
Kallonsu yayi snn ya d'aga masu hannu alamar su zo wurinsa, cikin sauri Sageer ya riga Sadeeq zuwa suka zauna a gefensa."
Kallonsa Jamila tayi ta d'anyi murmushin tace yarona Sauban yayi k'ok'ari sosai."
Shima murmushi yayi ya Kuma had'e fuska ya kalli sadig da sagir yace "meyasa bakuzo na d'aya aka Baku kyauta ba Kuma makaranta kamar yanda aka Bawa kowa?"
Ashe dama ba karatu kukeyi ba?"
Baza kuyi koyi da yayanku Sauban ba?"
Sageer yace munaso Abba,
Sadeeq yace "Ni nafison nafishi ta ko Ina."
Murmushin Abdullah yasaki domin ya dad'e da fahimtar duk halin mahaifiyarsa sadeeq ya d'auko,
Yace "tayaya zakafishi bayan baka mayar da hankali a karatu ba,
Gargad'i na k'arshe da zan Kuma yimaku shine duk kuka kuskura hakan ta Kuma kasancewa sai na d'aukar maku mataki."
Jamila tayi karaf tace "tayaya?"
A'a nifa bana son hakan, duk abinda ya faru da akwai wata a k'asa,
Kai kutashi kushiga daga ciki Allah ya rayamunku domin Ni ka d'ai ke sonku a cikin gidan Nan."
Suka tashi cikin sauri suka nufi d'akinsu,
Ido kawai Abdullah ya zuba Mata baice da ita komai ba ya tashi ya fita Yana tir da Hali irin nata."
Fitarsa b'angaren Hajjah yanufa ya d'auki Sauban ya fita dashi yanufi Gidan gonar mahaifiyarsa, Wanda ya lura da Sauban Yana matuk'ar son zuwa wurin Yana Jin dad'in KASANCEWARsa a cikin gidan gonar Koda yaushe tamkar mahaifiyarsa bintu
Sai kusan k'arfe bakwai suka dawo gida,
BaYan ya Kai Sauban b'angaren Hajjah snn yawuce masallaci sukayi sallar magariba tare da maimartaba suna cikin masallacin akayi Isha'i kamar yanda suka Saba a kullum,
bayan sun kammala yin sallar ne suka fito a tare suna tafiya dogarai na biye dasu a baya
Sarki yake cewa "Abdullah ya kamata kayi aure ka maye gurbin Bintu Wacce ta mutu,
Murmushi kawai Abdullah yayi bai tankawa mahaifin nasaba,
Sarki yaci gaba da cewa idan ka shirya ko a gobe zan d'aura maka aure, sai dai wnn karon mata biyu zaka aura a lokaci d'aya domin inason lokacin da zan sauka a kan kujerar mulki idan za'a d'oraka akai ya zamana kana da Mata hud'u kamar yanda aka San ko wanne sarki,
idan ka cireni daga ciki koni akwai dalilina nayin Mata d'aya."
Murmushi Abdullah yasaki baiyi magana ba domin koshi Yana da buk'atar k'arin auren koba komai ya dinga samun kulawa ya Kuma dinga samun natsuwa idan buk'atarsa ta motsa domin Jamila yanzun Bata da lokacin komai sai mulki dasaka a gaba da hidimar yaranta."
Sarki yace Kai nake saurare meye ra'ayinka ko baka buk'ata ne?"
Girgiza Kai Abdullah yayi cike da girmamawa yace "duk abinda kace shine dai dai,
Bana da zab'i sai naka a kullum burina nayi maka biyayya na faranta maka nasaka ka farin ciki, ko yanzun ka shirya Nima a shirye nake za'a iya d'auramun auren da ko wacce macce kake so zan karb'eta hannu biyu."
Sarki yaji dad'in furucin Abdullah Wanda sai murmushi yakeyi Yana girgiza kai,
Ba Wanda ya sake yin magana a cikinsu har Abdullah ya Kai maimartaba d'akinsa kamar yanda yasaba idan suka dawo sallar, sai ya kaisa har d'akinsa snn yayi Masa sallama yafito yanufi d'akin Hajjah itama yayi Mata sallama snn yanufi nashi d'akin domin ya kwanta,
Wnn karon bayan ya Kai maimartaba d'akin nasa wuri yasamu a gefensa ya zauna tare da sunkuyar da Kai Yana jiran ya Sanya Masa Albarka kamar yanda yasaba snn yatashi yafita."
Sarki ya juyo ya dafa kansa kamar yanda yasaba yashiga "fad'in Abdullah Allah yayi maka Albarka Allah ya sanyawa rayuwarka hak''ika wnn biyayya da kakeyimun Allah yabaka d'anda zai lunka maka fiye da hakan , snn kazama cikin shiri gobe za'a d'aura maka aure da wasu tsala tsalan bayi wad'an da Aka 'yanta Naga sun dace da Kai Allah yabaku zuri'a Mai Albarka."
'Ameen Abdullah yace Yana murmushi Mai cike da jin dad'i."
Wayarsa tayi ringing yayi kamar bazai d'aukaba sarki yayi murmushi yace ka d'auki wayar Mana."
Cikin sauri ya Sanya hannu a Aljihu ya d'auko wayar,
Ganin sunan Abokinsa ne Wanda suka tashi a tare wato sarkin Bauchi Wanda mahaifinsa ya rasu aka d'orashi a kan kujerar mulkin,
Yana murmushin ya d'aga wayar tare da karawa a kunnensa da sallama a bakinsa, cike da tsokana Yake fad'in ranka ya dad'e sarki Allah ya k'ara maka lafiya ya kake?"