← Book details Dan Sarkin Sauban Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 33

Sashe 12

Dan Sarkin Sauban Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Gabanta ya yanke ya fad'i ta kalli kuyangar tace "meyafaru me Yake so yacemun?"

"Ranki ya dad'e Nima bansaniba Amma yace "afad'a maki magana zakuyi Mai mahimmamci ."

"Kije kiyi Masa iso ki ajiyeshi a falon saukar Baki kifad'a Masa Ina zuwa."

"To ranki ya dad'e Allah ya k'ara maki lafiya, kuyangar ta mik'e tafita domin ai watar da umurnin uwar d'akin nata."

Sai da aka d'auki kusan minti 15
Bata fitoba sai da ta dai dai ta natsuwarta akan rud'anin da tashiga sannan tafito cikin k'asaita da nuna Isa tanufi inda sarkin gida Yake a zaune a d'akin Baki."

Tana zuwa cikin Isa da nuna mulki ta nemi kujera ta zauna,
Wanda dama sarkin gida Yana zaune a kan cafet,
Sai da ta zauna ta d'auki k'afa d'aya ta d'ora akan d'aya snn ta juyo ta kalli sarkin gida dake durk'ushe a gabanta Yana fad'in "barka da fitowa gimbiya barka da fitowa sarauniyar gobe Kuma fulanin sarki in Allah ya yarda, Allah ya k'ara maki lafiya,

Tsawa ta daka Masa domin tin farko sarkin gida baya cikin tsarinta asalima haushi yake Bata saboda suffar munafukai garesa, don Yana tsananin shiri da Hajjah sannan ta lura Yana matuk'ar son Sauban da kulawa dashi akan yaranta dako kallon banza basu ishesaba."

"Me Yake tafe dakai ta fad'a a tsawace."

Murmushi yasaki domin yasan Bata son ganinsa, yace "ranki ya dad'e zuwa nayi domin na jinjina maki akan namijin k'ok'arin da kikayi hak'ik'a kinyi matuk'ar k'ok'ari wurin samun nasarar Sauban yaci abincin dakika dafa a jiya, saboda Sauban yarone Mai tsananin wayau Kuma bayacin abincin kowa sai na Hajjah."

Zaro Ido tayi cike da firgici,
Ko me tatina a Nan take ta Kuma saita kanta tare da daka Masa tsawa "rufemun Baki mekakeso kace ne?"
Kana nufin nice nazubawa Sauban wani abin a cikin abinci domin yaci ya mutu?"
Ko kana nufin nice nayi yunkurin kashesa?" Lallai kanaso kayi Wasa da rayuwarka,
Binciken da aka turoka kayi mun kenan?"
to bara kaji kada ka manta Kai sarkin gida ne, Ni Kuma gimbiya ce ko yanzun idan naso zan iya cireka daga matsayin da kake nabawa wani snn daga k'arshe idan naso zanyi sanadin barinka gidan gaba d'aya, Dan hakan. Ka tsaya iya matsayinka kada kayi yunkurin shiga hurumin da banaka ba."

Sarkin gida yace "hakan ne gimbiya matar yarima, gskya kina namijin k'ok'ari a cikin gidan Nan."
to Amma Ni abinda bansaniba shine komeye ribarki ta son kikashe Sauban?"
Kina tinanin idan binciken da sarki yakeyi idan ya gano kece sila komeye makomarki?"

Waifa Ina ganin Dubara ta b'ace maki idon ki a rufe Yake shiyasa Kika aikata abinda Kika aikatawa Sauban,
diba kigani."

Ya Ciro wayarsa a Aljihunsa ya kunna video tin lokacin da Sauban yashiga b'angarenta har zuwa lokacin da yafito har fad'uwar da yayi da lokacin da ya fad'i ta lek'a ta gansa yashe a k'asa tasaki dariya ta koma ta rufe k'ofarta."

Murmushin mugunta sarkin gida yasaki yace "mezakice Dan ganne da wnn video snn bashi kad'ai bane na ajiye wani a wuri Mai mahimmaci,
Ya mik'e tsaye yace idan kinshirya magana Dani Zaki iya nemana tin kafin lokaci ya k'ure maki."

Jikin Jamila duk yayi sanyi hankalinta ya tashi zufa sai tsiyaya take Mata a jiki kamar wacce tafito daga wanka takasa bud'e Baki tayi magana
Har sarkin gida ya Kai bak'in k'ofar fita, sannan tamik'e tsaye tace "dakata sarkin gida."

Cak ya tsaya batare da yajuyo ya kalletaba,
Tafiya ta farayi sai da tazo daf dashi ta tsaya tace " nawa kake buk'ata domin ka rufe wnn maganar?"
zan baka duk abinda kake so in har zaka rufe wnn maganar a cikin gidan Nan."

Murmushi sarkin gida yasaki domin anzo wujen dama abinda Yake buk'ata yaji daga bakinta kenan saboda yasan watan arzikinsa ya kama."

Juyowa yayi ya kalleta yasaki murmushi yace "miliyan biyu kawai nakeso daga gareki ba yawa."

"Bani account no naka tace a tak'aice,
Cikin sauri yashiga karanto mata,
Yana Nan a tsaye cikin minti talatin yaji alert din miliyan uku."

Ta dubeshi tace harda k'ari naiyimaka domin bana buk'atar naji makamanciyar wannan maganar
Kafi kowa sani komai zan iya aikatawa Wanda ya zalinceni,
Kasani muddun maganar Nan tafita bayan nabaka kud'ina kasani da Kai da zuri'arka Kuna cikin tsaka Mai wuya mutuwa ko rayuwa."

"Bakida matsala indai wnn ne ai tinda kin biya shikenan,
Ya Kuma zuwa gabanta ya durk'usa yace "kina burgeni ranki ya dad'e kud'i ba matsalarki bane shin me zai Hana kisaki kud'i domin a aika da Sauban lahira."

Murmushi tasaki ta taka zuwa kan kujerarta ta zauna,
shima sarkin gida ya dawo ya zauna a gabanta domin yaga maganarsa tasamu karb'uwa a wurinta."

"Mekake gani za'ayi domin biyan buk'ata ta na ganin sauban ya bar duniya?"

"Ranki ya dad'e ai wnn aikin Mai sauk'i ne abinda za'ayi shine, kisaye likitan dake kula dashi a asibity da kud'i, ya masa allurar guba a Nan take zai mutu wnn shine mafita."

Dariya Jamila tasaki Mai sauti tace "Ashe dama kana da wnn tinanin da hikima tin tini ka gujeni ka nuna k'iyayyata a fili?"

Kiyi hakuri ranki ya dad'e kece tin farko Kika nuna tsana ga gareni, wnn dalilin yasa bana wata alak'a dake sai dasu Hajjah wad'anda babu abinda suka tsinanamun tin iya zamana dasu sai dai nayita masu bauta Ashe ke Alheri ce."

"Ya Isa tace."
"Ta Yaya zanga likitan domin muyi maganar?"

Ranki ya dad'e indai Zaki saki kud'i ganin likita baya da wani wahala Ni da kaina zan d'auko maki shi na kawo makishi har cikin falonki.
Sabida kinsan Hajjah da sarki sun yarda Dani d'ari bisa d'ari."

Murmushin farin ciki Jamila tasaki tace "ka burgeni ban tab'ajin farin ciki irin na yau ba,
Kaje ka d'auko mun likita ko nawane zan bashi in har burina zai cika ganin Sauban ya daina motsi a doron k'asa,
kaima zakayi murmushi domin idan burina ya cika za kayi mamakin abinda zanyi maka."

"Godiya nake ranki ya dad'e bara natafi kada a ga mundade a wuri d'aya a zargi wani abin, ki Sanya idon ganinmu xuwa anjima tare da likitan."

**************

Bincike akeyi sosai a cikin gidan sarautar domin ganin an kamo masu hannu a cikin wad'anda sukayi yunkurin kashe Sauban,
Ba wani abu da aka gano ko wata alama,
Wanda har da Jamila ake binciken wnn yasa ta b'atarwa mutane da hankali akan ayi bincike a kanta."
Saboda tana matuk'ar nuna bakin cikinta Akan abinda ya faru,
Inda Abdullah yake Mata kallon tafi kowa shiga cikin damuwa na faruwan lamarin wani lokacin har lallashinta yakeyi."

***************

Sarkin gida sai zirga zirga yakeyi tsakanin gida da asibity domin Hajjah tayi matuk'ar yarda dashi duk abinda za'a sawo Dan gane da magani ko wani abun to shi ake Bawa kud'i Ya sawo,
Wnn dalilin yasa yasamu damar keb'ewa wuri d'aya dashi da likita ya fad'a Masa cewar gimbiya tana buk'atar ganinsa yau da misalin k'arfe 8 na dare."

Likita bai kawo komai a ransa ba,
domin yaga yanda sarkin gida yake zirga zirga a asibityn sannan ya lura da yanda aka yarda dashi

Ganin anyarda dashi d'ari bisa d'ari yasa baiyi tinanin komaiba ya amsa Masa da to idan yatashi daga asibity idan zai koma gida Yana Nan tafe,
Yashiga tinanin wata k'ila akan maganar ciwon Sauban ne take nemansa."

Misalin k'arfe 8 sarkin gida ya tsaya a can bayan asibity inda ba Wanda zai iya ganinsa yakira likita a waya, cikin minti 5 likita yafito daga asibity dama lokacin tashinsa yayi, ya tarar da sarkin gida ya d'aukeshi a mota ya nufi wurin gimbiya Jamila dashi."

Hak'ik'a Jamila tayi farin cikin ganin likita a gabanta zaune sai murmushi take saki a fuskarta,
Ta kalli likita da kyau tace "barka da zuwa doctor."

"Yawwa hajiya barka da gida Yaya iyali?" inji likita."

Bata amsa Masa ba tace "Yaya jikin Sauban d'in ?"
ta kuma jeho Masa wata tambyar."

"Alhamdulillah sauki yanata shigosa sai dai har yanzun lakkan jikinsa Bata Fara aiki ba domin. Abinda akayi amfani dashi, Yana da k'arfi sosai domin yafi guba masifa a jikin d'an adam Wanda har yanzun mun rasa Gane ko meye."

Murmushi ta saki ta girgiza Kai, tace "likita katab'a rik'a miliyan 20 a matsayin naka na kanka?"

Wata irin zabura tare da Zaro ido sarkin gida yayi Jin Ankira miliyan 20 to Ashe shi da yace abashi miliyan 2 kad'an ya d'iba kenan tab da yasani da yace sai anbashi miliyan goma."

Girgiza Kai likita yayi yace "ranki ya dad'e a Ina zanga miliyan 20 bare har na rik'eta, kinsan aikin namu a k'ark'ashin wani mukeci, sai dai idan wata ya k'are muke k'arb'ar Albashi Wanda bazai wuce dubu 80 ba dashi muke rufawa iyalinmu asiri tare da 'yan uwanmu."

Wani shu'umin murmushi Jamila tasaki tace "kana son ka mallaki miliyan 20 naka nakanka?"

"Kwarai Kuwa likita yace tare da Kuma gyara Zama."

Jamila tace "so nakeyi a matsayinka na likita Wanda kasan sirrin jikin d'an Adam so nake kasan yanda zakayi cikin hikima da dabara irin taku ta likitoci ka kawar mun da Sauban yaron gidan Nan Wanda kake kula dashi, ya bar duniya."
Idan ka kawar dashi to kasani zaka mallaki miliyan 20 Kai har da ma k'ari domin zan K'ara yi maka wata kyautar ta ban mamaki."

Zaro Ido likita yayi gumi ya shiga wanke Masa jiki, ga k'oshi ga kwanan yunwa,
Yana son kud'i sosai Yana son ya mallaki miliyan 20 din Nan, to Amma idan asirinsa ya tonu Yaya zaiyi da sarki maimartaba Yaya zaiyi da aikinsa Wanda ya dad'e Yana nema da kyar yasameshi."

*REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍

🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴

Writing by
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)

*Page 12*

Taimakon Gaggawa aka shiga Bawa Sauban inda aka sakashi a cikin wata na'ura domin ceto rayuwarsa."

tayi yunkurin shiga inda yake likitoci suka dakatar da ita tare da Bata hakuri da lallashin akan bazata Sami ganinsa ba,
Sai Nan da wata d'aya domin Yana cikin wani yanayi Wanda Addu'arsu kawai ake buk'ata"
Chapter 12 · 0% Book details