Sashe 56
Auren Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Yau Aslam yana zaune a dakinsa a kasan dan karamin carpet dake jikin bed dinsu Yana cin abinci, Siyama tana zaune a saman bed tana bawa Muhammad Nono da yan hakoransa ya gartsa Mata cizo,bata san Sanda ta duke shi ba ji kake dim dim a bayan yaro,dariya yake yana kallonta ya dage kafa daya ya riketa da hannunsa dadi ya gama kaiwa yaro,ya zaci Wasa take Masa sai ya sake cizonta,Siyama ta fisge nononta ta cillo shi kasa aka wani dangwarar da yaro da karfi yaji zafi ya fashe da kuka tace idan ka sake cizona sai na mareka yaro marar kunya ,Aslam Fuska ya daure takaici ya kamashi yace mene haka Wai ke aljanu ne dake ne? wannan yaron me ya sani sabo da Allah dan ya cijeki baza kiyi hakuri ba,Siyama tace kaji zafin Kuwa Ina magana Yana min dariya na yaye shi daga yau yayiwa Kansa bazai sake Shan nono ba,yace ai lokaci bai Kai ba baki Isa kin yaye min yaro ba,ai Kai sai ka bashi naka nonon ya sha,dansa ya dauka da yake zaune yana kuka ya lallaba shi yace kyale Mummy taje da nononta ga abinci yaci gaba da bashi abincin Yana ci,a banza kuma ta huce tazo zata dauke shi Aslam yace kyale min yarona baza ki dinga dukansa a banza ba,Dariya tayi tace Indai shine gashi nan rigimarsa ma ta isheka,an Masa wanka? Siyama tace ae an masa,yaci gaba da lallaba shi Kamar zaiyi bacci sai yaki yi gashi Aslam ana so a Sha soyayya da Siyama yaro yaki bacci,Light ya kashe ko zaiyi bacci amma yaki yi,saman gadon ya kwanta da shi,Siyama zata Yi magana yace shiiiit Shuru Shuru...ana ta lallaba yaro har ya fara bacci Aslam ya lallaba zai tashi yaro ya fashe da kuka,Siyama ta dinga dariya tace matsa ka gani ta kwanta tare da yaron ta sa Masa nono a baki Yana Sha sai bacci Aslam yace wow tana bawa jariri nono yana cire Mata Kaya,aka dauke yaro aka maida shi bed dinsa, sai da suka kwantar dashi yayi bacci,bargonsa Dan karami aka lulluba Masa kansa a waje,tace Yana tashi wajen Nanny Zan kaishi,Aslam yace ban yarda ba babu Nannyn da Zan Bari ta dinga kwanar mim da yaro komai dattijantakarta a zamanin nan da duniya ta lalace sai an kula sosai da yara,gashi nan kyuya ta matanmu tasa suna ta jefa yaransu ga halaka ko a lalata maka rayuwa danka musamman ya mace sai an kula sosai nawa Zaki ji yaron gida yayiwa Yar wani fyade,Yar aiki ta lalata yarka tana lesbian da ita,akwai na kirki a Yan aiki Kinga ko wannan Yar aikin na yarda da ita ta dade a gidan nan I think farko ma a nan kuka taba ganinta,tun Mum tana kasar nan take Mana aiki amma komai yarda ya kamata a kiyaye,Siyama bargo ta ja musu tace to Allah ya Kare mu da yaranmu yace ameen shi yasa baza ki aiki ba karatu dai zan bari kiyi Amma kina gamawa shike nan
Tace to ka tuna min gobe Ina da test ko karatu banyi ba ta mike zata dakko littafi yace ai sai dai kici Kan jaki amma yau babu karatu sai na aure, yaron ne ya farka kadan ya kwala Kira Daddy,Aslam yace baya nan,Jin muryar Aslam sai kuka Siyama tace wannan yaron da babba ne yau sai yaci dukan tsiya,Aslam yace je ki dauki danki ni na gama bangarena bazan sake daukansa ba na gaji,ya isheni da kuka ya hanani bacci karki haifo wani da wuri wannan kadai ya ishemu nan gaba idan Muka huta da yawa sai a Karo haba Yara su dami mutum,Siyama ta tuntsire da dariya tace Kai da kace ayi sauri a Karo yace na janye magana ta yau,kaiwa Nanny shi,Siyama tana ta dariya tace kace danka bazai kwana can ba,yace Kai Mata Allah ya kiyaye kaishi,juyawa tayi zata fita yace Madam da kayan baccin Zaki fita ai tana dakin dake palon kasa,ta fita ta Kai Mata Muhammad,ta karbe shi suka kwanta sai yayi shuru ya koma baccinsa,ta dawo tace har ya koma bacci,yace dumin uwarsa yake son ji ai Kuwa bai Isa ba sai in ba da dare ba,ya jawota Suka Shige bargo
Haka rayuwar ta kasance musu cikin farin ciki da kaunar juna sai jarabawar rayuwa da Allah baya barin bawa ba jarabawa.
ALHMDLLH
Masu Sharhi Ina Matukar godiya wacce ba adadi, gaba Daya yan group din BABU KAUNA musamman masu bibiyar littafin nan Ina Matukar gode muku
Sai Watarana kuma idan da rai da lafiya cikin yardar Allah na sake muku sabon Novel Amma fa Zan dade banyi sabo ba sai an huta an huta an gaji sannan.
Copy by Zainab Butalawa
AsmaBaffa
Tace to ka tuna min gobe Ina da test ko karatu banyi ba ta mike zata dakko littafi yace ai sai dai kici Kan jaki amma yau babu karatu sai na aure, yaron ne ya farka kadan ya kwala Kira Daddy,Aslam yace baya nan,Jin muryar Aslam sai kuka Siyama tace wannan yaron da babba ne yau sai yaci dukan tsiya,Aslam yace je ki dauki danki ni na gama bangarena bazan sake daukansa ba na gaji,ya isheni da kuka ya hanani bacci karki haifo wani da wuri wannan kadai ya ishemu nan gaba idan Muka huta da yawa sai a Karo haba Yara su dami mutum,Siyama ta tuntsire da dariya tace Kai da kace ayi sauri a Karo yace na janye magana ta yau,kaiwa Nanny shi,Siyama tana ta dariya tace kace danka bazai kwana can ba,yace Kai Mata Allah ya kiyaye kaishi,juyawa tayi zata fita yace Madam da kayan baccin Zaki fita ai tana dakin dake palon kasa,ta fita ta Kai Mata Muhammad,ta karbe shi suka kwanta sai yayi shuru ya koma baccinsa,ta dawo tace har ya koma bacci,yace dumin uwarsa yake son ji ai Kuwa bai Isa ba sai in ba da dare ba,ya jawota Suka Shige bargo
Haka rayuwar ta kasance musu cikin farin ciki da kaunar juna sai jarabawar rayuwa da Allah baya barin bawa ba jarabawa.
ALHMDLLH
Masu Sharhi Ina Matukar godiya wacce ba adadi, gaba Daya yan group din BABU KAUNA musamman masu bibiyar littafin nan Ina Matukar gode muku
Sai Watarana kuma idan da rai da lafiya cikin yardar Allah na sake muku sabon Novel Amma fa Zan dade banyi sabo ba sai an huta an huta an gaji sannan.
Copy by Zainab Butalawa
AsmaBaffa