← Book details Auren Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 56

Sashe 22

Auren Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Bata taba ganin ya Mata kyau ba irin yau kallonta yake yi bata sani ba botin din rigarta ya bude daga kirji ana hango shatin boobs dinta,tana aikin kallonsa shi Kuma Yana kallon kirjinta sai kace maye har sai da ta lura tayi maza ta gyara mayafinta da sauri ya dauke Kai kamar bai gani ba ya basar yace Hajiya Aunty Sannu dan Allah ga key dina ki ajiye a wajenki abokina zaizo zai karba a wajenki karki Yi nisa ai kina gida ko? Raudat ta karba da sauri tace to Inshaallah,yace zaizo ne bazan jira shi ba zance zanje nafi so na dawo da wuri Kar ta gaji da jirana ta ce ta fasa ko ya Kika ce? Raudat nan take taji zuciyarta ta dau zafi Kamar tayi kuka dama tunda taga wankan ta firgita,Affan yace Hajiya Aunty ya Kika ce nayi? Kina ganin zata Yaba? Raudat kokari tayi ta danne tayi Murmushi dole tace sosai ma ai yau sai ta kusa Suma Ina tabbatar maka sai tace tana sonka,Affan ya daga Mata babban yatsa ya Bude motarsa wacce ta Sha wanki kal kal tare da shigewa ya bar gidan,Yana barin gidan Raudat kasa tafiya tayi daga wajen bakin ciki da bacin rai yasa ta zauna ragwaf a bakin kofarta ta zuba uban tagumi abin duniya ya Mata zafi tana tunanin bata San Sanda ta Fara hawaye ba har ta koma kuka sosai wiwi,a haka Sayyeed yazo ya samu Raudat yace baiwar Allah lafiya? Raudat da sauri ta tsaida kukanta tare da goge hawayenta tace rasuwa aka min tayi karya,yace Allah yaji Kan rai Dan Allah wace Raudat a gidan Nan?tace nice,yace ashe ma yarinya ce budurwa na zaci Babba ce,Murmushin karfin hali tayi tare da bashi key ta mike ta Shige cikin palonta,tana zuwa ta shiga kitchen ta shirya abinci lafiyayye ta window Sayyeed yaji ana cewa bakon Affan ga abinci,mamaki ya kamashi ganin windows har biyu ta cikin dakunanta suke labile ta janye tare da zuge glass ta Mika Masa tire Kato ya karba Yana kallonta, chocolate ce amma me haske haka Kalar Raudat take kyakyawa ce harda Yar karamar wushiryarta me Yar karamar Fuska jikinta Kuma Kato domin doguwa ce Kuma akwai uban mazaunai da boobs kana ganinta kasan ba karya akwai kudi Hutu da Jin dadin ya ratsata kalarta Kalar yaran Madara ne,Sayyeed dama yunwa yake ji ya zauna Yana ci yana Jin Dadi lallai Raudat tayi yace a ransa gaskiya Ina sonta Indai zata so ni Zan aureta bai San Sabo da Affan ake Masa tarbar ba,window ta sake budewa ta Miko Masa fruits cikin wani bowl ya amsa yace thanks,ta rufe window din,kitchen ta koma ta Fara tunani me Zan bashi ne ya Kara ta shiga tunani sai Kuwa ta bude fridge ta zaro kaza me kankara tayi melting kankarar sannan ta dora farfesu ta shirya shi me Rai da lafiya me dadi kadan ta ragewa kanta ta zuba Masa a flask me kyau da tsada ta sake komawa ta bude window tun kafin ma tayi magana Sayyeed ya Miko Hannu tuni Yana dariya,itama dariyar tayi ta bashi ya karba Yana godiya,yaci ya bar wani ya rufe cikinsa sai da ya cika dam sannan Raudat ta tafi ta gyara gidanta tayi wanka tare da chakarewa cikin Riga da skert na wata sabuwar Atamfa me tsada shape ya fito komai cas da ita Kamar a saceta abinka da Yan gayu wayayyu compound ta fito tana jiran dawowar Affan itama Wai yaga wankanta,Wajen Landlady taje Suka fito compound suna Hira abinsu amma hankalin Raudat yana Hanya.

Siyama Kawunta ne ya kirata yace Siyama zo,har dakinsa ta shiga tare da durkusawa tace Kawu gani yace Siyama Kar kiga Kamar na takura miki,Babanki mahaifi Yana da babban Amini Mai suna Mallam Arifullah,amininsa ne na gaske duk duniya bai da aboki sama da shi tun ainihi liman ne me tarin ilimi Yana da matan sa biyu da yaransa Tara,Bayan babanki ya rasu duk wata sai ya kawo Mana Kayan abinci har Kika girma Kuma tun kina karama duk shekara sai ya Miki dinkin Sallah kala biyu nasan kin sanshi ma Zaki ganeshi domin Yana zuwa gidan nan sosai mutumin kirki ne,Siyama tace na ganeshi Kawu har nake ce Masa Liman amma me kudi,yace yawwa kin gano shi Yana da arziki sosai to shine dai yace Yana da wani yaronsa Wanda ya yaba da nutsuwarsa da tarbiyyarsa me zai hana idan Kun dai daita kuyi aure Kar kice na takura Miki,Siyama tace kawu ya kake Abu Kamar ba Kawuna ba nasan ai baza ka cuceni ba ko,Kuma baza a min auren dole ba sai idan na Amince yace hakane Siyama tace to ba matsala yazo,Kawu yace dan Allah karki watsawa Mallam kasa a Ido Yana kaunarki Yana kaunar mahaifinki,Siyama tace to ita Kam duk duniya bata ga Kamar Aslam ba,duk shi bai nuna Yana sonta ba ya zata yi gwara idan ta samu mijinta Kawai ta aure shi ta huta.

Wanka tayi da kwalliya cikin leshinta me kyau na bikin Nusaiba da tasa Aslam ya dinka mata da shi taci kwalliya ta Sha kyau ta zauna tana jiran Wanda aka ce zai zo.
Affan ne yazo har kofar gidan da motarsa cikin wankansa shi duk gidansu bai dame shi ba yasan shima a baya talakan ne sosai shi yaga ma gidansu da kyansa ba laifi ba ruwansa da wani talaka da Mai kudi duk Daya suke a wajensa,Wayar Kawu ya Kira Suka gaisa yace ya karaso,Kawu yace Siyama yazo Yana kofar gida shigar da shi dakin zaure tace to ta mike ta yafa mayafinta sannan ta fita cikin takunta me kyau,Yana cikin mota ya hangota ta fito ba karya tana da kyau ta hadu ta Kai a so ta amma shi Kam gaskiya wankan Raudat yafi Masa kyau gwara ya kalli Raudat sau dubu,Dake Affan yasan mutunci Fitowa yayi daga motar da gayunsa ya amsa sallamarta,tayi Murmushi tace ka shigo ya bita Suka shiga palon Wanda ba komai sai red carpet dake malale a kasa, Affan baya son Zama a kasa Kar kayansa su yamutse haka ya hakura ya dan dosana duwawunsa,Ruwa da lemon da Kawu ya siyo taje ta kawo Masa sannan Itama ta zauna can gefe,Ina yini tace,ya amsa lafiya Alhmdllh ya mutan gida tace lafiya lau,yanda taga Yana kwalisa bata zaci mutunci haka daga gare shi ba, Affan bai son wulakanta dan Adam shi Kam,baiyi zancen soyayya ba bare zancen aure,bai ma Yi zancen Liman ba Kawai Yana duba wayarsa ya dago Suka hada Ido da Siyama wayarsa aka Kira ya daga Wanda yake siyen shadda a wajensa ne yace ka duba WhatsApp na turo maka da latest,Affan a waya Suka dinga labarin wanka da gayu ita dai Siyama tana ji har ya gama ya duba chat ya gansu zuka zuka,ya nunawa Siyama yace Kinga colors tayani zaba,Siyama ta leka Wayar ta nuna Kalar ta Mata pink tace wannan color yayi,Affan yace ke baki San Kalar maza ba na Mata Kika sani matsa can gefe

Siyama tayi Murmushi ya Gama zabensa pink din data dauka a ciki ya sake nuna Mata yace sai wacce color Kuma? ta sake zaben dark blue,yace sai kace Dan fulani sukayi dariya bai dade ba ya mike yace zai tafi har sun Dan Saba ta rakoshi jikin mota kenan yace me color din Mata sai Watarana kuma,tace to ka gaida gida na gode tana Murmushi dai dai lokacin Aslam ya karaso kofar gidan a motar Sabeer ganin ya fito Gaban Siyama ya Fadi Haka Kawai taji kunyarsa da tsoronsa ya kamata tana zance,kallon Affan yayi Kawai Aslam ya bata rai ya daure Fuska tam juyawa yayi ya koma cikin mota yace Sabeer muje kawai,Affan bai sani ba ya zaro kudi dubu biyar yace gashi ki sa Kati bai San ko waya Bata da ita ba,Aslam ya kura musu Ido gashi Yana yiwa Sabeer masifa muje dalla malam
Siyama kin karbar kudin tayi Affan yace mene haka Kuma bana so nayi kyauta a maida min,Siyama juyawa tayi Kawai ta Shige gida duk ta firgice ta tsorata, Affan baki ya tabe yaja motarsa ya wuce,Aslam tuni sun tafi.

Siyama tana komawa gida tace kawu ya tafi Aunty na dawo Suka ce to sai bayan Isha Kya bamu labari tace to tare da fadawa dakinta ta kwanta akan katifarta ta fashe da kuka Wai Aslam ya ganta tana zance har da cewa na shiga Uku na shiga dubu tana rusa uban kuka Kamar wacce aka Mata mugun duka,Aunty ce taji kukanta ta fado dakin da gudu tana cewa me Zan gani Siyama lafiya? Saurayin ne yaci Miki mutunci ko me? Marinki yayi? Siyama tace shike nan tawa ta Kare na gama yawo ta sake sakin kuka tana shesheka tace Aslam ne Aslam,Aunty tace mutuwa yayi? Siyama tace Aunty Aslam Aunty wash...shike nan Aunty Aslam ya kamani ya ganni Ina zance Innalillahi, Subhannallahi,Ashahdu Allah ilaha illallah ta Dora Hannu aka tace Aslam kuru kuru ya ganni,Aunty Tsaki ta ja tace ke dalla rufe Mana baki mahaukaciya amma dai sonsa kike dama ko? Charity tace Mijin Nusaiban haba Aunty mijin kawata kuma abin kunya ne ai,Aunty tace to rufe Mana baki sakarya, Kawai ki Fara Mana kuka sabo da rashin aikin yi,Siyama tagumi ta zuba tana goge hawaye ta kasa tashi Sam sabo da jimami.
Chapter 22 · 0% Book details