← Book details Auren Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 55 OF 56

Sashe 55

Auren Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Sai Yamma likis ta koma gida, Siyama kuwa ganin Nusaiba ta tafi tace dan Allah wannan abinda kakewa Nusaiba ka daina Sweetheart,ba dadi tana son danka ka dinga Mata haka Indai tazo kana nan bata sakewa, kin San fa me ta min Yarinyar nan bai kamata ma ki dinga kulata ba tunda wani abin a gabanki akayi,ya Ilahi ta gane kurenta ta nemi yafiya me yayi saura gaskiya ni ka daina Mata haka ba dadi,to nan fada kike min ko umarni kike bani ko kuwa shawara? tunda kina sonta haka sai aje a maida aure ta dawo ku Zama kishiyoyi sai kuci gaba da zumunci,Siyama ta bude baki tare da furta haka nace maka? Kawai kace sonta kakeyi har yanzu zaka dawo da ita shine magana kawai,dansa ta Mika Masa ungo danka ko na fatalar da shi,ya karbi abinsa ya haura sama Yana dariya a ransa,tace ka dawo muyi magana akwai wani abu kasa a ranka wannan Maganar bata mutu ba,bai kulata ba tun daga ranar Siyama bata sake zancen Nusaiba ba, bakinta kanin kafarta har Bata so ma Nusaiba tazo su hadu da Aslam.

Tana zuwa kofar gidansu taga Machine din Salahu masoyinta Wanda ya fece,ko kallonsa bata Yi ba zata wuce ya dakatar da ita yace Nusaiba dan Allah kiyi Hakuri ki yafe min nayi kuskure,Kiyi hakuri dan Allah,tunawa tayi yanda itama tayiwa wasu laifi Kuma aka yafe mata tace ba komai na yafe maka,Yace dan Allah ki bani dama na dawo da Maganar auren mu,dama gwadaki nayi na gani da gaske kina sona tsakani da Allah Kuma na tabbatar naji labari,Nusaiba tace waye ya baka labarin? Yace Aslam tsohon mijinku shi yace kin canja yanzu Kar na dauki zugar mutane idan Ina sonki tsakani da Allah na dawo na aureki ya fada min kinyi nadama ke yanzu sabuwar Nusaiba ce,Nusaiba Murmushi tayi jin Wai Aslam da Kansa yasa baki a aureta shi da ya tsane su,juyowa tayi tace in ka shirya ka turo manya bani bukatar yin sabuwar hirar soyayya da kai ka azabtar da zuciyata,Salahu yace kiyi hakuri na gode Kuma Inshaallah Jibi za a turo ki fadawa Abba,Nusaiba Kamar bata murna ta fada gidansu sai Murna tana cewa Mama Allah ya amsa ta bawa Mama Labari,Mama tace Kai duniya shi yasa akace ka taka a sannu.

Bayan wata daya aka Sha bikin Nusaiba da angonta,Ihsan da nata itama ma'aikacin banki,Mijin Nusaiba gida ne Wanda iyayensa Suka mutu suka bar Masa gado ya gyara shi sosai ya maida shi na zamani yayi kyau dan madaidaici harda gate dinsa ko Ina tiles tsakar gida broken tiles ne dagwas, Landlady ita tayi kayan kitchen na Nusaiba da Ihsan sauran Kuma Shehu ne yayi Kamar yanda uba ke yiwa yarsa,Affan ne da Raudah Suka hada lefe Akwatu hudu kasancewar Angon yaron Affan ne na hannun dama,machine din ma Lifan Affan ne ya siya Masa,Siyama ce ta tasa Aslam a gaba da kuka sai ya bata kudi tayi gudunmuwa dan Dansa da Nusaiba ke so yace me za ayiwa Nusaiba me ya dace, Siyama tana share hawaye tace a bata jari tunda mijinta baida hali sosai sai rufin asiri idan aka bata sai ta dinga sana'a a gidanta ko irin dan siyar da su Maggi,omo etc,Nawa za a bata? dubu dari ? Yace to Zan Miki transfer ki tura Mata kice gudunmuwarki ba ruwana a ciki,Siyama tace hakan ma yayi na gode,haka ta turawa Nusaiba Suka Yi shawarar kayan da zata dinga siyarwa nan gaba,Ango Kuma yace in sun Gama amarci zai maida ta makaranta itama tayi ilimi,Nusaiba sai godewa Allah akeyi ana murna.
Siyama kuwa Private University Aslam ya sata taci gaba da karatunta tana kula da danta Wanda yayi wayo sosai.
Aisha ta Haifi yarta mace katuwa,Nabeela ma mace ta Haifa,sai matar Sabeer da ta Haifi Yan biyu duka maza manya,su Aslam sune na hannun dama a nan.

Raudah ce bata Haihu ba har sai da cikinta ya shiga wata goma,Affan yace idan ba dama Kawai suje asibiti ayi aiki a cire dan,Raudah tace bazai yuwu ka kassara min rayuwa ba in samu matsala Ina lalacewa wata zaka aura haihuwa ta Allah ce a barni Allah zaiyi ikonsa haka Kawai ayi min aiki nazo na samu akasi matsala ta afku shike nan sai naji gudar Amarya a gidana bada ni ba,Affan yayi dariya yace wannan zafin kishi Ina za a kaishi Raudah ni nace zanyi kishiya Ina nake da wannan kwarin gwiwar ni waye ni,who be me? bayan kin gama dani sai abinda Kika ce,Suna haka Kamar Wasa Raudah ta fara Nakuda,damtsen Affan ta rike tace bala'iiii ah'ah Affan....wayyo ta kwala ihu ta rike Mara tace Subhannallahi...mutuwa zanyi..Affan yace idan Wasa kike ma ki daina,tunda yaji Raudah ta hayayyako Masa da masifa da bala'i Kamar zata cinye shi karka isheni karka dameni,Malam ka saurara min bana son wulakanci...yace to da gaske ne nakuda ce muje asibiti tana masifa taya Zan iya tashi ta balla Masa harara,bata ita yake ba ya dauketa da kyar ya sata a mota,tace kayan haihuwar ko da yatsunka za a yanke cibin? Affan yace ki dinga bina a hankali Baby, tace Kar na sake Jin kalmar nan a bakinka,Affan ya koma da gudu ya dakko takarkacen data shirya,ya figi mota tana ta faman wash wash Allah na har suka je asibiti aka dauketa cikin gaggawa,Affan hankalinsa a tashe sunfi kafin 1hr sannan aka ce Masa ta haihu,Uwar gidan Liman ce a wajen Raudah itama Namiji ta santalo katon gaske da gani ya dade a ciki,Raudah ta Sha wahala ba a sallameta ba sai washe gari da Yamma sannan,Matar Yusuf har tazo,Haka Maman Raudah da kanwar mamanta sunzo Suka ce tafiya zasuyi da ita,Affan yace bai yarda ba ya dauke jariri ya Hana kowa

Da kyar ya hakura yace iya sati biyu daga Haka karta Kara ko kwana daya,suka tafi kuwa har kudin rago Affan sai da ya tura raguna guda biyu sai dai suyi waya da Rauda ko video call yaga jaririnsa,Ranar Suna yaro yaci Abdallah,su Raudah acan sun Sha shagalin suna,tana cika sati biyu Affan yaje airport ta sauka da jaririnta ya dakko matarsa Suka dawo gida,sai lokacin suka nemi yar aiki Nanny dattijuwa me Kamala,Siyama har barka taje mata itama.
Nusaiba Kuwa an Kama sana'ar Omo da su Maggi etc Hannu bibiyu har yasa ta zana waec da Neco tana Fitowa bata samu direct degree ba sai NCE ya sama mata ta Fara zuwa,Siyama kuwa anyi nisa a school,Su Nusaiba an farfado kullum Mama cewa take ta kula da mijinta ta rike shi Hannu bibiyu Kar tayi Wasa da aurenta.
Bayan wata biyar Landlady ciki ta samu dama bata taba haihuwa ba yanzu ta samu a gidan Shehu,Ihsan itama sai ciki har ta samu ciki kullum laulayi da amai,Nusaiba kuwa nata cikin ko abinci ba komai take iya ci ba sai abinda taji zuciyarta ta raya mata Haka suke fama

Siyama danta har ya fara rarrafe gwanin sha'awa gashi ta tara masa suma an daure Masa ita kamar yaron turawa kowa ya kalle shi yasan ba karya dan gidan Yan gayu ne,shi kuwa Affan Abdallansa kaishi yake ana Masa shegen aski style style har sumar tayi yawan gaske Yana zama,Babu style din da ba'a Masa yaron nan,kayansa ma in aka saka Masa kasan babansa dan wanka ne yanda ake kwalkwale yaron nan,idan Yana gida har goya shi yake yasa zani ya daure abinsa a baya Kamar mace haka Affan ke yi, yau ma Yana gida ya goya Abdallah a bayansa ya daure shi da zani harda jijjiga shi Raudah tana Masa dariya.

Bayan wasu watanni Nusaiba ta Haifi yarta mace Siyama sune na jikin gado,ranar Suna aka sa mata Jawahir, Nusaiba ana zaune cikin rufin asiri ba rashin ci ba rashin sutura Yar unguwarta idan zata je ya dauki matarsa a machine dinsu abinsu shar, Nusaiba da shegen Iyayi harda koyon machine Lifan ta iya sosai sai ta saka riga da wando ta sa Abaya da mayafi taci glass ta tuka machine taje inda taga dama,Landlady ta haifi Namiji itama. Muhammad din Siyama yayi wayo ya Fara Kiran Daddy da Mummy Yana tafiyarsa ko Ina dagwai dagwai Amma ba sosai ba, idan Aslam bazai dade a Office da shi yake tafiya yaron suje su dawo
Chapter 55 · 0% Book details