Sashe 11
Auren Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai Yamma baici komai ba ya dawo ya iske Siyama tana Shirya Dining sallama yayi ta amsa tare da furta Sannu da zuwa,Nusaiba fa? Ya tambaya tace bacci takeyi Kai ya jinjina ko a jikinta ita, wanka yayi ya canja kaya wani yard hadadde ya fito da takardu zai sake fita Siyama tace dan Allah ka tsaya kaci abinci tukun,wa ya bani lokacin cin abinci ya furta,tace ka dai Yi hakuri ka dauki komai a nutse,Dining din ya karasa ya zauna Yana Kiran Abokinsa Sabeer Wanda tunda matsalar ta faru tare suke shige da ficensu,Jullof rice ta zuba Masa taji Hadi sai dai ba nama tace Naman fridge din ya Kare jiya Nusaiba ta kwashe ta soyesu duka suna dakinta a soye,yace kyaleta ya fara cin abincin yaji ba nama amma yayi mugun dadi yace Wai ke da Nusaiba waye ya girmi wani ne? Dariya Charity tayi tace Santi ne ko me? Yace na Dade Ina so na tambaya sai na manta yau dai na tuna,Na girmeta Mana ai Nusaiba bama sa'a ta bace Kawai dai school ne ya hadamu kasan makaranta ba lallai ace shekarunku Daya ba ni na girmeta da wurin shekaru uku Yayarta ce ni Charity Allah yayota da son girma Yan watanni ta bawa Nusaiba amma sai tayi ta cewa shekaru ta bawa Nusaiba,Nusaiba ce ta fito ita ba alamar Wasa a fuskarta tace to munafuka na hakura da aikinki ki tattara kayanki ki tafi gidan ubanki,sai wani shishigewa mijina kike Yi karuwa,Charity tace Ina zani ba inda Zan tafi Zama daram,gidanki ne Naga nina kawoki ko,to bazan tafi ba cewar Siyama har ya gama cin abinci suna fada ya mike ya fice,Yana barin gidan Nusaiba ta Kira wani mutum tace ya fita kazo ka dauki motar,Wanda ta Kira bai Dade ba yazo ya shiga katuwar motar Aslam me tsada ya fita da motar,Hijab ta saka tabi Wanda ya dauki motar,wurin siyar da motoci Suka karasa aka Yi cikin mota Wanda ya siya yace ki dawo gobe ki karbi kudi tace to ta tsaya a gefen titi zata shiga mota sai ga wani matashi a dankareriyar mota da alama Yana da kudi yace ranki ya dade barka da Yamma,Nusaiba ta kalleshi ta ja tsaki,yace Dan Allah idan baza ki damu ba ki shigo na rage Miki Hanya,Bata kulashi ba sai da ya fito daga motar wani baki ne Dan mummuna da shi yaci gayu Yana kamshi yace dan Allah ki shiga na rage Miki Hanya sai muyi magana,motar ta bude tare da shigewa Gaban motar ta zauna ya shiga shima yace ko na kaiki wurin cin abinci zamu fi sakewa a nan,tace to ya ja mota zuwa wani hadadden Joint Suka zauna yasa aka kawo Mata lafiyayyen abinci shima haka suna ci suna labari,yace tunda na ganki naji Ina sonki Nusaiba,Dan Allah ki so ni ki aureni,Nusaiba tace Ina da aure Amma karka damu auren ya kusa mutuwa,Matashin me Suna Sufyan yace Alhmdllh Allah yasa ya sakeki da wuri muyi aurenmu,Nusaiba tayi Murmushi tana kora lemo har Suka gama hirarsu wurin magriba ya kawota har bakin gate ta fita tana Masa bye bye ta Shige gidanta,tana Shiga Aslam Yana sama Yana kallonta ta saman yace daga Ina kike Ina motata da Kika fita da ita? Kallonsa tayi Kawai ta dauke Kai,da sauri ya sakko cike da bala'i bata taba sanin ya iya Fushi ba sai yau sai da ta tsorata cikin tsawa yace Ina motata,Tace karka dameni mari ya kwada Mata Karo na farko kenan,Siyama ta fito taga abinda ke faruwa yace Ina motata,Nusaiba ta firgita dafe da kumatu ta fada cikin Palo da gudu
Wata wire doguwa Siyama ta Mika masa tace ungo ka zaneta sai ta fito maka da mota karka yarda tunda bata Jin magana,karba yayi ya bita ya zaneta tas yasa key ya kulleta a wani daki yace sai ta fito Masa da mota sannan zai Bude ta,Nusaiba ta fashe da kuka ba shiri ta Kira Mamanta,tana dagawa tace kizo Mama Aslam zai kashe ni wlh ya min dukan tsiya sannan ya kulleni a daki sai na fito Masa da mota,Mama tace karki damu gani nan zuwa gidan duk zafin talauci ne ya dame shi
Aisha zaune take a dakinta da aka gyara Mata cikin gidansu na rufin asiri babansu ya sata a gaba da fada yace yanzu ke abinda Kika Yi kin kyauta haihuwa bata Allah bace, ba fa lallai ki samu miji kamar Farooq ba amma tunda haka kika zaba ga gidan nan kizo kiyi ta zama Allah ya bada sa'a wata haihuwar ma ba gwara babu ba da ita wasu yaran ma in Banda su addabi alumma me suke yi yanzu watakil Baki San Wanda Zaki Haifa ba Allah ya dubaki ya hanaki amma baki gode ba Kawai ke dai ki Haihu ai shike nan ya mike ya fice.
Aisha tana gida Farooq yaje biko yafi sau Nawa Taki yarda har ya gaji ya hakura,Umma ce ke fada na gaji da kwanciyar nan taki Aisha tunda Kika zo bakya hasala komai a gidan nan sai kwanciya baiwarki ce ni da Zan zauna kullum sai dai na dafa na baki kici ko Sanda kina gidan mijinki Haka kike yi,Aisha ta mike zaune cike da Takaici domin kullum aikin gidan nan kusan ita ke Yi amma mamanta ta hanata sakewa ta Saba da gidanta sai abinda taga dama gaba Daya a takure take jinta,tashi tayi tace gaskiya ni na gaji kullum aiki kullum aiki,idan baki ba Kuwa wallahi babu ke ba cin abinci a gidan nan,Aisha ta zauna Kuwa taki tashi ita kuma Ummanta tana Gama abincin ta hanata ranar yini tayi suna fada da Ummanta kowa na Jin haushin kowa,Aisha sai gidan Yan Uwa taje taci abinci ta dawo.
Washe gari ma Aisha ta daura gaba da Ummanta ba Wanda yace wa wani ko kazil suna ta gaba da juna,Umma bata Mata magana itama Aisha haka,Takaici yasa Umma ta Kai karar Aisha wurin Babanta tace Wai ka Haifi yaro a cikinka ya dinga gaba da kai Alhaji ka duba Aisha Wai dani zata Yi gaba,Alhaji yace ba ruwana karki sake kawo min Maganar Aisha ke Kika je Kika zugata ta fito daga gidan mijinta sai ku zauna tare gaki gata nan ai,Umma ta fito tana hawaye tace dama nasan baza ka Mata fada ba tunda ba kaunata kake ba Watarana Naga Alama Aisha dukana zata Fara Yi a gidan Nan,Aisha tana ji ko magana haka tayi mirsisi da ita ta Danna headphone a kunnenta tana Jin Waka tana bi da bakinta baza ma taji fadan ba bare ma ta sakko,kwafa Umma ta ja ta koma ta Fara wanke wankenta Aisha baza tayi ba.
Affan tubewa yayi ya Shiga wanka ya fito daure da guntun Towel,Raudat tana bedroom itama ta window tana hango shi Yana shiryawa Yana ta faman shafe shafe da feshe feshen jikinsa da turaruka Yana ta kalailaita har yafi mace,tunda yazo taje sumarsa yafi minti talatin Yana Abu Daya akan Suma,Raudat baki ta tabe ta saka doguwar rigar baccinta me Dan kauri ta kwanta tare da shigewa bargo duk bata da sukuni sabo da Affan zai kalleta komai sai ta faki idonsa take yi,Yana kallonta duk abinda takeyi kayan baccin ma a toilet ta shirya,Dan gajeren wando ya saka sannan ya zauna a bakin bed Yana Shan ruwa,windown ta ya bude glass yace iska Wai zai Sha,Raudat ta mike ta zuge,ya sake tashi ya bude,ta fito daga bargo ta zuge kafin ta koma ya Mika hannu ta cikin window ya jawo rigarta ta manne a jikin bango rankwashinta yayi ta saki Kara yace karki dawo nan na fada Miki idan ba haka ba Zan dawo cikin bedroom dinki,Raudat da taurin Kai tace wlh baka Isa ka hanani sukuni ba ta maida Hannu zata kulle window ya taka windown ya dane ya shigo cikin bedroom dinta ta window daga shi sai gajeren wando,ihu ta saki kwarto Jama'a kwarto,yace yau sai munyi musayan bed ki kwana a nawa yau a naki Zan kwana tace Allah kiyaye ka shafa min kazantarka a gadona,takawa yayi da Niyyar Daukanta tayi sauri ta taka window tare da dirgawa cikin bedroom dinsa tana ihu,Windown ya kulle yaje ya fada saman gadonta ya kwanta,tace Allah ya Isa mugu azzalumi taci gaba da tsaiwa tana kallon dakinsa ya Sha furniture komai me tsada da kyau ko Ina kamshi yake a ciki Kal Kal Tsaki ta ja ta shiga kitchen dinsa kamar na Amarya komai akwai Raudat tace lallai ya shiryawa karya mutumin nan ta duba sosai tana Bude flask taga soyayyar kaza ta hau kaza da ci taci da yawa sai da ta kusa cinyewa sannan ta duba fridge taga wani katon juice an tsiyayi rabi a ciki ta dauka taci gaba da Shan abinta ya leka ta window Yana kallonta bata sani ba kwayar maye ya saka Mata a ciki yasan kwadayinta sai ya kaita ta Sha,Nan da nan Raudat ta Zama wata Yar kwaya ta kasa bacci taji wani karfi ai sai ta hau gyaran gidan ko Ina sai ta share ta goge ko ba dirty Bata Yi bacci ba Yana dakinta Yana sheka bacci akan gadonta ita Kuwa tana ta gyara Masa gida lungu da Sako har kasan bed sai data janye ta share ta goge ta gyara komai ta fada toilet ta wanke ta goge ko Ina ta dawo aiki bai isheta ba ta fito da kayan fridge ta wanke komai ta goge ta maida kayan neat ta dawo ta rasa me zata Yi ma ta bude kofa tsakar dare ta fita ta Fara sharan uban compound da parking space kowa na bacci tana ta fama kafin gari ya waye ta share compound din me dauke da Interlock ya dawo tsaf,flowers din dake compound har su ta share kasansu kafin gari ya waye taji jiki bata sani ba sai data gama ta fada dakinsa inda ta fito lokacin Sallar asuba yayi lokacin kwayar ta Fara sakinta ta window ta sake haurawa zuwa dakinta ta fada Saman bed bata san da mutum ba ta manta jikinta ya mutu Affan Yana bacci yaji jiki me laushi ya fado Kansa
Wata wire doguwa Siyama ta Mika masa tace ungo ka zaneta sai ta fito maka da mota karka yarda tunda bata Jin magana,karba yayi ya bita ya zaneta tas yasa key ya kulleta a wani daki yace sai ta fito Masa da mota sannan zai Bude ta,Nusaiba ta fashe da kuka ba shiri ta Kira Mamanta,tana dagawa tace kizo Mama Aslam zai kashe ni wlh ya min dukan tsiya sannan ya kulleni a daki sai na fito Masa da mota,Mama tace karki damu gani nan zuwa gidan duk zafin talauci ne ya dame shi
Aisha zaune take a dakinta da aka gyara Mata cikin gidansu na rufin asiri babansu ya sata a gaba da fada yace yanzu ke abinda Kika Yi kin kyauta haihuwa bata Allah bace, ba fa lallai ki samu miji kamar Farooq ba amma tunda haka kika zaba ga gidan nan kizo kiyi ta zama Allah ya bada sa'a wata haihuwar ma ba gwara babu ba da ita wasu yaran ma in Banda su addabi alumma me suke yi yanzu watakil Baki San Wanda Zaki Haifa ba Allah ya dubaki ya hanaki amma baki gode ba Kawai ke dai ki Haihu ai shike nan ya mike ya fice.
Aisha tana gida Farooq yaje biko yafi sau Nawa Taki yarda har ya gaji ya hakura,Umma ce ke fada na gaji da kwanciyar nan taki Aisha tunda Kika zo bakya hasala komai a gidan nan sai kwanciya baiwarki ce ni da Zan zauna kullum sai dai na dafa na baki kici ko Sanda kina gidan mijinki Haka kike yi,Aisha ta mike zaune cike da Takaici domin kullum aikin gidan nan kusan ita ke Yi amma mamanta ta hanata sakewa ta Saba da gidanta sai abinda taga dama gaba Daya a takure take jinta,tashi tayi tace gaskiya ni na gaji kullum aiki kullum aiki,idan baki ba Kuwa wallahi babu ke ba cin abinci a gidan nan,Aisha ta zauna Kuwa taki tashi ita kuma Ummanta tana Gama abincin ta hanata ranar yini tayi suna fada da Ummanta kowa na Jin haushin kowa,Aisha sai gidan Yan Uwa taje taci abinci ta dawo.
Washe gari ma Aisha ta daura gaba da Ummanta ba Wanda yace wa wani ko kazil suna ta gaba da juna,Umma bata Mata magana itama Aisha haka,Takaici yasa Umma ta Kai karar Aisha wurin Babanta tace Wai ka Haifi yaro a cikinka ya dinga gaba da kai Alhaji ka duba Aisha Wai dani zata Yi gaba,Alhaji yace ba ruwana karki sake kawo min Maganar Aisha ke Kika je Kika zugata ta fito daga gidan mijinta sai ku zauna tare gaki gata nan ai,Umma ta fito tana hawaye tace dama nasan baza ka Mata fada ba tunda ba kaunata kake ba Watarana Naga Alama Aisha dukana zata Fara Yi a gidan Nan,Aisha tana ji ko magana haka tayi mirsisi da ita ta Danna headphone a kunnenta tana Jin Waka tana bi da bakinta baza ma taji fadan ba bare ma ta sakko,kwafa Umma ta ja ta koma ta Fara wanke wankenta Aisha baza tayi ba.
Affan tubewa yayi ya Shiga wanka ya fito daure da guntun Towel,Raudat tana bedroom itama ta window tana hango shi Yana shiryawa Yana ta faman shafe shafe da feshe feshen jikinsa da turaruka Yana ta kalailaita har yafi mace,tunda yazo taje sumarsa yafi minti talatin Yana Abu Daya akan Suma,Raudat baki ta tabe ta saka doguwar rigar baccinta me Dan kauri ta kwanta tare da shigewa bargo duk bata da sukuni sabo da Affan zai kalleta komai sai ta faki idonsa take yi,Yana kallonta duk abinda takeyi kayan baccin ma a toilet ta shirya,Dan gajeren wando ya saka sannan ya zauna a bakin bed Yana Shan ruwa,windown ta ya bude glass yace iska Wai zai Sha,Raudat ta mike ta zuge,ya sake tashi ya bude,ta fito daga bargo ta zuge kafin ta koma ya Mika hannu ta cikin window ya jawo rigarta ta manne a jikin bango rankwashinta yayi ta saki Kara yace karki dawo nan na fada Miki idan ba haka ba Zan dawo cikin bedroom dinki,Raudat da taurin Kai tace wlh baka Isa ka hanani sukuni ba ta maida Hannu zata kulle window ya taka windown ya dane ya shigo cikin bedroom dinta ta window daga shi sai gajeren wando,ihu ta saki kwarto Jama'a kwarto,yace yau sai munyi musayan bed ki kwana a nawa yau a naki Zan kwana tace Allah kiyaye ka shafa min kazantarka a gadona,takawa yayi da Niyyar Daukanta tayi sauri ta taka window tare da dirgawa cikin bedroom dinsa tana ihu,Windown ya kulle yaje ya fada saman gadonta ya kwanta,tace Allah ya Isa mugu azzalumi taci gaba da tsaiwa tana kallon dakinsa ya Sha furniture komai me tsada da kyau ko Ina kamshi yake a ciki Kal Kal Tsaki ta ja ta shiga kitchen dinsa kamar na Amarya komai akwai Raudat tace lallai ya shiryawa karya mutumin nan ta duba sosai tana Bude flask taga soyayyar kaza ta hau kaza da ci taci da yawa sai da ta kusa cinyewa sannan ta duba fridge taga wani katon juice an tsiyayi rabi a ciki ta dauka taci gaba da Shan abinta ya leka ta window Yana kallonta bata sani ba kwayar maye ya saka Mata a ciki yasan kwadayinta sai ya kaita ta Sha,Nan da nan Raudat ta Zama wata Yar kwaya ta kasa bacci taji wani karfi ai sai ta hau gyaran gidan ko Ina sai ta share ta goge ko ba dirty Bata Yi bacci ba Yana dakinta Yana sheka bacci akan gadonta ita Kuwa tana ta gyara Masa gida lungu da Sako har kasan bed sai data janye ta share ta goge ta gyara komai ta fada toilet ta wanke ta goge ko Ina ta dawo aiki bai isheta ba ta fito da kayan fridge ta wanke komai ta goge ta maida kayan neat ta dawo ta rasa me zata Yi ma ta bude kofa tsakar dare ta fita ta Fara sharan uban compound da parking space kowa na bacci tana ta fama kafin gari ya waye ta share compound din me dauke da Interlock ya dawo tsaf,flowers din dake compound har su ta share kasansu kafin gari ya waye taji jiki bata sani ba sai data gama ta fada dakinsa inda ta fito lokacin Sallar asuba yayi lokacin kwayar ta Fara sakinta ta window ta sake haurawa zuwa dakinta ta fada Saman bed bata san da mutum ba ta manta jikinta ya mutu Affan Yana bacci yaji jiki me laushi ya fado Kansa