← Book details Auren Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 56

Sashe 10

Auren Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

Bayan sati biyu Charity tana gidan kullum tana kallon haukar da Nusaiba take zubawa Iskanci kala kala Aslam bai Isa da ita ba duk da haka Siyama sai ta fada mata gaskiya tana ta kokarin ganar da ita tana kwantarwa da Aslam hankali Abu yaci tura kullum ma abin na Nusaiba karuwa yake Yi,Mota me kyau ta million uku ya siyowa Nusaiba ya shigo da Fara'a yace yau zaki surprise Zo muje ki gani,Charity tana goge dining yace taho kema ki taya kawarki murna,Nusaiba tana zumudi tace ka daina cewa kawata Yar aiki na ce fa suna Fitowa ya nuna Mata dalleliyar mota sabuwa ya Mika Mata key yace gashi Taki ce,Maimakon fara'a da murna sai aka ga Nusaiba ta bata rai tace yanzu Baby ka rasa motar da zaka siyo min sai Toyota Carina matan masu kudi irinka suna Hawa manyan motoci su Marcedes benz su perari,bugati amma kamarka me kudi haka ka siya min Toyota ordinary Toyota,Da karfi charity tace Nusaiba...oh my God wannan wacce irin rayuwa ce,ke Kika nema Masa kudin,Nusaiba ki tuna fa gidanku da inda Kika fito,Tsaki Nusaiba ta ja ta koma ciki abinta tace bana so Indai Toyota ce wallahi bana so,zuciyar Aslam ji yake kamar ta fito sabo da bakin ciki da bacin rai,Charity har kwalla tayi sabo da takaicin Nusaiba da tausayin Aslam,tace kayi hakuri dan Allah,kaddara ce Allah ne ya jarabceka kayi hakuri ka cinye jarabawarka,kowanne Dan Adam da tasa Jarabawar kayi hakuri ka kwantar da hankalinka please,Aslam kasa magana ma yayi ya wuce ciki Kawai.

Bayan wasu Yan kwanaki Aslam kullum cikin damuwa yake ko abinci bai iya ci,hankalinsa a tashe Charity ta kula da Haka amma matar tasa Nusaiba bata ma gane shi ba Kawai a bata kudi ita Kam, Yana zaune a garden yayi tagumi Yana ta waya Charity taje har Inda yake,sai da ya Gama Wayar tace sir Ina da Yar tambaya ne,yace go ahead Ina jinki,Nusaiba ce tazo wajen sanye cikin bum short da Yar wata t-shirt yace amma kin San me gadi zai iya ganinki da wannan shigar ko? Nusaiba tace naji tana tabe baki,Charity tace Naga kwana biyu kullum cikin damuwa kake ko abinci baka ci,Nusaiba tayiwa Charity wani banzan kallo up and down tace ke a wa Kuma da wannan tambayar,Aslam bai kula Nusaiba ba yace matsala na samu da kayan Dana shigo dasu gashi bashin bank na karba Kuma kayan sun salwanta ba ma custum ne Suka Kama ba jirgin ruwa ne yayi hatsari Suka nitse,yanzu komai nawa banki ne zasu karbe har gidan da nake ciki motocina da komai Ina Miki zancen yanzu Banda komai nan da sati ma bank zasu zo sabo da dana karba wata Daya nace Zan maida kudin kin San Kuma bashin banki,Innalillahi wa Innailayhirraju'un cewar Siyama tace kayi ganganci kaima daka karbi bashin bank gaba Daya ka tura aka turo da Kaya da kudin,yace duk kadarar da na mallaka Ina fada Miki baza ta biya bashin bank din ba,Wata shewa Nusaiba tayi tace wa zaka rainawa hankali Kawai kace akan jiya nace ka bani dubu dari Zan canja waya sabo da mammako baza ka iya bani ba shi yasa ka kirkiri karya Wai kayanka sun nutse a ruwa just like that,heee Aslam tsabar son kudi ne yasa sai ka min karya Allah ya kyauta idan ba karya kake ba to tabbas kazo gidanmu da karya Ashe motoci da kudin daka nuna Mana ashe duk na karya ne dama ance samarin yanzu aron mota da gida suke bayan kwana biyu su karanta maka matsala shike nan ka shiga talauci tana Gama fada ta juya ta koma ciki abinta,shi ta daina daga Masa hankali ma ba ta ita yake ba yanzu ta kudinsa yake Yi,Ya kalli Siyama da damuwa yace baza ki gane ba Siyama amma Dan kasuwa shi Ina karanta Masa zai Gane,Siyama tace na fahimta ma wlh ubangiji Allah ya mayar maka da mafi Alkhairi Allah yasa ka samu Wanda Suka fi Wanda kayi asara Allah Kuma ya Kare gaba wlh da ace Ina da kudi da na taimaka nima,kallonta yayi yace karki damu na gode

A ranar ya sallami me gadi yace Isa baka min komai ba ga salary dinka na wata biyu ka tafi gida Zan nemeka,Isa yace Sir fatan ba wani laifi nayi ba dan Allah karka kore ni yace ba laifin komai idan na samu yanda nake so Zan kiraka a waya,Isa ba a son ransa ba ya tafi,ya Kira Daya me aikin itama Bara'atu ya sallameta yace nan gaba zai kirata itama tana takaici ta tafi.
Washe gari Siyama ya samu tana girki ya Bata dubu sittin cash yace gashi na wannan watan da watan gaba kije gida domin nan da sati ma'aikatan banki zasu iya zuwa su kore mu daga gidan Nan,Charity tace bazan karbi ko kwandala ba Sir na bar maka ka rike Kuma bazan bar gidan Nan ba sai ranar da Yan bank Suka zo Zan biku naga gidan da kace zaka Kama haya idan naga gidan sai na koma gida Zan dinga zuwa lokaci lokaci Ina dubaku kayi hakuri da kawata kaddara ce da Jarabawar rayuwa ka Zama me tawakali kasa Allah a ranka Inshaallah shi zai taimakeka,Murmushi yayi cikin dacin zuciya yace ba damuwa,Mamansa ya Kira a waya itama da kudinsa take gadara duk da cewa a wajen Yayarta take zaune a turai,Zuciyar Mum dinsa ta kusa bugawa da taji irin bala'in daya tunkaro danta musamman da ya fada Mata halin Nusaiba abinda take Masa,itama Mum hakuri take bashi akan halin Mata tace sai yayi hakuri dole,tana so ta taho Nigeria yace Kar tazo idan tazo ma wahala zata Sha gwara tayi zamanta Kawai ta tayashi da Addua,Mum har kuka tayi danta ya samu karayar arziki taje tana bawa Yar uwarta labari.
Tun daga Sanda Nusaiba ta tabbatar Aslam ya talauce kudinta na accnt da shi take kwasa ta fita yawon shakatawarta ya sallami driver dinsa ma duk da cewar ma'aikatan bank din Basu zo ba tukun a taxi take fita tunda bata iya mota ba,Siyama ce ke Masa girki,yau ma tun safe bai karya ba ya fita akan matsalar data fada masa.
Chapter 10 · 0% Book details