← Book details Auren Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 52 OF 56

Sashe 52

Auren Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Suna compound na gidan Aslam sai ga motar Aslam ta shigo ya dawo, door bell Nusaiba ta danna amma Siyama tasa an hanata yin kara,knocking tayi Allah yasa tana kitchen ta fito tace Baby tare da bude kofa ai Kuwa Ihsan ta washe baki tace irin Yan Novels,dariya ta basu Siyama tace kune a gidan ku shigo suka shiga kamshi da sanyi Yana dukan su,Siyama tace yau an tuna da kawancen kenan? Nusaiba tace uhm zuwa nayi mijinki ya yafe min ko na samu hakkinsa ya daina bibiyata na samu mijin aure,Siyama tace Inshaallah ma ya yafe Miki Nusaiba,Duniya kenan Wai Nusaiba ce yau ke neman Yafiyar wani,bana son Iskanci tunda kin aure shi da shegen munafuncinki da kutungwila ai sai ki kyaleni,Dariya Siyama tayi tace kece Kika yiwa kanki fa Nusaiba babu laifina,Nusaiba tana dariya tace da laifinki Mana tunda kece kike kula da shi idan ba shishigi ba Ina ruwan Yar aiki da kula da mijin matar gida,to ita matar wa yace tayi wasarere da mijinta,Kinga mu ki kawo mana kayan dadi muci karki dame mu cewar Nusaiba,Siyama ta kawo musu abubuwan ci da sha sai lokacin Aslam ya turo kofa tare da shigowa,Siyama ta mike taje tana Masa oyoyo oyoyo harda Masa kirari ga hantsi leka gidajen kowa,me karya icen dawa sai giwa,hadarin sama zo da jido ko tsawa,angon Siyama Oga yazo, Kaine da gidan Kaine da dakin, bakaki me karya gada,ko su bi ko suki sai dai su bari, abi oga a zauna lafiya,Oga karya kafafun arna,aje gari ya jima sai kwarya,sunyi bakar tafiya ka kayar,Dan asali kuji babban suna,sai an Kai su tasha ko sunki,dariya yakeyi shi mamaki ma Aslam yake sai kace wata Yar tauri yanda ta iya kirari kamar me Waka kullum da Kalar da take Masa ba irin na baya ba Indai tana nishadi to zai Sha kirari sai dai ya tsaya Yana kallonta Kuma wani Dadi yake ji sai yaji Kansa yayi wani gingiringim, rungumeta yayi tana dariya itama hannunsa ta rike ta kaishi ya zauna ta kalli Nusaiba da Ihsan Wanda Suka zuba musu Ido suna Shan kallo Siyama tace ga Sadauki ku gaida shi,Sadauki Aslam shi Kuma an murtuke Fuska ba raini,Nusaiba tace Ina yini wani kallon banza ya Mata da kyar yace lfy,Ihsan Kuwa tana gaida shi ya amsa da fara'a yace ya school tace Alhmdllh,Siyama tace wannan ba karatu take ba na Santa har gidan kawarta take tafiya karatun Novel soyayya ta sani Kawai,Ihsan tayi dariya Nusaiba tace ta ya Kika sani? tace ni da tayi a gabana naje gidan kawata ce yayar kawar Ihsan basu San Ina wajen ba in Banda zancen aure ba abinda sukeyi wallahi ku aurar da ita da wuri Ihsan Nema take ta lalace,Ihsan Fuska ta boye tana Jin kunya a hankali tace ai Ina da saurayina,Aslam yace ae lallai da gaske ne,Siyama tace kaji ko Baby na fada muku,bakya so kiyi karatu me zurfi? Aslam ya tambaya,tace ai yace zai biya min a gidansa sai nayi a can dakin mijina,dariya ta Kama Aslam Wai dakin mijjnta,Yace to Masha Allah,Nusaiba ce ta katse hirar tace Siyama tana mintsinawa Siyama Ido Wai ta yiwa Aslam magana,Siyama tace Sadaukina Nusaiba fa zuwa tayi ka yafe mata abinda tayi maka shi Kawai take bukata,ke dan Allah saurara karki min wannan zancen bana so ya mike ya haura sama abinsa ya barsu,Siyama tace tab akwai aiki,yanzu abinda za ayi Zan ta rokar Miki shi Inshaallah zai hakura,Nusaiba jikinta yayi sanyi tace dan Allah ki taimaka Kawata,Siyama tace karki damu,Nusaiba tace Bari mu tafi Kar Mama tayi Mana fada kin San yanzu Mama an San annabi ya faku,dariya Suka yi Siyama tace Ina zuwa ta haura sama da sauri ta shiga bedroom ta samu Aslam ya tube zai shiga wanka yaga ta bude akwati tana eban turaruka da kayan make up ya kalleta yace Ina Zaki Kai su? tace Nusaiba Zan bawa,yace bada abinda na siya ba zube yaje ya kwace kayan ya maida akwati ya kulle abinsa,Siyama ta Bata rai tace to ka bani kudi na basu kudin mota,yace badai kudina ba Indai Nusaiba ce baza ta sake cin kwandala ta ba har abada,Wai mene Haka Baby ai ni zaka bawa na basu ba wai Kai ka basu ba,bazan bayar ba bana son musu,tace fine ai na tuna Ina da abubuwan da Aunty ta kawo min tsaraba ban saka ba ai wannan Nawa ne ba naka ba,ta dakko Abaya masu kyan gaske blue da black kala biyu ta zuba a Leda da turaren da aka bata tsaraba sai sabulai,Aslam yace wannan kayan da nace Zaki saka min su sunyi kyau su Zaki bayar baki Isa ba kokawa Suka Fara tace ciki ne dani maza ka zubar da cikin,yace zanyi fushi,Siyama tace ka Dade baka yi fushi ba kayi,to shikenan tunda ban Isa dake ba sai na kunyata ki,zai fito wajen su Nusaiba ya disgata tasa key ta baya ta kulleshi a dakin ta fito abinta ta basu suna ta godiya,Nusaiba tace mu dai zuba Mana snacks din nan a Leda mu tafi ya min Dadi,Siyama ta juye musu a wata ledar da lemuka sun Kai biyar suka tafi da Kaya niki niki sai da ta rakasu sannan ta dawo ta bude kofar Aslam yayi Fushi sosai bai san har snacks da lemukansa an basu ba,itama Siyama bata kulashi ba tace kuma ga kayan lefenka nan tunda dama ba ni ka mallakawa ba halak malak mene amfaninsu ban Isa nayi iko da kayana ba.

Yana shafa lotion bai kulata ba Wai fushi yake,ya fito ba snacks din da tayi a kitchen gaba daya Yana so zaici babu,ta dawo Palo tana kwashe kwanika yace ke Ina snacks din? tace na hada musu da shi,yace flour tawa da na siyo da kudina,Siyama tace harda lemuka sunfi biyar idan kaga dama ka fashe sabo da fushi,kwafa yaja ya mike zai bar gidan tace wlh kana cin abinci a waje sai anyita dani zaka ga makirci idan baka sani ba ka sani makira ce ni ta karshe,dariya ta bashi yace to shike nan ki nuna min makircin naki na gani ya juya zai fita ta Sha gabansa tace hmm muje bedroom idan ka min service sai ka wuce dan tani ka cinye ma harda kujerun restaurant din,yace ai ke ba kunya ce dake ba dama can,tace ae naji a haka aka gani aka ce ana so,ke har kina da bakin magana matar data dinga kuka a kaina idan ba a baki ni ba sai kin haukace, Kai ba a sirri da Kai Siyama ta furta tayi mukus,bakya Jin magana Siyama kin rainani koshi ya Miki yawa in Kika sake sai na Miki ta Abba Shehu da Mama na hanaki abinci,Dariya Suka Yi tace ai nasan baza ka iya ba, wash ka tuna min da dadinka muje ta riga shi yin sama harda Yi Masa dan Kira sai kace karuwa dole sai da ta sashi dariyar dole ya bita ba shiri,abinci ta kawo Masa yaci ya koshi sannan Suka fara shagali.

Raudah yau ta koma aikinta ta riga Affan dawowa gidan ta gyara a gurguje tayi wanka ta cakare sannan tana girkinta tasan gaf yake da dawowa, Landlady ta dakko Shehu a dankareriyar motarta Suka zo gidan Rauda Shehu an faso gari an auri me kudi motocin Landlady ma har ya koya shi Kansa driving yake ya fita inda yaga dama da motar, Mama Kuwa sati biyu kenan Shehu ko dakinta bai kalla ba tunda ta dawo,abin Yana Mata ciwo tana gidan amma bai taba lekota ba sai da ta shafe sati biyu,tana dai ta Shan gyaran jikinta,gashi ta dawo birni tayi kiba tayi haske ta murje,sai gayu take yi.
Har landlady tazo da mijinta Suka Sha hira Affan bai dawo ba gashi wayarsa bata shiga,hankalin Raudah ya tashi,bayan sunyi Sallar magriba Suka tafi ba tare da Affan ya dawo ba,Rauda tayi Sallar Isha ta zuba tagumi taji karar motarsa,da sauri ta mike ta fito taga shine ya fito ras da shi, dama yasan shi take jira hankalinta sai ya tashi,kankame shi tayi tana murna tace Allah na gode maka daka dawo min da mijina gida lafiya,Murmushi yayi yace kiyi hakuri aikine ban gama ba munyi baki gashi wayata haka kawai naga ta dauke ta mutu duf,tace okay shi yasa naji shuru ya rike hannunta Suka Shiga ciki,wanka ya shiga ta bude toilet din ta Shiga ta dakko ribbon dinta zata fito yace zo nan My Sugar, tana zuwa ya jawota ciki ya cire Mata Kaya Suka yi wankan tare,Towel din ya daura ya jawota ya bude ya sata itama a cikin towel din nasa guda daya tal Suka daura su biyu sai rike towel din yayi bazai dauru ba tana manne a jikinsa suka fito suna tafiya Kamar masu ciwon kafafu suna dariya bayan sun shirya tace yau Ina da wani labari me dadi amma muje Dining Suka fito yaga abinci na musamman kala kala an Masa yace na mene haka tace nasan baza ka iya guessing ba,wata takarda ta Mika masa tana Murmushi tace read,karantawa yayi bakinsa yaki rufewa ya wani saki dariya ta farin ciki ya duka a wajen yayi sujjudulshukur ya mike yace My Sugar You are pregnant for 3mnths oh my God dana Yana cikin mahaifarki,tace kasan kwana biyu Ina zazzabi da tashin zuciya shine na biya asibiti daga wajen aiki aka min test gashi Ina da ciki,ka kusa Zama Daddy rungumeta yayi yace dole muyi celebration yau, kissing dinta ya shiga Yi kamar me sannan ya zauna a kujera itama taja ta zauna ya sake rungumota jikinsa Yana cewa Zan iya Kuwa cin abincin nan yanzu murna zata barni Kuwa,ai yau Zan fadawa Yaya Yusuf,Raudah tana ta kallon yanda yake murna itama haka,tun daga ranar Affan kullum kafin ya fita sai ya Dora bakinsa a cikin ya kwararawa dansa Addua sannan yace Baby Daddy zai fita a Mana addua idan ya dawo ma haka sai yayi Masa addua yace Daddy ya dawo,Raudah Kuwa yanda take ji da cikin nan nata Kamar kwai.
Chapter 52 · 0% Book details