← Book details Auren Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 56

Sashe 23

Auren Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Aslam kuwa suna tafiya Sabeer yace zamuje park din? da masifa ya furta ka kaini gida Malam Babu Maganar park din banza kaini gida gwara nayi tunani me kyau na huta,ka fasa zuw...bazan je ba karka dameni ya furta da masifa,Sabeer yace kaga nifa bani naje zance wajen Yarinyar Nan ba bare kace,to ni nace maka naji haushinta ne Ina ruwana ta kula maza dubu ma Ina ruwana,Sabeer dariya kawai yayi Yana tukinsa yace tana da saurayinta kana ganinsa dai sharr da shi gwara ka auri Nabeela, Allah ya kiyaye na auri sakin wawa Nima fa sakin wawan nayiwa wata nasan me tayiwa mijinta ya saketa ba duk bazawara ce ta kirki ba gwara wacce ma mijinta ya mutu amma Wanda ake sakowa na tsorata da su wa yasan me Suka aikata aka sake su,Sabeer yace wallahi akwai Wanda laifin mazajensu ne,Aslam yace ae naji naji bana so bata min ba ni da wata kafarta a gwame,nufinka idan ta sa min riga da wando haka Zan na ganin Ball leg dinta sun kantare,Sabeer dariya Kamar me yace yaushe kaga kafafunta maye yanzu har ka San tana da Ball leg? Kwarai kuwa ko zaka ce karya ne? Sabeer yace tabbas wlh ba musu lallai mutumin auren Nusaiba ya sake gogar dakai da ko kallon Mata baka yi,Aslam yace dan Allah ka kyaleni bana son surutun me gwamammiyar kafa dai bana Yi karka sake min zancenta ana Neman macen kirki kana kawo min bage,Sabeer yace sorry na Siyama yana dariya,ance maka son Siyama nake Yi wai nifa ban shirya aure ba ku sani ma ya furta Yana turo jajayen lips dinsa yace kaini wajen Mum ma gwara na ga uwata na huta da duk wata ya mace.
Wajen Mum suka tafi can Suka zauna har dare Mum har ta Fara damun Aslam cewar ka Nemo Mata ta gari Aslam gashi ma Kai naga Kamar baka da niyya Wanda hakan hatsari ne ga duk namijin da ya taba aure bai dace ya zauna ba Mata ba ka dinga dubawa kaji,to Aslam yace kawai.

Affan kuwa akan idon Raudat ya shigo da motarsa gidan tana tsaye ta juya baya ita da Landlady suna hira ya wuce da mota abinsa Yana yin parking ya fito Raudat tana kallon inda yake fitowa,part dinsa ya Shiga da sauri,Raudat ta sauke ajiyar zuciya ta Shige part dinta ita ma,ai tana Shiga ciki taji suna tafawa da Sayyeed suna magana Affan yace Kai Kuma wannan tarkacen flask din da tire Ina ka samo su? Sayyeed yace ai baka sani ba budurwa nayi Raudat ce ta dinga Miko min ta window ashe windown ku daya, Affan yayi dariya yace Kai dalla ba sonka takeyi ba mutunci ne da ita Haka take da kirki ita tana ma da mijinta matar wani ce aiki ya kawota weekend take komawa gidanta, Sayyeed ya zaci da gaske ne yace eyya na hakura gwara da ka fada min,ai Kuwa tana da kirki kalli girki ya shiga budewa Affan Yana kallo,yace ta hutar Dani dama da tunaninka na dawo na nema maka abinci,Raudat tana jinsu suka hau Hira Sayyeed har yayi wanka Affan yace ko zamu fasa gari ne?Raudat ta Riga su fitowa ta tsaya kamar zata Shiga motarta,Affan ya fito tare da Sayyeed,Affan yace Hajiya Aunty fita zakiyi ne? Tace ae Ina son fita amma bana son driving din na gaji,Affan yace muje to Mana na kaiki ni Naga yanda Kika karrama abokina na gode fa,Hmm ba komai cewar Raudat zata Shiga Bayan motar Affan yace shigo gaba Sayyeed sai ya Shiga baya shi,Sayyeed ya Bude baki matar wani Kuma Affan yace Kawai dai Sayyeed ya Shiga Bayan mota,Affan ya tashi mota Suka wuce Raudat bata San inda zata je ba,Affan yace Ina za a kaiki? tunawa tayi da wata kawarta da suke aiki waje daya wata Hafsat ta nuna Masa gidan har ya kaita kofar gidan Hafsa yace yaushe za a zo a daukeki? Raudat tace sai 10pm,Affan ya zaro Ido yace haka Kawai ki zauna a gidan wata matar tana da aure fa har goman dare ki takura musu idan mijinta Yana son yayi Yar harka fa gaskiya bai dace ba,Raudat tana dariya tace to karfe nawa Zaka dawo? Yace gaskiya 8pm Haba kina mace a dinga sakaki dake bazai yuwu ba,To sai ka dawo cewar Raudat yace yawwa 8pm ki shirya har ta juya yace Aunty ta juyo da sauri yace ba ruwanki da mijinta sawunki a likkafa ki dauke idonki dan mazan yanzu ba mutunci gare su ba wlh sai yace Yana sonki ato ki kula Kar azo kawa ta nada Miki duka a gidanta irinku Aunty sai kusa mijin wata ya kifa yaci ta ka,Dariya Raudat keyi yace gaskiya nake fada Miki ki Kama kanki ba ruwanki da mazan wasu,Raudat tace to sai dai ka dawo ta juya ta Shige tana dariya,Affan sai da ya daina ganinta sannan yace da Sayyeed Kai katon gardi dawo gaba Kuma wallahi karka sake muna kwance ko yatsanka ya taba min fatata nasan baka iya kwanciya ba na tsani jikin Namiji ya taba Ni da ace dai macece aha wannan is okay Sayyeed ya koma gaba yace nasan halinka ni a Palo ma Zan kwana Kuma kaji tsoron Allah kana kula matar wani,Affan yace ai mun Saba da ita, Sayyeed yace naga alama dalla karka Raina min hankali let's go,Suka tafi yawonsu.

Tun kafin 8pm Suka koma gida da kayan ciye ciyensu ya bar Sayyeed ya sake zuba wankan 3qtr da riga me gajeren hannu farare ya tafi dakko Raudat,8pm dot yayi horn dit dit Raudat taji ta shirya tare da yiwa Hafsat Sallama,Hafsat ta rakota tare da mijinta har mota ta Mika Mata turarukan wuta masu kyau a Leda,Affan ya kalli Raudat kadan ya juya da mota Suka hau kwalta sannan yace mijinta har da rakiya Ina ruwansa dake Kai wasu mazan ma Sai a barsu gaba Daya wasu rako Suka yo,Raudat ana ta Jin dadi har da narkewa a jikin mota taki magana ta rasa yanda zata Yi sabo da murna,yace naji kinyi shuru? Raudat ana wani tararrabewa an samu waje tace kaina ke min ciwo a ranta tana istingifari da karyar da ta shararo, Sannu ya furta tace yawwa,yace a tsaya a siya Miki paracetamol? No ta furta Ina da shi a gida yace sai a kyaleki kina cuta Kuma, yayi parking bakin wani chemist ya shiga ya siyo Mata paracetamol da ruwan roba ya dawo dauke da Leda a hannu daya hannun a aljihu Yana taku dai dai yana zuwa ya Mika Mata yace Sha,ai Raudat tabara ta fara tace bana son magani Allah,yace ashe Kuwa baza mu koma gida ba a nan zamu zauna harda gyara parking,farin ciki yasa Raudat ta Kara narkewa tace please kayi hakuri,Affan tsigar jikinsa tashi takeyi idan tana Masa Shagwabar nan tana tuna Masa da Nabeela,Murfin robar ruwan ya balle ya balli paracetamol biyu ya zuba a cikin murfin ya dan zuba ruwa ya wani narka maganin sai kace zai bawa dan yaye yace tsaya na baki to Yana kallonta,sabo da shine zai bata kalau take amma tace to tayi wani kasa da kai lagaf, Hannu yasa tare da dago kanta a hankali harda cewa haa ta bude ya zuba Mata ta shanye ji tayi kamar ta Sha alawa sabo da shi ya bata, ruwa ya bata a baki ta shanye abinta ta wani kwanta a saman kujera Yana cewa sannu yaki tashin mota sai data kwashe 30mnt tace naji sauki har na daina ji sannan ya yiwa motarsa key

yace me kike son ci? tace Ice cream ai Kuwa ya tsaya ya siya Mata wata katuwar roba guda biyu da su yogourt me sanyi ya dawo ya leko ta windown ta yace abinci fa ranki ya dade Hajiya Aunty? tace naci a wajen Hafsat,duk da haka sai da ya siyo Mata tsire lafiyayye sannan ya shiga mota Suka tafi, ana tafiya tana Shan ice cream dinta Yana driving yace ni bazan Sha ba? tace Sorry gashi yace tuki nake ai tace to sai munje gida,yace ki bani a Baki ,Ido Raudat ta zaro taji kunya tace bazan iya ba,yace kaji locality me nake ji ba dadi haka sai kace wani suna Siyama,dariya tayi taki bashi bai ce komai ba har ya kawota gida tayi godiya ta wuce part dinta shima ya shige wajen Sayyeed,tana zuwa tayi sufa akan gadonta tana tsalle da murna.
Chapter 23 · 0% Book details