Sashe 51
Auren Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Kawu Mama ya samu yace ki godewa Allah Aslam yayi Miki rana Wanda duk duniya babu me miki irinta ya sa Shehu zai maida ke dakinki amma yace ki koma Kauye zai Miki magana da Kansa,Mama ta fashe da kukan farin ciki tace dan Allah ku barni a nan ku taimakeni Kauye wahala inda kasan Ina cikin wuta,Kawu yace ai yace Indai a nan kika zauna bazai dawo Dake ba ai da sauri Mama ta Fara tattara kayanta zata tafi kauyen nasu haka,Kawu yaji tausayinta amma gwara ta Sha wahala sosai yanda ko ance ta sake yin wani abin baza tayi ba,Haka ta koma Kauye taci gaba da Shan bakar wahala a gidansu tunda ba iyaye ne da ita ba a gidan Yan Uwa ne Kuma Yan uwansu kaf basu da mutunci kowa dan iskan Kansa ne kudi Kawai shine mutuncinka a idon su,Gashi idan tana so ma a San Mata abincin sai taje anyi aiki da ita a gidan surfe da daka sai tayi dole,hannun Mama yayi kanta yayi kaushi sabo da wahala,gashi Shehu Shuru har ta sake yin wata guda a kauyen su Nusaiba sai rokonsa suke Yi har kuka sai da Suka yiwa Shehu sabo da Ameer yaje yaga halin da mahaifiyarsu take ciki,Shehu sai lokacin ya nemi yan uwan Mama maza Suka Yi magana za a sake maida aure sabo da ta gama Idda tuni,bata sani bama sai Yan uwanta ne Suka sanar Mata an maida Aurenta da Shehu,Zabura Mama tayi gwanin tausayi tace yazo ne? Yace ae yazo ya koma ma yace idan kin shirya ko yaushe zaki iya tarewa a dakinki,Mama tace yau Zan koma ai tsofaffin gidan Mata Suka ce ai Kya tsaya dai ki gyara jikinki,Suka hana Mama Sai lokacin suke bata abinci ishashe sabo da sunji taci gaba zata koma birni lokacin abinci sai ta ture,har kyautar Sabulai da su Omo suke bata Kuma ta daina taya su aiki amma abinci sai ta ture,kowacce sai ta bata kyautar magungunan Mata na gyara jiki,Mama sabo da an Mata kishiya ta dage da Sha tana ta gyara kanta bata aiki kaushin Hannu duk ya gudu babu tayi Yar kibarta da haske,sai da tayi gyaran sosai sannan ta shirya wasu dattijai su biyu Suka rakota gidan mijinta,Yaranta sai rungumeta da murna Kamar me,Su dai dattijai suna kawota Suka koma Kauye abinsu,Yaran Mama sun zagayeta suna ta murna yau sun rasa inda zasu saka kansu,Nusaiba ce ta kawo Mata abinci a plate da cokali harda siyo Mata lemo, Mama ta bude abincin ta ga shinkafa da Miya da nama harda salat,Mama yaushe rabo tace haka kuka ci gaba a rayuwa? Nusaiba tayi dariya tace Mama ai yanzu Abba abinda muke so muke dafawa,haka yake cewa mu zabi abinda muke so,Ameer yace kinga shagon Abba da kasuwancinsa ya bunkasa sosai, Mashaallah cewar Mama ta Fara antaya loma sai da taga bayan abincin nan tas,Nusaiba tace a Karo miki? tace na koshi Alhmdllh,duk da haka Nusaiba sai da ta tsamo Mata nama a tukunya kusan guda goma tace Mama cinye nasan yanzu kina yiwa mutum baki ko tsinuwa zata Kama mutum sabo da rashin cin nama akwai dafi me zafi yanzu a yawunki,Mama tayi dariya tace sai ku kuka da kanku amma ai kullum Albarka nake saka muku ko laifi kuka min naji haushi a bayan idon ku sai nace na yafe muku Allah ya muku albarka,Nusaiba tace badan Aslam ba shike nan Mama baza ki dawo ba,Mama tace ke dai bari Naga rayuwa yanzu fatana ki samu miji ko talaka ne, ameen cewar Nusaiba zanje Nima na nemi gafarar Aslam da Sufyan.
Shehu dai a ranar ma Mama bata ganshi ba haka ta kwana ita kadai,washe gari da Yamma Nusaiba ta shirya ita da Ihsan kanwarta ta rakata Suka Fara zuwa gidan Sufyan sun ci sa'a Yana gida dake weekend ne,shima matarsa tana da ciki,matar bata San su waye ba ta sauke su cikin mutuntuwa Nusaiba sai kallon gidan takeyi komai an zuba sabo,Sufyan ne ya fito ya ga Nusaiba abinka da so,Sufyan gangariyar so yayiwa Nusaiba tsakani da Allah bai wani bata Fuska ba tunda yasan shima Yana da laifi tana da aure ya dinga soyayya da ita,gaisawa Suka yi tace zuwa nayi na baka hakuri ka yafe min abinda nayi maka,Yace oh ba damuwa na yafe Miki Nima ki yafe min munyi kuskure Allah ya yafe mana,tace na gode ta mike zasu tafi ya bata 5k taki karba sai Ihsan ya bawa ita Kuwa ta karbe Suka wuce gidan Aslam
Tunda tazo bakin gate ta Fara hawaye ta tuna haukar da tayi da wannan gidanta ne ta cuci kanta,Ihsan tace Aunty kiyi hakuri haka kin Riga kin cuci kanki Siyama ta Shige gidan kunyi change kawa da kawa Kun auri miji daya haka Allah ya rubuta sai kin Fara Shiga gidan itama gashi tazo ta Shige ta fiki wayo da Imani Aurenku Aunty kawaye ko wacce ta dandani zumar Mijin Daya shike nan 50-50,Nusaiba tace yau na shiga Uku ubanki Ihsan wato har kinyi girman da Kika San mene zumar maza zanci Ubanki wallahi sai na fadawa Abba yaci ubanki wato Yar iska kike so ki dawo,Nima fa Aunty na Isa auren nan wlh 18yrs fa komai na hada wlh ina samun miji aure zanyi ni dai,gashi nan a novel nake Jin soyayya idan Muna karantawa a makaranta a Wayar wasu friends, writers da basa tsaftace alkalaminsu wani ka rantse Bf kake kallo,Nusaiba tace ai wasu na daya daga cikin Wanda suke gurbatawa Yara tarbiyya komai fada akeyi gatsal batsa tun farko har karshen novel yawanci ma yaran Mata sunfi manyan matan karatun novels,Allah ya shirya yasa su gane su gyara alkalaminsu wajen rubutu sabo da tarbiyyar yaranmu masu tasowa gaba,Ihsan tace to Aunty da dadi auren? Baki Nusaiba ta bude tace ke in kina da saurayi ki fito da shi gwara a Miki auren nan, Ihsan tace Ina da abina,dariya ta bawa Nusaiba suna rike da hannun juna tace waye? tace Mahmoud wani yayan kawata ne manager ne a bank baki ganshi ba Aunty ya hadu mugun sona yake kin San na fiki haske duk gidanmu nice ziza haka yake ce min Zizata,Nusaiba tace ba karya Ihsan na yarda to kice ya dinga zuwa zance,tace dama ce Masa nayi Kar yazo Abba zai dukeni,kice yazo kina yin candy sai a daura mu Sha biki,Murna Ihsan take yi writers sun ruda yarinya da soyayya.
Shehu dai a ranar ma Mama bata ganshi ba haka ta kwana ita kadai,washe gari da Yamma Nusaiba ta shirya ita da Ihsan kanwarta ta rakata Suka Fara zuwa gidan Sufyan sun ci sa'a Yana gida dake weekend ne,shima matarsa tana da ciki,matar bata San su waye ba ta sauke su cikin mutuntuwa Nusaiba sai kallon gidan takeyi komai an zuba sabo,Sufyan ne ya fito ya ga Nusaiba abinka da so,Sufyan gangariyar so yayiwa Nusaiba tsakani da Allah bai wani bata Fuska ba tunda yasan shima Yana da laifi tana da aure ya dinga soyayya da ita,gaisawa Suka yi tace zuwa nayi na baka hakuri ka yafe min abinda nayi maka,Yace oh ba damuwa na yafe Miki Nima ki yafe min munyi kuskure Allah ya yafe mana,tace na gode ta mike zasu tafi ya bata 5k taki karba sai Ihsan ya bawa ita Kuwa ta karbe Suka wuce gidan Aslam
Tunda tazo bakin gate ta Fara hawaye ta tuna haukar da tayi da wannan gidanta ne ta cuci kanta,Ihsan tace Aunty kiyi hakuri haka kin Riga kin cuci kanki Siyama ta Shige gidan kunyi change kawa da kawa Kun auri miji daya haka Allah ya rubuta sai kin Fara Shiga gidan itama gashi tazo ta Shige ta fiki wayo da Imani Aurenku Aunty kawaye ko wacce ta dandani zumar Mijin Daya shike nan 50-50,Nusaiba tace yau na shiga Uku ubanki Ihsan wato har kinyi girman da Kika San mene zumar maza zanci Ubanki wallahi sai na fadawa Abba yaci ubanki wato Yar iska kike so ki dawo,Nima fa Aunty na Isa auren nan wlh 18yrs fa komai na hada wlh ina samun miji aure zanyi ni dai,gashi nan a novel nake Jin soyayya idan Muna karantawa a makaranta a Wayar wasu friends, writers da basa tsaftace alkalaminsu wani ka rantse Bf kake kallo,Nusaiba tace ai wasu na daya daga cikin Wanda suke gurbatawa Yara tarbiyya komai fada akeyi gatsal batsa tun farko har karshen novel yawanci ma yaran Mata sunfi manyan matan karatun novels,Allah ya shirya yasa su gane su gyara alkalaminsu wajen rubutu sabo da tarbiyyar yaranmu masu tasowa gaba,Ihsan tace to Aunty da dadi auren? Baki Nusaiba ta bude tace ke in kina da saurayi ki fito da shi gwara a Miki auren nan, Ihsan tace Ina da abina,dariya ta bawa Nusaiba suna rike da hannun juna tace waye? tace Mahmoud wani yayan kawata ne manager ne a bank baki ganshi ba Aunty ya hadu mugun sona yake kin San na fiki haske duk gidanmu nice ziza haka yake ce min Zizata,Nusaiba tace ba karya Ihsan na yarda to kice ya dinga zuwa zance,tace dama ce Masa nayi Kar yazo Abba zai dukeni,kice yazo kina yin candy sai a daura mu Sha biki,Murna Ihsan take yi writers sun ruda yarinya da soyayya.