Sashe 34
Auren Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Period din Siyama kwana hudu take yi yau ta cika 4days amma bata fadawa Aslam ba gudun Kar ya dameta da zumudi,Yana hutun amarcinsa ya Kira Yaronsa a wajen aiki Yana fada taya za ayi baka rubuta abinda nace ba har yanzu baka tura min ba,Naga alama tunda naji labarin kayi aure Sam baka kula da aikinka Wasa kake Yi,Watarana ma baka zuwa sam idan baka bukatar aikin ka fada min Zan iya sallamarka,Hakuri ya dinga bawa Aslam yace anjima da yamma zan shiga Office din kazo mu hadu a can yace an Gama oga
Zuwa yamma ya shirya cikin Riga Armless da 3qtr me fadi sky and white ya Sha kyau,Siyama ta fito zata rakashi tana Fushi Wai dole sai ya tafi da ita,yace kiyi hakuri yanzu Zan dawo ba lalle ma nayi 1hrs ba,tana shagwaba tace to sai ka dawo Allah ya tsare ta Bude Masa mota ya shiga,ya daga mata Hannu sannan yayi driving Kansa zuwa Office dinsa.
Nusaiba ce ta Kira mijinta tace Ina Kan hanyar gida,Sufyan yace jeki Office dina ki jirani idan na zo sai mu taho tare bazan iya barin matata tana yawo a Napep ba,Nusaiba tace kamata ai ma bai kamata ba babu tsari ace Ina shiga Napep, taci gayu na gaske cikin tsadajiyar shadda Blueblack doguwar riga,Address ya tura Mata na Building din ta wuce can,tana zuwa kowa kallon dai dai take Masa Sabo da mijinta ne C.E.O a wajen sai yanga tana uban gadara ta haura sama a lift tana dubawa ba tare da ta tambayi kowa ba lokacin ma ma'aikatan gaba Daya suna ta tafiya sun tashi 5pm tayi sai daidaiku suma Kuma Shirin tafiya suke yi,tana Bude office kowanne a kulle da key Kuma tafi karfin ta tambaya sai kace na ubanta,tana zuwa hawa na uku taga wani hadadden Office na musamman tace ga na mijina nasan ma nan ne tana murdawa taji ya bude ta Shiga,haduwar Office din ta Kai haduwa sanyi da kamshi ke tashi kawai komai unique ne a Office din,kujera ta samu ta zauna tana jiransa sai kallon Office din takeyi tana Jin dadi yanzu nan na mijinta ne,Aslam ne ya fito daga wani daki a cikin Office da wani cup a hannunsa,yayi mamaki ganin Nusaiba tana zaune,Fuska ya daure itama ta daure Fuska a ranta tace oh a nan aka dauke shi aiki mijina ne ya dauke shi ashe me shara da gogeg goge ne Alhmdllh zai ga wulakancin duniya,kallon up and down take Masa sai yace ranki ya dade me kike bukata? tana harararsa tace Office din mijina nazo kaga Mallam dalla kawo min lemo Kai baka iya kula da bakin oganka ba ta ja tsaki,Aslam ya kalleta tare da furta Sorry Hajiya ya shiga inda aka tanada wajen da yake zuba kayan coffee dinsa,tea da lemuka,ya bude fridge tare da dakko wani lemo me mugun tsada ya dakko ya kawo gabanta tace zuba min mana Yana tausayinta a ransa ya zuba Mata tare da Mika Mata ta karba tana Masa kallon banza ta Sha lemon tana tunani a ranta lallai lemon nan na musamman ne,ta sake cewa I wonder har yanzu wani kamshi yake me Dadi ya fa kamata mutumin nan talauci yasa aji Yana wari amma kullum fes da shi,wani kyau ma yake da kiba,muryarsa taji yace shike nan abinda kike bukata? Wani kallon banza tayi Masa ta ja tsaki tace kaga karka tsaya min a kai ci gaba da share sharenka....kafin ta rufe baki Sufyan ya shigo da sauri Yana zuwa gaban Aslam ya rusuna tare da furta dan Allah kayi hakuri Sir wallahi abubuwa ne Suka Sha kaina kayi hakuri dan Allah wallahi na manta shaf amma Zan rubuta anjima kadan na tura maka,Aslam yace kayi sauri please Zan jira a gida ka tura min ta Email don't waste my time, Inshaallah Sir Inshaallah ,Nusaiba Ido ta zaro tana kallon ikon Allah amma duk da haka bata wannan take ba ita ya aka Yi Aslam yake da kudi kenan ba talaucewa yayi ba,Kai ta dafe Kamar zata yi kuka ta fara tunanin ta ya zata koma wajen tsohon mijinta mamaki Kuma ya kashe ta dama Sufyan yaron Aslam ne a karkashinsa yake aiki,Aslam Yana kallonta ransa a bace ya hade rai ya wuce ta gabanta zai wuce gida,Sufyan ya mikawa key yace ka rufe min Office ya fito,da sauri Sufyan ya ja hannun Nusaiba da tayi mutuwar zaune Suka fito ya rufe Office din suna Fitowa Suka samu Aslam ya Danna remote din mota tun daga nesa ya bude ta ya shiga,Nusaiba kallon motar takeyi tabbas itace Suka Zo a cikinta tare da Siyama,Kawai kallon ikon Allah takeyi,motar Sufyan ta kalla wata kucakar mota wani takaici ya lullube ta haka ta bishi Suka shiga sai gida,Aslam kuwa mamaki yake yi dama Sufyan ne ya auri Nusaiba amma take Masa iyayi,dariya yayi wani farin ciki ya kama shi tabbas yanzu yasan Nusaiba tana cikin wani hali, cike da farin ciki ya koma gida Siyama tana Palo Yana shigowa tazo ta fada jikinsa tana furta Oyoyo ya dagata sama Yana murna,tace wannan murnarfa? Ya Shiga bata labarin abinda ya faru tsakaninsa da Nusaiba ai Siyama har kasa ta durkusa da hannu biyu ta kwaso Shoki yayi dariya ta sake kwasowa tana waka da baki tace yau Nusaiba ba bacci Yar banza,mijin nata ma ashe yaron mu ne,na Kara maka farin ciki? Yace da me Yana Murmushi ya manna ta a kirjinsa tace yau Ina Sallah na gama period,Aslam harda ihun murna yace ai yanzu ba jiran wani dare ya dauketa Kamar jaririya sai bedroom dinsa Yana cewa first Evening zamuyi ba first night ba
Nusaiba Kuwa suna komawa bedroom Suka shiga shi Sufyan ma bai San matar Ogansa bace yace Wai lafiya Naga kin rasa sukuni sai gumi kike yi,Nusaiba mayafinta ta jefar ta zame dankwalinta ta jefar tana fifita da hannunta tana huci tace Aslam oganka tsohon mijina ne shine Wanda ka zuga ni na kaishi Kara ka zugani na karbi takardar sakina a hannunsa,Sufyan ya dora Hannu a Kai Yana wayyo Naga ta kaina Ogana ne na Shiga Uku aikina,Nusaiba tace wa yake ta wani aikinka yanzu ya fika kudi dama ashe da kudinsa,ya zanyi na Shiga dubu ma ba uku ba, gashi Siyama ta aure min miji ya zanyi,Sufyan baki ya bude yana kallon ikon Allah yace Ina ta aikina kina ta wani kudi baki da hankali Wai dama? Nusaiba tace dalla karka dameni mafitata nake hangowa,Sufyan mamaki ya kashe shi yace amma ke butulu ce baki San arziki ba,Iyayena nake hanawa ci da Sha sabo dake sabo da ke na kasa tara komai,Sai kayi Kuma cewar Nusaiba,sai nayi fa Kika ce? ta duro ashar tace burar.....kafin ta rufe baki mari taji ta ko ina,daina gani tayi na wani lokaci ya nade hannun riga ya hau jibgarta Kamar ya samu katon gardi tana ihu nan take idonta ya kakkafe ya juye numfashinta ya koma sama sama sai ta Fara furzo da jini ta bakinta amma Sufyan ko asibiti bai kaita ba sai da Allah ya taimaketa numfashinta ya dawo dai dai ta kasa tashi sabo da dukan data ci sai Jan jiki da Haka ta jingina jikin bed tana cewa ni ka sakeni wallahi wajen Tsohon mijina Zan koma ga me kudin gaske,Tsaki Sufyan ya ja sabo da zai iya kisan Kai ya fice ya barta a gidan tana ta tunanin kudin Aslam Yaya za ayi ta koma wajensa.
Affan kuwa kyale Raudah yayi sai da aka kwashe kwana uku ya tabbata ta huce sannan ya sameta a compound zata fita ya tareta yace Raudah ta,Baki ta turo gaba,yace my Life, Mene ta furta yace dan Allah kiyi hakuri,wa Zan so in bake ba,Ina nuna Miki cewar ke kadai nake da,kece kadai a zuciyata,ki rage kishin nan My life tsohuwar budurwata ce fa me zanyi da ita,Raudah tace sau Nawa kuke komawa wajen tsofaffin budurwarku kuce ai ita kuka Fara so baku mantawa da juna,Banda ni to Ni ai na baki labarin abinda Suka min ta ya Zan koma wajenta ai da na cika marar zuciya,Kiyi hakuri ba laifina bane,Raudah ta kalle shi tayi missing dinsa tace idan na sake ganin wata tazo wajenka duk abinda na maka Kai ka jiyo,Affan yace ae ki mare ni ma,Murmushi tayi tace ko da kudi ai ban iya marinka,key din motar ya karba yace muje na kaiki Office,Kar ka ja min a wajen aikin nan namu akwai Yan mata,ke Kam kishi ya Miki yawa,tace ya zama dole ai indai akanka ne,Key din ta kwace ta Shige mota tace da kaina zanje ta Shige mota taja ta tafi tana Murmushi tare da dago Masa Hannu.
Zuwa yamma ya shirya cikin Riga Armless da 3qtr me fadi sky and white ya Sha kyau,Siyama ta fito zata rakashi tana Fushi Wai dole sai ya tafi da ita,yace kiyi hakuri yanzu Zan dawo ba lalle ma nayi 1hrs ba,tana shagwaba tace to sai ka dawo Allah ya tsare ta Bude Masa mota ya shiga,ya daga mata Hannu sannan yayi driving Kansa zuwa Office dinsa.
Nusaiba ce ta Kira mijinta tace Ina Kan hanyar gida,Sufyan yace jeki Office dina ki jirani idan na zo sai mu taho tare bazan iya barin matata tana yawo a Napep ba,Nusaiba tace kamata ai ma bai kamata ba babu tsari ace Ina shiga Napep, taci gayu na gaske cikin tsadajiyar shadda Blueblack doguwar riga,Address ya tura Mata na Building din ta wuce can,tana zuwa kowa kallon dai dai take Masa Sabo da mijinta ne C.E.O a wajen sai yanga tana uban gadara ta haura sama a lift tana dubawa ba tare da ta tambayi kowa ba lokacin ma ma'aikatan gaba Daya suna ta tafiya sun tashi 5pm tayi sai daidaiku suma Kuma Shirin tafiya suke yi,tana Bude office kowanne a kulle da key Kuma tafi karfin ta tambaya sai kace na ubanta,tana zuwa hawa na uku taga wani hadadden Office na musamman tace ga na mijina nasan ma nan ne tana murdawa taji ya bude ta Shiga,haduwar Office din ta Kai haduwa sanyi da kamshi ke tashi kawai komai unique ne a Office din,kujera ta samu ta zauna tana jiransa sai kallon Office din takeyi tana Jin dadi yanzu nan na mijinta ne,Aslam ne ya fito daga wani daki a cikin Office da wani cup a hannunsa,yayi mamaki ganin Nusaiba tana zaune,Fuska ya daure itama ta daure Fuska a ranta tace oh a nan aka dauke shi aiki mijina ne ya dauke shi ashe me shara da gogeg goge ne Alhmdllh zai ga wulakancin duniya,kallon up and down take Masa sai yace ranki ya dade me kike bukata? tana harararsa tace Office din mijina nazo kaga Mallam dalla kawo min lemo Kai baka iya kula da bakin oganka ba ta ja tsaki,Aslam ya kalleta tare da furta Sorry Hajiya ya shiga inda aka tanada wajen da yake zuba kayan coffee dinsa,tea da lemuka,ya bude fridge tare da dakko wani lemo me mugun tsada ya dakko ya kawo gabanta tace zuba min mana Yana tausayinta a ransa ya zuba Mata tare da Mika Mata ta karba tana Masa kallon banza ta Sha lemon tana tunani a ranta lallai lemon nan na musamman ne,ta sake cewa I wonder har yanzu wani kamshi yake me Dadi ya fa kamata mutumin nan talauci yasa aji Yana wari amma kullum fes da shi,wani kyau ma yake da kiba,muryarsa taji yace shike nan abinda kike bukata? Wani kallon banza tayi Masa ta ja tsaki tace kaga karka tsaya min a kai ci gaba da share sharenka....kafin ta rufe baki Sufyan ya shigo da sauri Yana zuwa gaban Aslam ya rusuna tare da furta dan Allah kayi hakuri Sir wallahi abubuwa ne Suka Sha kaina kayi hakuri dan Allah wallahi na manta shaf amma Zan rubuta anjima kadan na tura maka,Aslam yace kayi sauri please Zan jira a gida ka tura min ta Email don't waste my time, Inshaallah Sir Inshaallah ,Nusaiba Ido ta zaro tana kallon ikon Allah amma duk da haka bata wannan take ba ita ya aka Yi Aslam yake da kudi kenan ba talaucewa yayi ba,Kai ta dafe Kamar zata yi kuka ta fara tunanin ta ya zata koma wajen tsohon mijinta mamaki Kuma ya kashe ta dama Sufyan yaron Aslam ne a karkashinsa yake aiki,Aslam Yana kallonta ransa a bace ya hade rai ya wuce ta gabanta zai wuce gida,Sufyan ya mikawa key yace ka rufe min Office ya fito,da sauri Sufyan ya ja hannun Nusaiba da tayi mutuwar zaune Suka fito ya rufe Office din suna Fitowa Suka samu Aslam ya Danna remote din mota tun daga nesa ya bude ta ya shiga,Nusaiba kallon motar takeyi tabbas itace Suka Zo a cikinta tare da Siyama,Kawai kallon ikon Allah takeyi,motar Sufyan ta kalla wata kucakar mota wani takaici ya lullube ta haka ta bishi Suka shiga sai gida,Aslam kuwa mamaki yake yi dama Sufyan ne ya auri Nusaiba amma take Masa iyayi,dariya yayi wani farin ciki ya kama shi tabbas yanzu yasan Nusaiba tana cikin wani hali, cike da farin ciki ya koma gida Siyama tana Palo Yana shigowa tazo ta fada jikinsa tana furta Oyoyo ya dagata sama Yana murna,tace wannan murnarfa? Ya Shiga bata labarin abinda ya faru tsakaninsa da Nusaiba ai Siyama har kasa ta durkusa da hannu biyu ta kwaso Shoki yayi dariya ta sake kwasowa tana waka da baki tace yau Nusaiba ba bacci Yar banza,mijin nata ma ashe yaron mu ne,na Kara maka farin ciki? Yace da me Yana Murmushi ya manna ta a kirjinsa tace yau Ina Sallah na gama period,Aslam harda ihun murna yace ai yanzu ba jiran wani dare ya dauketa Kamar jaririya sai bedroom dinsa Yana cewa first Evening zamuyi ba first night ba
Nusaiba Kuwa suna komawa bedroom Suka shiga shi Sufyan ma bai San matar Ogansa bace yace Wai lafiya Naga kin rasa sukuni sai gumi kike yi,Nusaiba mayafinta ta jefar ta zame dankwalinta ta jefar tana fifita da hannunta tana huci tace Aslam oganka tsohon mijina ne shine Wanda ka zuga ni na kaishi Kara ka zugani na karbi takardar sakina a hannunsa,Sufyan ya dora Hannu a Kai Yana wayyo Naga ta kaina Ogana ne na Shiga Uku aikina,Nusaiba tace wa yake ta wani aikinka yanzu ya fika kudi dama ashe da kudinsa,ya zanyi na Shiga dubu ma ba uku ba, gashi Siyama ta aure min miji ya zanyi,Sufyan baki ya bude yana kallon ikon Allah yace Ina ta aikina kina ta wani kudi baki da hankali Wai dama? Nusaiba tace dalla karka dameni mafitata nake hangowa,Sufyan mamaki ya kashe shi yace amma ke butulu ce baki San arziki ba,Iyayena nake hanawa ci da Sha sabo dake sabo da ke na kasa tara komai,Sai kayi Kuma cewar Nusaiba,sai nayi fa Kika ce? ta duro ashar tace burar.....kafin ta rufe baki mari taji ta ko ina,daina gani tayi na wani lokaci ya nade hannun riga ya hau jibgarta Kamar ya samu katon gardi tana ihu nan take idonta ya kakkafe ya juye numfashinta ya koma sama sama sai ta Fara furzo da jini ta bakinta amma Sufyan ko asibiti bai kaita ba sai da Allah ya taimaketa numfashinta ya dawo dai dai ta kasa tashi sabo da dukan data ci sai Jan jiki da Haka ta jingina jikin bed tana cewa ni ka sakeni wallahi wajen Tsohon mijina Zan koma ga me kudin gaske,Tsaki Sufyan ya ja sabo da zai iya kisan Kai ya fice ya barta a gidan tana ta tunanin kudin Aslam Yaya za ayi ta koma wajensa.
Affan kuwa kyale Raudah yayi sai da aka kwashe kwana uku ya tabbata ta huce sannan ya sameta a compound zata fita ya tareta yace Raudah ta,Baki ta turo gaba,yace my Life, Mene ta furta yace dan Allah kiyi hakuri,wa Zan so in bake ba,Ina nuna Miki cewar ke kadai nake da,kece kadai a zuciyata,ki rage kishin nan My life tsohuwar budurwata ce fa me zanyi da ita,Raudah tace sau Nawa kuke komawa wajen tsofaffin budurwarku kuce ai ita kuka Fara so baku mantawa da juna,Banda ni to Ni ai na baki labarin abinda Suka min ta ya Zan koma wajenta ai da na cika marar zuciya,Kiyi hakuri ba laifina bane,Raudah ta kalle shi tayi missing dinsa tace idan na sake ganin wata tazo wajenka duk abinda na maka Kai ka jiyo,Affan yace ae ki mare ni ma,Murmushi tayi tace ko da kudi ai ban iya marinka,key din motar ya karba yace muje na kaiki Office,Kar ka ja min a wajen aikin nan namu akwai Yan mata,ke Kam kishi ya Miki yawa,tace ya zama dole ai indai akanka ne,Key din ta kwace ta Shige mota tace da kaina zanje ta Shige mota taja ta tafi tana Murmushi tare da dago Masa Hannu.