Sashe 12
Auren Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tashi yayi da sauri yaga itace tana shigewa jikinsa da sauri ya dirga kasa daga bed din har zai kwanta a kasa ya tuna shi fa guy ne baya kazanta Tsaki ya ja yabi ta window ya koma dakinsa yace aikin banza warin balaga takeyi ma Yana karkade jikinsa harda shinshina inda ta fado Masa a jiki yace kaji ko warinta ya manne min a jiki irin wannan warin sai na balaga yanzu ma ta Fara balaga na rainata ma banza ta gyara min daki kwadayayya ta cinye min kazata ya furta tare da fadawa saman bed dinsa ya kwanta Kiran Sallah yaji an kwala yace ta cuceni ban karasa baccina ba ya tashi ya daura Alwala ya wuce masallaci yana doro da carbi a hannunsa Kalar jallabiyarsa kullum ko masallaci zai je carbinsa ma toomatch yake da carbi da kayansa carbinsa sunfi kala hamsim ko wanne Kaya da Kalar carbinsa ana taku dai dai ya shiga masallacin unguwar, Liman ya sanshi Yana shigowa zaka ji kamshinsa Yana bawa liman dariya sai dai Yana birge mutane duk gayunsa Sallah a jam'i kullum ba fashi ko wacce Sallah har sun Saba da liman da duk wani me zuwa masallacin.
Sai da aka idar da Sallah Affan ya daga hannu sama Yana Addua Allah ka azurtani,Allah ka bani kudi....kudi ya Allah na halak...Liman yace samari barka da asuba Affan yace Morning liman how are you? Dariya liman yayi yace Alhmdllh, Affan ya mike tsaye yace lafiya dai liman muyi Maganar a tsaye sabo da rigata zata yamutse ka ganta ta Sha guga bana so ta yamutse na tafi hanya a haka,liman ya zaro Ido yace asuba ce fa yaro da sauran duhu wa zai ganka,Sabo da jin dadin kaina ai ni Zan kalli kaina cewar Affan,Liman ya jinjina kai Yace baka da aure ne? Affan yace wuuu Ni aure rufa min asiri da yanzu Ina nan hankali a tashe Ni da cikakken bacci munyi hannun riga,Liman Murmushi yayi yace kaga Kuma da zaka Yi auren sai kafi haka nutsuwa,Affan yace to nifa gaskiya bana son aure yanzu mace ta dameni da kudin cefane kaina ma da kyar nake rikewa,Liman yayi dariya yace baka da budurwa saurayi kamarka kyakyawa da Kai haka kowa ya ganka yaga Namiji irin Kalar da Mata ke yayi,Affan ya shafa sajensa yace ba ruwana haka Kawai soyayya yanzu sai da kudi inje in tari budurwa bani da abin bata ta ci min mutunci,Liman me kudi ne na gaske yace kaje ka kula ko wace Indai da aure kake sonta Ni Kuma ko nawa zaka Bata Yar hidimar Mata dai Zan dinga baka har muga abinda Allah zaiyi, Affan yace to yaji samun kudi yace dama Ina da budurwa Ina sonta fada mukayi akan kudin anko tana so na za ayi biki na kasa siya Mata anko kunya tasa da kaina na fece,Liman yace tayi aure ko bata Yi ba? Bata Yi aure ba jirana takeyi Kawai Liman yace ka koma ka Bata hakuri ku daidaita Yar hidimar Mata dai Zan dinga baka har a tsaida Maganar aure ya kamata ace kana da aure bai dace mutum me addini irinka ba ka zauna haka Kuma muna limamai mu zuba muku Ido bayan Allah ya hore Mana yanda zamu tallafeku, Affan yayi godiya ya fice Yana murna a ransa wurin samun kudi ya samu shi Kam Yana cewa Allah na gode ma ka amsa Addua ta sai ta fada Kan liman.
Kwanan Nusaiba biyu a daki a kulle Aslam ya kulleta yace sai ta fito Masa da motarsa abinci ma Dan kadan yake Dan zubawa ya Mika mata,tana ta kuka ta dinga Kiran Mama a waya,ba shiri Mama ta sauka a kofar gidan Charity tana bakin kofar da aka kulle Nusaiba tace ki fito Masa da motarsa a zauna lafiya,Nusaiba tace sai naci uwarki shegiya munafuka,Aslam Yana gidan yaji ana bubbuga gate yaje ya bude yaga mama ce ta shigo tana karewa gidan kallo tace Ina kudinka? Ina motocinka makaryacin banza dama karya kaje kake Mana ka jefa yata a masifar talauci,Aslam yace kije ki fadawa yarki ta fito min da motata,Mama ta kalle shi tace butulu wato babu mutunci ba girmamawa Aslam bai kulata ba suka shiga ciki yasa key ya Bude dakin Daya kulle Nusaiba Yana tsaye ya tare Hanya Mama ta shiga tana shiga ya maida kofa ya datse ya kulle su tare a dakin yace ku fito min da motata na fada muku,Mama ta zaro ido tace dama haka yake baida mutunci,Nusaiba tana hawaye tace wlh Mama zai kashe mu Yana da bindiga,Mama tace kwantar da hankalinki yanzu Ina motar? tace na siyar da ita ko kudin ma ban karba ba ya kulle ni,a jikin kofar Mama ta tsaya tace dan Allah surukina ka Bude mu sai muje a karbo maka motarka,Aslam ya kalli Charity dake sanye da Riga da skert na Atamfa wasu kodaddu yace wlh mutanen nan sun maidani wani banza,tunaninsu Banda hankali, charity tace yo ai Basu san da hankalinka bane basu san Kai cikakken Namiji bane sai yanzu,Aslam yace dan Allah? Charity tace Allah,yanzu ni cikakken Namiji ne? Ae sosai yanzu na tabbatar Amma da ka zauna Kamar solobuyo,Murmushi Aslam yayi yace Ni kaina sai najini wani na sake girma yanzu, Charity tace ah ai sai yanzu ni kaina na ganka kato,yace haba,? Tace Allah da karami nake ganinka, dariya sukayi Siyama tace Kara sa key na uku a fito da mota,Aslam ya bubbuga kofa gam gam hankalin su Nusaiba ya sake tashi yace a fito da mota,abinda zai muku zakuyi mamaki idan baku fito da mota ba cewar Charity tana taya Aslam Kamar kanwarsa.
Sai zuwa Safiya Aslam ya Bude kofa zai Basu abinci Nusaiba ta kwada Masa tsinin takalmi choge Nan take ya dafe Kai ya Fadi kasa a sume ga Charity bata kusa da gudu Nusaiba da Mama Suka fice daga gidan suka tafi wurin siyar da motoci zasu karbi kudi babu Wanda ya karbi mota ba alamarsa Suka tambayar duniya akace ba a sanshi ba Ashe Dan damfara ne barawon mota Kuma ya gudu da mota,Nusaiba sai da ta Fadi har kasa sabo da kudin ta gama kasafin su,ba kunya suka tashi Suka koma gidan Aslam,lokacin Charity ta shigo ta kwala ihu ganinsa a kwance jini na zuba ta Kansa da gudu ta fita ta samo wasu maza biyu Suka taimaka Mata aka sashi a mota taxi zuwa asibiti,Allah yasa Babu matsalar kirki dressing Suka Masa bayan ya farfado suka dawo gida Kansa nade da bandage Charity tana Masa Sannu sannan tana bashi hakuri har Maman Nusaiba ta shigo da gudu tana kuka tace Nusaiba ce ta Sume,Siyama ta rude ta fita taga Nusaiba a sume tayi suman karya sun hada wayo,Aslam ya fito shima da Kansa ya dauki Nusaiba Kamar bai gano su ba ya shigar da ita bedroom ya kulle ya sake sa key yace sai ta fito min da motata,Mama da tana murna Aslam ya yarda da karyar su, yace Mama tun kafin na dakko bindiga ki bar min gida,Mama da gudu ta fice daga gidan,Charity tace dan Allah kayi hakuri haka tunda motar nan sun riga sun siyar,Nusaiba tana daga ciki a kulle ta saki kuka tace wlh dan damfara ne ya gudu da kudin,Aslam saman kujera ya zauna cike da bacin rai sai da yayi kwalla sabo da bakin ciki yanzu ya tabbatar Kuwa siyar da motar tayi,yana so ya siyar da su ya biya banki kudi yanzu ta salwantar da motar gashi tafi kowacce tsada,hawaye ne ya zubo Masa Sabo da bakin ciki wannan wacce irin kaddara ce haka,tashi yayi Kawai ya sa key ya bude Nusaiba ta fito tana kallonsa tace akan wata tsohuwar mota harda kwalla lallai ka cika me son kudi Kan bala'i,waccen irin marar Imani ce ke Nusaiba Charity ta furta ranta a jagule ashar Nusaiba ta dura Mata ta haura sama tana Jan tsaki tana cewa akan wata banzar tsohuwar mota.
Cikin kwana uku Aslam ya tattara komai na kadara ya damkawa bank gida Kawai yake jiran ranar da zasu zo,Mum ma dubu dari Uku ta turo Masa daga can kasar da take Qatar, wasu kayan girkin ma babu a gidan yau Charity ta rasa me zata dafa kwata kwata tana Jin kunya Kuma a halin da yake ciki ta tambayi wani Abu Kawai sai ta dafa wake da shinkafa da Mai da yaji,ta shiga tayi wanka ta canja cikin doguwar rigar tsohon leshi tayi kyau gata kyakyawa komai yaji,tana Fitowa ta iske Nusaiba an Sha gayu cikin wani tsadajjen material tana latsa waya,Aslam ne ya fito sanye cikin kayan Shan iska Gajeren wando da Riga me gajeren hannu sky and white yayi kyau sai dai ya dan rame sabo da matsalar da yake ciki,Siyama tace Yaya Aslam na gama abinci amma wake da shinkafa na dafa da Mai da yaji,yace oh da kin fada min ba abubuwa na manta wasu abin sun Kare da an siyo ai Allah bai hanani kudin cefane ba ai ni na manta ke kuma baki tuna min ba,Charity tace bana so na takura maka ne ban San halin da kake ciki ba,thank you ya furta,Nusaiba ko kallon su Bata Yi ba tana Danna waya sai ma tabe baki da tayi,Siyama tace amma Ina ganin da kifi zaka fi iya ci,dubu Daya ta isa? ya tambaya tace ae ta karba,Nusaiba ta ja tsaki tana kunkuni Dan karya anzo gidanmu da motocin aro ana nuna kudi an kawo Ni tankamemen gida Ashe duk na aro ne daga yin aure cikin wata uku za ace komai ya Kare bank ya cinye kudi dama ba gaskiya bane duk kayan aro ne.
Sai da aka idar da Sallah Affan ya daga hannu sama Yana Addua Allah ka azurtani,Allah ka bani kudi....kudi ya Allah na halak...Liman yace samari barka da asuba Affan yace Morning liman how are you? Dariya liman yayi yace Alhmdllh, Affan ya mike tsaye yace lafiya dai liman muyi Maganar a tsaye sabo da rigata zata yamutse ka ganta ta Sha guga bana so ta yamutse na tafi hanya a haka,liman ya zaro Ido yace asuba ce fa yaro da sauran duhu wa zai ganka,Sabo da jin dadin kaina ai ni Zan kalli kaina cewar Affan,Liman ya jinjina kai Yace baka da aure ne? Affan yace wuuu Ni aure rufa min asiri da yanzu Ina nan hankali a tashe Ni da cikakken bacci munyi hannun riga,Liman Murmushi yayi yace kaga Kuma da zaka Yi auren sai kafi haka nutsuwa,Affan yace to nifa gaskiya bana son aure yanzu mace ta dameni da kudin cefane kaina ma da kyar nake rikewa,Liman yayi dariya yace baka da budurwa saurayi kamarka kyakyawa da Kai haka kowa ya ganka yaga Namiji irin Kalar da Mata ke yayi,Affan ya shafa sajensa yace ba ruwana haka Kawai soyayya yanzu sai da kudi inje in tari budurwa bani da abin bata ta ci min mutunci,Liman me kudi ne na gaske yace kaje ka kula ko wace Indai da aure kake sonta Ni Kuma ko nawa zaka Bata Yar hidimar Mata dai Zan dinga baka har muga abinda Allah zaiyi, Affan yace to yaji samun kudi yace dama Ina da budurwa Ina sonta fada mukayi akan kudin anko tana so na za ayi biki na kasa siya Mata anko kunya tasa da kaina na fece,Liman yace tayi aure ko bata Yi ba? Bata Yi aure ba jirana takeyi Kawai Liman yace ka koma ka Bata hakuri ku daidaita Yar hidimar Mata dai Zan dinga baka har a tsaida Maganar aure ya kamata ace kana da aure bai dace mutum me addini irinka ba ka zauna haka Kuma muna limamai mu zuba muku Ido bayan Allah ya hore Mana yanda zamu tallafeku, Affan yayi godiya ya fice Yana murna a ransa wurin samun kudi ya samu shi Kam Yana cewa Allah na gode ma ka amsa Addua ta sai ta fada Kan liman.
Kwanan Nusaiba biyu a daki a kulle Aslam ya kulleta yace sai ta fito Masa da motarsa abinci ma Dan kadan yake Dan zubawa ya Mika mata,tana ta kuka ta dinga Kiran Mama a waya,ba shiri Mama ta sauka a kofar gidan Charity tana bakin kofar da aka kulle Nusaiba tace ki fito Masa da motarsa a zauna lafiya,Nusaiba tace sai naci uwarki shegiya munafuka,Aslam Yana gidan yaji ana bubbuga gate yaje ya bude yaga mama ce ta shigo tana karewa gidan kallo tace Ina kudinka? Ina motocinka makaryacin banza dama karya kaje kake Mana ka jefa yata a masifar talauci,Aslam yace kije ki fadawa yarki ta fito min da motata,Mama ta kalle shi tace butulu wato babu mutunci ba girmamawa Aslam bai kulata ba suka shiga ciki yasa key ya Bude dakin Daya kulle Nusaiba Yana tsaye ya tare Hanya Mama ta shiga tana shiga ya maida kofa ya datse ya kulle su tare a dakin yace ku fito min da motata na fada muku,Mama ta zaro ido tace dama haka yake baida mutunci,Nusaiba tana hawaye tace wlh Mama zai kashe mu Yana da bindiga,Mama tace kwantar da hankalinki yanzu Ina motar? tace na siyar da ita ko kudin ma ban karba ba ya kulle ni,a jikin kofar Mama ta tsaya tace dan Allah surukina ka Bude mu sai muje a karbo maka motarka,Aslam ya kalli Charity dake sanye da Riga da skert na Atamfa wasu kodaddu yace wlh mutanen nan sun maidani wani banza,tunaninsu Banda hankali, charity tace yo ai Basu san da hankalinka bane basu san Kai cikakken Namiji bane sai yanzu,Aslam yace dan Allah? Charity tace Allah,yanzu ni cikakken Namiji ne? Ae sosai yanzu na tabbatar Amma da ka zauna Kamar solobuyo,Murmushi Aslam yayi yace Ni kaina sai najini wani na sake girma yanzu, Charity tace ah ai sai yanzu ni kaina na ganka kato,yace haba,? Tace Allah da karami nake ganinka, dariya sukayi Siyama tace Kara sa key na uku a fito da mota,Aslam ya bubbuga kofa gam gam hankalin su Nusaiba ya sake tashi yace a fito da mota,abinda zai muku zakuyi mamaki idan baku fito da mota ba cewar Charity tana taya Aslam Kamar kanwarsa.
Sai zuwa Safiya Aslam ya Bude kofa zai Basu abinci Nusaiba ta kwada Masa tsinin takalmi choge Nan take ya dafe Kai ya Fadi kasa a sume ga Charity bata kusa da gudu Nusaiba da Mama Suka fice daga gidan suka tafi wurin siyar da motoci zasu karbi kudi babu Wanda ya karbi mota ba alamarsa Suka tambayar duniya akace ba a sanshi ba Ashe Dan damfara ne barawon mota Kuma ya gudu da mota,Nusaiba sai da ta Fadi har kasa sabo da kudin ta gama kasafin su,ba kunya suka tashi Suka koma gidan Aslam,lokacin Charity ta shigo ta kwala ihu ganinsa a kwance jini na zuba ta Kansa da gudu ta fita ta samo wasu maza biyu Suka taimaka Mata aka sashi a mota taxi zuwa asibiti,Allah yasa Babu matsalar kirki dressing Suka Masa bayan ya farfado suka dawo gida Kansa nade da bandage Charity tana Masa Sannu sannan tana bashi hakuri har Maman Nusaiba ta shigo da gudu tana kuka tace Nusaiba ce ta Sume,Siyama ta rude ta fita taga Nusaiba a sume tayi suman karya sun hada wayo,Aslam ya fito shima da Kansa ya dauki Nusaiba Kamar bai gano su ba ya shigar da ita bedroom ya kulle ya sake sa key yace sai ta fito min da motata,Mama da tana murna Aslam ya yarda da karyar su, yace Mama tun kafin na dakko bindiga ki bar min gida,Mama da gudu ta fice daga gidan,Charity tace dan Allah kayi hakuri haka tunda motar nan sun riga sun siyar,Nusaiba tana daga ciki a kulle ta saki kuka tace wlh dan damfara ne ya gudu da kudin,Aslam saman kujera ya zauna cike da bacin rai sai da yayi kwalla sabo da bakin ciki yanzu ya tabbatar Kuwa siyar da motar tayi,yana so ya siyar da su ya biya banki kudi yanzu ta salwantar da motar gashi tafi kowacce tsada,hawaye ne ya zubo Masa Sabo da bakin ciki wannan wacce irin kaddara ce haka,tashi yayi Kawai ya sa key ya bude Nusaiba ta fito tana kallonsa tace akan wata tsohuwar mota harda kwalla lallai ka cika me son kudi Kan bala'i,waccen irin marar Imani ce ke Nusaiba Charity ta furta ranta a jagule ashar Nusaiba ta dura Mata ta haura sama tana Jan tsaki tana cewa akan wata banzar tsohuwar mota.
Cikin kwana uku Aslam ya tattara komai na kadara ya damkawa bank gida Kawai yake jiran ranar da zasu zo,Mum ma dubu dari Uku ta turo Masa daga can kasar da take Qatar, wasu kayan girkin ma babu a gidan yau Charity ta rasa me zata dafa kwata kwata tana Jin kunya Kuma a halin da yake ciki ta tambayi wani Abu Kawai sai ta dafa wake da shinkafa da Mai da yaji,ta shiga tayi wanka ta canja cikin doguwar rigar tsohon leshi tayi kyau gata kyakyawa komai yaji,tana Fitowa ta iske Nusaiba an Sha gayu cikin wani tsadajjen material tana latsa waya,Aslam ne ya fito sanye cikin kayan Shan iska Gajeren wando da Riga me gajeren hannu sky and white yayi kyau sai dai ya dan rame sabo da matsalar da yake ciki,Siyama tace Yaya Aslam na gama abinci amma wake da shinkafa na dafa da Mai da yaji,yace oh da kin fada min ba abubuwa na manta wasu abin sun Kare da an siyo ai Allah bai hanani kudin cefane ba ai ni na manta ke kuma baki tuna min ba,Charity tace bana so na takura maka ne ban San halin da kake ciki ba,thank you ya furta,Nusaiba ko kallon su Bata Yi ba tana Danna waya sai ma tabe baki da tayi,Siyama tace amma Ina ganin da kifi zaka fi iya ci,dubu Daya ta isa? ya tambaya tace ae ta karba,Nusaiba ta ja tsaki tana kunkuni Dan karya anzo gidanmu da motocin aro ana nuna kudi an kawo Ni tankamemen gida Ashe duk na aro ne daga yin aure cikin wata uku za ace komai ya Kare bank ya cinye kudi dama ba gaskiya bane duk kayan aro ne.