← Book details Auren Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 44 OF 56

Sashe 44

Auren Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Washe gari daga gidan Mallam aka kawo musu lafiyayyen kari,Affan Yana ta fama da jinyar Raudah ana lallabata har dare ya sake yi tana kwance a saman bed tana latsa waya,Shi Kuma Yana zaune yana aiki a laptop dinsa tana saman cinyarsa Yana shigar da aikinsa,wayarsa ce tayi Kara ya duba yaga wata Yar BUK ce da Suka Yi Service tare Mardiyya,Wayar ya daga tare da furta hello Mardiyya ya kike,Ai Raudah tana ji ya Kira sunan mace Mardiyya ta mike zaune,Yana gaisawa da Mardiyya ta dawo jikinsa ta baya ta hade kirjinta da bayansa sannan ta Mika kunnenta jikin Wayar Wai sai taji me take cewa,Yana jinta yaci gaba da wayarsa ya aikin to kwana biyu kin buya,Raudah ta zaro Ido waje tare da sake tura kunnenta jikin Wayar Affan Yana ji,Mardiya tace dama Kira nayi mu gaisa yace na gode na gode ya kashe wayar, Wayar hankalinsa na Kan system Raudah a hankali tace wacece? Yace wata ce da Muka Yi service,Kuma macece fa Baby, tana da aure? Yace Ni kin tuna min ma na manta na tambayeta Yaya saurayinta da zai aureta naji auren Yana nan,Raudah tace au saurayine ma da ita ba Miji ba? Akwai danger gaskiya,yace menene haka Raudah? Kince fa kin daina yanzu Zaki Fara halinki ko,Raudah tace to ai laifinka ne Sanda nazo na Kara kunnena zanji me kake cewa shine kayi waye ka rage Volume Dan Kar naji,Affan yace wanne irin rage Volume nu ban danna komai ba kina gani waya Kawai nake,Raudah ta sake manne jikinta a nasa tasa hannunta tare da sakalo shi ta wuyansa tace ni na gani Sanda ka Danna Kaine baka kula ba,Ohhhh Wai me yasa kike min haka,Raudah tsoron fadansa taji tace okay naji amma dai ka kula saurayine da ita fa ba Miji ba,Affan ya girgiza Kai Kawai yace to aiki nake koma ki kwanta,Raudah tace oh korata kake Yi sabo da kayi waya da mace har ka Fara gajiya dani kwana daya,yanzu laushin kirjina fa kake ji duk ban kyauta ba because of that useless girl Mardiyya, Affan yace yi hakuri ni ba korarki nake Yi ba Yi zamanki a Haka,Raudah ta gyara sosai tare da makalkale shi a haka yake danna system din,Yana gamawa ya juya kanta,ta jawowa kanta Yana ta kokarin barinta sai ta warke amma ta jawo sha'awa baza ta bari ya kyaleta ba ya koma tare da hakkewa a kanta tana kuka tana rokonsa amma Ina Sam babu daga kafa.

Suna ta soyayyarsu da Raudah kamar zasu lashe juna har sati daya sannan ya koma aikinsa shima badan ransa ya so ba,5pm Raudah gida yaji gyara ko Ina ya dauki sheki da kamshi ta gama girki ta shirya a dining taci uban gayu na musamman,Yana shigowa ta tareshi tace Kai da kace 5 zaka dawo kalli time 5:30pm fa Ina ta jira,yace wani dan aikine ya rikeni,kayan jikinsa take karewa kallo taga wani waje yayi Kamar Kalar Powder ta Mata,tace mene wannan Kamar powder din mace,bani hannunka ta jawo Hannun Affan ta shinshina tace bani dayan naji shima ta shinshina tace yawwa babu komai,Raudah tayi kasa ta Fara kokarin janye Masa wando tace tsaya na gani,Affan ransa ya baci cikin tsawa yace Raudah tsorata tayi ta sake shi da sauri ta Fara bashi hakuri,yace Kamar fa kin Fara haukacewa kishi ne zai haukataki idan baki Wasa ba,wallahi idan nayi niyya ke baki Isa ki hanani kula wata ba,daga auren zan Fara kula Mata,ki kwantar da hankalinki ke kadai nake da ita,tace to ni ko mene kazo wajena ko me kaji kana so ka dawo gida Zan baka, Affan ya samu salon wayon da zaina Mata dama tana damunsa da kukan zafi da kyar take yarda da shi, tunda hakane shi yaga hanya,Murmushi yayi Yana Jin dadi yace ke nake bukata Ina cin abinci,tace ka Bari Mana sai 10pm ni wlh zafi,yace okay so kike na fara yin Yan Mata...Raudah da sauri tace ba damuwa muje ko Mene Zan maka Kawai ka fada zanyi,yace Kuma har 10pm din Zan sake round 2 tace to da sauri, Wai ita Kar yayi budurwa,idan zai fita da kuka suke rabuwa ita bazai fita ba sai dai su zauna tare a gida.

AsmaBaffa
[4/1, 5:47 AM] Sis Asma: 🛢️ AUREN MU🛢️

86-90

Official

By
AsmaBaffa

Page naki ne
AIDA MAMAN TASNIM

Nusaiba tana cika Iddarta ta shirya a boye sai gidan Aslam tana zuwa taga gidan ya sake haduwa komai an canja Masa new design,a bakin gate ta tsaya ta kasa shiga gida tasan ba halin shiga idan ta tuna abinda ta aikata gate din take shafawa da hannayenta tana zubar da hawaye ta Dade a haka har ta gaji ta juya gida inda ta fito,washe gari gidan Sufyan ta shirya taje gidan ta zaci gwauro ne bata san Yana sakinta da wata daya ya koma ya nemi gafarar Iyayensa ya auri tsohuwar budurwarsa Zahrau sun rabu tana sonsa Yarinyar kirki Yar tarbiyya ai Kuwa Yana aurota bai Dade ba ya samu Offer a land and housing sai dai albashinsa ba Kamar na Aslam ba amma ba laifi,yanzu iyayensa da Yan Uwa duka komai Yana musu,Zahrau har Kara takura Masa takeyi akan dole yayi musu abubuwa,Nusaiba tana Shiga gidan taga Zahrau tana gyarawa Sufyan kwalar rigarsa suna dariya cike da so ai kasa karasawa tayi tasan yayi aure ta juyo da sauri ba tare da sun ganta ba,ta dawo gida sai kuka Wanda ba shiri Mama ta shirya ta tafi gidan da Mum take ta manta irin wulakancin data Yi Mata lokacin da Mum tazo a gyara.

Mama gidan da Mum take ta shiga tana ta kwada Sallama Hajiya Zainab ta tafi gidan biki sai Mum,Mama tana ta sallama ba ji ba gani Mum ta fito sai taga Mama Fuska ta daure cike da bala'i Mum tace Wai wace ne ta damemu da Sallama taki ci taki cinyewa,Mama ta marairaice tare da langabar da kai tace surukata...ohhhhh da baki san ni surukarki bace sai yanzu dan Allah malama Fadi me ya kawoki sauri nake yi Ina da aikin yi,Mama tace zuwa nayi Dan Allah Surukata ki taimaka kisa danki ya maida Nusaiba dakinta dan Allah kuyi Hakuri komai ya wuce zamu gyara Inshaallah dan Allah ki taimaka Mana,Mum wani kallo ta Mata up an down sannan ba tare data furta komai ba ta tofar mata da yawu tuf ta juya tare da komawa ciki ta bar Mum a tsaye kikam,gajiya tayi da tsaiwa ta juya ta koma gida dabarunta sun Kare dama duk Shirin da tace shine kawai zata yi,Nusaiba ana gida zaman gida Wasa farin girki, bayan wasu Yan lokuta Shehu baya dagawa mama da Nusaiba kafa baya sakar musu fuska da Mama da Nusaiba wahala suke Sha sauran yaransa yake yiwa abinda suke so kawai,suna haka katsam sai ga Aslam,Shehu Yana gida yace a'a dana yau Kaine a gidan? Aslam yace ae Abba ya zauna kusa da Shehu a tabarma ya gaisar da shi ko kallon Mama da Nusaiba baiyi ba Wanda gasu nan a tsaye sun taho da sauri sun tsaya musu a kai suna magana kasa kasa da ita da Nusaiba,Shehu yace ashe haka arzikinka dama yana nan ya dawo naji labari Ina ta so ma nazo har gidanka Allah mun gode maka,Aslam yace Abba Kai na daban ne nasan me kaunata ne Kuma babban mutum ne Kai idan ba damuwa bana Inshaallah zamu tafi aikin Hajji tare da Kai,Shehu yace wayyo Allah dadi kashe ni Aslam ya dinga dariya,Nusaiba da Mama harda murna tunanunsu bikon Nusaiba zaiyi shi yasa ya Fara kashe musu kudi irin da,Aslam yace Kawu ba iya Makkah zaka tsaya ba Paris da Dubai zaka je inda Nusaiba take mafarkin zuwa yanzu gashi Shehu Babanta shi zai je Kuma Aslam Yana sani yayi hakan Sabo da farkon aurensu haka tace sai an kaita honey moon Paris ko Dubai,yace sannan duk Sanda kaji kana son hutawa Abba karka damu ka hada kayanka kazo gidana ka huta,ko me kake bukata Kawai ka kirani a waya,Shehu Kamar yayi suman dadi haka yake ji gani yake Kamar a mafarki,yace Kuma tare da abokinka zaku je Baban Siyama Kawu da Aunty,Shehu yace Alhmdllh na gode na gode ya dinga godiya Yana murna,Aslam yace Maganar shirye shiryen visa Zan kiraka a waya ya mike ya zaro Yan dubu dubu ya mikawa Shehu yace gashi kayi amfani da wannan,Mama ta dafe kirji,Nusaiba Hawaye ya Fara antayo Mata a kumatu,Mama tace surukina dan Allah kayi hakuri abinda Muka maka,Nusaiba tace dan Allah ka yafe min ka dawo muyi aure,Aslam yayi hanyar barin gidan ya juyo yayiwa Nusaiba da Mama kallon banza yace mugaye kawai yaja Tsaki ya juya shi da Shehu Suka fice,har mota Shehu ya rakashi ya tafi sannan ya dawo Yana taku dai dai Yana doro,Shehu yace Alhmdllh Yana takama a gidan ya zama Dan gayen dattijo aka bar Mama da Nusaiba da bakin ciki.

Aisha tuni an maida Aurenta da Farooq suna zamansu lafiya yanzu duk Karya da fadan da sukeyi sun daina sai mutunta juna kowa baya so wani Abu yazo ya shiga tsakaninsu,soyayya suke me tsafta abinsu su,Nabeela kuwa tana yin Idda ta samu miji wani babban mutum ne me Mata ta hakura da Affan tasan babu aure a tsakaninsu ma tunda Dan Uwansa Yana raye amma ta take gaskiya yanzu Kam ta hakura ta auri me Mata Kuma tayi zamanta babu Neman rigima,Sabeer ma yayi aure ya auri zankadediyar matarsa Habiba.

Raudah da Affan suna soyayyarsu sosai matsalar Raudah kishin tsiya,yau tana zaune a gida Affan ya fita sai ga Wayar Landlady ta shigo tana ta kiranta dagawa tayi tun kafin tayi magana Landlady tace Raudah maza maza fito ga mijinki Affan da wata sun shiga shopping zo ki gani da idonki,Raudah tace what? Na fada Miki maza basu da amana mijina haka ce ta rabamu da shi na aminta da shi Ashe maci amana ne,gani Ina ShopRite maza kizo kafin ya bar wajen, Landlady tayi gaskiya domin Affan ne da wata zasu shiga ciki ita Kawai dan ta ganshi da mace shine tace budurwarsa ce bata San cewar Amaryar liman bace ogan Affan Kuma Liman dinne yasa Affan ya kaita wajen wata Mata suna business tare da matar Liman,matar daga kasar waje tazo shine Affan ya kaita.
Chapter 44 · 0% Book details