Sashe 32
Auren Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Siyama kuwa ta Sha leshi dan ubansu golden and white,Kawu yace babu batun shagali ko angon bai je wajen Amarya ba Kawu ya Hana,Amarya tana zaune cikin Yan tsirarin abokanta suna cin abinci Kamar ba Amarya ba komai bata akeyi tana lashewa da ance gashi zata ci abinta, sun Kuna Bluetooth speaker suna Jin kidansu suna nishadi tunda ango ya bugo Mata waya yace sai na Zo daukan Amarya,Siyama tana Jin kunya tace ka daina zumudi fa period na Fara jiya da dare,Aslam yace ba komai bukatar maje hajji Sallah tunda an daura yanzu hankalina a kwance yake nasan kin Zama tawa,Murmushi yace 4pm zanzo daukan abata ki shirya da wuri,Siyama Wayarta ma ta kashe duk sai taji ba dadi abinka da wacce bata taba barin gida ba kullum kana tare da iyayenka dole idan za a rabaka da gida kaji ba dadi,Siyama kuka ta Fara Yi tun da wuri kawaye suna tsokanarta ta dauki pad dinta ta Shige toilet tana hawaye a cikin toilet din ta fashe taci kukanta ta koshi duk ta bata kwalliyar tata sai fuskar ta wanke gaba daya ta fito idonta yayi alamar Kuka,Aunty tana Sallamar baki ta kalli Siyama Suka hada Ido tace ke Kuma meye na kukan duk rashin kunyar tana ina? Yan Uwa Suka saki guda da shewa Siyama sai sabon kuka ya taho,dangi Suka Yi caaa a kanta da tsokana sabo da kowa ya Santa da baki amma yau Kamar ba Siyama ba,kawaye suna Mata tsiya Kawai ta kwanta a katifa ta juya musu baya tun tana hawaye har bacci ya kwasheta kowa yazo Ina Amarya sai aga tana shakar uban bacci tun 12 har kusan 3pm bacci takeyi,ana ta posting pics din ango da na Amarya a online Wanda suka Zo bikin duk da cewar ma basu dauki hoton tare ba, ai Yan layinsu suna fara zuwa bikin Suka tasheta da tsokana wata tazo ta Dana Mata duka a gadon baya ke dalla tashi Amarya da bacci ki tashi kiyi wanka aka taru akan Siyama sabo da mutane da yawa ana Wasa da ita ta ko Ina caccakarta akeyi,4pm Aunty tasa tayi wanka tare da canja Kaya wani material ta sa me shegen kyau na lefe,suna bikinsu dai Kafin dare aka Kai Yan biki gidan Amarya duk me son ganin gidan Amarya Aslam ya turo wasu bakin abokansa sun kaisu a mota har Aunty taje taga gidan yarta komai yayi Mata itakam,Yan bikin ma suna ta yabawa da yan uwa,na nesa sun tafi ma tuni sabo da Kawu dama ya fada musu ba taro shi yasa Basu zauna ba,Aunty Kuwa dama ta fadawa mutanenta Kawu ne zai Kai Amarya da Kansa shi yasa babu macen data zauna zuwa magriba kowa ya watse sai Yan uwan Aunty su Uku suna ta aikin gyara gidan,Sabeer ne yazo ya kwashi kayan lefe duk wani abinda Siyama take so ya tafi,Aslam ce Masa yayi ya bar kayan a motarsa da ita zai dakko Amarya idan sunje gida ya cire kayan gaba daya,Kamar Aslam bazai Zo daukan Siyama ba sai dare Aunty tace tayi wanka ta shirya ya yo waya yace gashi nan,Siyama tace ban dade da yin wankan ba fa to ai na Amarya ne idan Kika Yi yanzu ai kin huta Yi a can,Siyama haka ta fesa wanka tazo ta Gama shafe shafenta ta saka wani Leshi da Kawu ya dinka Mata na biki me shegen kyau sea blue and black mayafinta me shegen kyau Kalar kayan da takalmi da jaka komai same color tayi kwalliyarta me kyau ta shafa turaruka tana shiri Kawu da Aunty Suka shigo Suka zauna a dakin Suka Fara Mata nasiha iri iri tana ji ta fashe da kuka suna Yi tana kuka kanta a kasa har Aslam yazo tana kuka,Aunty itama harda hawaye ta fada bedroom dinta ta kwanta tana ta kuka Aunty zata rabu da yarta,Kawu shi ya tasa keyar Siyama tana kuka kanta a kasa ta rufe kanta da mayafi tana kuka ya kaita har mota inda Aslam ke mazaunin driver sanye cikin wata shaddar Yar ubansu ruwan kwai,Shiga tayi gefe ta zauna Kawu ya rufe dama ya yiwa Aslam tasa Nasihar tuni,Siyama ta sauke glass din motar tana shesheka tace Kawu..... Kawu yace a'a Siyama karyar rashin kunya ta Kare ki daina nemana gaki ga Aslam aje ayi ta samun ciki idan Kinga dama ki Haihu sau goma a shekara Allah yasa Albarka,Aslam Murmushi yayi Kawu ya yiwa Aslam godiya yace su tafi Aslam yaja mota Suka tafi Siyama na kuka.
Affan dawowa yayi gida daga wajen daurin Aure Raudat ta tsaya a jikin window tace Ina kaje ne haka? Yace yau ki tayani jaje an min gora,Nasha Sanda da Kaye an min mugun Kaye budurwa ta aka daurawa aure Bata so na wani take so,Raudat taji wani farin ciki tace amma ya Naga baka damu ba? Juyowa yayi Yana kallonta yace sabo da ke nake so,Raudat baki ta bude yace yes ke nake so fa na fada Miki kince sai kin duba shike nan ai rayuwa ce harda yin Kalar tausayi,Raudat tayi dariya tace ai zan baka amsa ne nan gaba,Affan ya girgiza Kai a ransa yace zanyi maganinki.
Washe gari da Yamma wata budurwa ce Yar kwalisa Fara ta dau wanka ta sa key ta bude part din Affan kawai ta Shige a gaban Raudat dake Compound,Raudat ta bita da kallo yarinya Shuru Shuru bata fito ba har Raudat ta gaji ta shigo ranta a bace tace ke wai wa kike jira? Yarinyar tana yanga tace Affan, Raudat tace a Ina Kika samu key dinsa? tace shi yaje gidanmu ya bani yace na jira shi, Fitowa Raudat tayi cike da kishi hankalinta a tashe ta zaune a compound Affan ya dawo da sauri ya fito ya shiga part dinsa Kuma ya rufo kofa,Shuru Shuru ta ga bai fito ba shigowa tayi ciki ta same shi a zaune shi kadai bakuwar Kuma tana kitchen tana girki kamshi na tashi,Raudat zuciyarta ta jagule ta rasa inda zata sa kanta a duniya taji san yi fita tayi cikin fushi ta koma bedroom dinta ta kwanta a saman bed dinta ta Fara hawaye kafin kace me ta fara ciwon kai ko Hussain bata taba sonsa haka ba bare ma tayi wani ciwon Kai a kansa amma Affan bayan ciwon Kai harda zazzabi ya lullubeta,Affan Kuwa Yana ganin Raudah ranta ya baci ya mike ya shiga kitchen yace Safara'u zo ki tafi gida kin gama aikinki, Safara'u ta fito tace Yaya Affan ka manta sakon da zaka bani na bawa Mallam,Yace af na manta ya mike da sauri ya dakko Mata kudi yace gashi kice ragowar kudin gidan Mai ne da nace Zan kawo tace to tare da ficewa,tana tafiya dan Masifa kunnen Raudat taji Sanda tayiwa Affan Sallama tashi Raudat tayi tare da saka hijab sai palon Affan.
Kishi ya gama cika Mata zuciya ta banko kofar ya mike zai shiga bedroom tace waccen wacece? Yace wa? Who is she? ta furta da fada tana rawar sanyi yace baki da lafiya ne? Ban sani ba mayaudari kace min Ni kake so kana zuwa ka kawo wata macen mene baka fada min ba,Affan yace Yar Liman ce fa uban gida na a'a Yar gidan sarkin musulmi ce karewar limanci si ba muharramarka bace da zaku kebe dan ubanta tazo tace zata maka girki Kawai kace sonta kake yi Kuma bana sonka bana bukatarka gaba daya ta juya ta fice Kamar zata tashi sama.
Affan yaji Dadi yace yawwa kin Kama kanki ya zauna Yana murna sosai tana sonsa,washe gari ogan Raudat yazo zai dauketa zasu tafi aiki,taji sauki ta fito cikin shirinta da simple doguwar Riga marar nayi ta fito da takardunta,Affan yau hutawa yake a gida yaga Raudat an dauketa a dalleliyar mota ya zaci saurayi ne ya kule sosai Kamar zaiyi duka.
Yamma nayi ta dawo Affan ya tareta a Hanya waye wancan? wa? Wanda ya daukeki a mota,abokin aikina nane ai gwara ni ba namiji na kawo dakina ba,Tambayarta yayi a nutse Raudat mu daina irin wannan kina so na ko bakya so na? Tsayawa tayi tana tunani Kawai ya juya ya Fara tafiya abinsa tace wait bai tsaya ba ta bishi da sauri tace Ina sonka kayi hakuri,tsayawa yayi cak Yana murna,gabansa ta dawo ta tsaya tace Ina sonka wlh kayi hakuri,sabo da murna ma kasa magana yayi,takardunta ya karba yace mu je na Zama mijjn Kan tace suna tafiya abinsu Suna hira abinsu amma kishin masifa ne da Raudat duk da haka tana zargin Affan ko suna shiri da Safara'u.
Affan dawowa yayi gida daga wajen daurin Aure Raudat ta tsaya a jikin window tace Ina kaje ne haka? Yace yau ki tayani jaje an min gora,Nasha Sanda da Kaye an min mugun Kaye budurwa ta aka daurawa aure Bata so na wani take so,Raudat taji wani farin ciki tace amma ya Naga baka damu ba? Juyowa yayi Yana kallonta yace sabo da ke nake so,Raudat baki ta bude yace yes ke nake so fa na fada Miki kince sai kin duba shike nan ai rayuwa ce harda yin Kalar tausayi,Raudat tayi dariya tace ai zan baka amsa ne nan gaba,Affan ya girgiza Kai a ransa yace zanyi maganinki.
Washe gari da Yamma wata budurwa ce Yar kwalisa Fara ta dau wanka ta sa key ta bude part din Affan kawai ta Shige a gaban Raudat dake Compound,Raudat ta bita da kallo yarinya Shuru Shuru bata fito ba har Raudat ta gaji ta shigo ranta a bace tace ke wai wa kike jira? Yarinyar tana yanga tace Affan, Raudat tace a Ina Kika samu key dinsa? tace shi yaje gidanmu ya bani yace na jira shi, Fitowa Raudat tayi cike da kishi hankalinta a tashe ta zaune a compound Affan ya dawo da sauri ya fito ya shiga part dinsa Kuma ya rufo kofa,Shuru Shuru ta ga bai fito ba shigowa tayi ciki ta same shi a zaune shi kadai bakuwar Kuma tana kitchen tana girki kamshi na tashi,Raudat zuciyarta ta jagule ta rasa inda zata sa kanta a duniya taji san yi fita tayi cikin fushi ta koma bedroom dinta ta kwanta a saman bed dinta ta Fara hawaye kafin kace me ta fara ciwon kai ko Hussain bata taba sonsa haka ba bare ma tayi wani ciwon Kai a kansa amma Affan bayan ciwon Kai harda zazzabi ya lullubeta,Affan Kuwa Yana ganin Raudah ranta ya baci ya mike ya shiga kitchen yace Safara'u zo ki tafi gida kin gama aikinki, Safara'u ta fito tace Yaya Affan ka manta sakon da zaka bani na bawa Mallam,Yace af na manta ya mike da sauri ya dakko Mata kudi yace gashi kice ragowar kudin gidan Mai ne da nace Zan kawo tace to tare da ficewa,tana tafiya dan Masifa kunnen Raudat taji Sanda tayiwa Affan Sallama tashi Raudat tayi tare da saka hijab sai palon Affan.
Kishi ya gama cika Mata zuciya ta banko kofar ya mike zai shiga bedroom tace waccen wacece? Yace wa? Who is she? ta furta da fada tana rawar sanyi yace baki da lafiya ne? Ban sani ba mayaudari kace min Ni kake so kana zuwa ka kawo wata macen mene baka fada min ba,Affan yace Yar Liman ce fa uban gida na a'a Yar gidan sarkin musulmi ce karewar limanci si ba muharramarka bace da zaku kebe dan ubanta tazo tace zata maka girki Kawai kace sonta kake yi Kuma bana sonka bana bukatarka gaba daya ta juya ta fice Kamar zata tashi sama.
Affan yaji Dadi yace yawwa kin Kama kanki ya zauna Yana murna sosai tana sonsa,washe gari ogan Raudat yazo zai dauketa zasu tafi aiki,taji sauki ta fito cikin shirinta da simple doguwar Riga marar nayi ta fito da takardunta,Affan yau hutawa yake a gida yaga Raudat an dauketa a dalleliyar mota ya zaci saurayi ne ya kule sosai Kamar zaiyi duka.
Yamma nayi ta dawo Affan ya tareta a Hanya waye wancan? wa? Wanda ya daukeki a mota,abokin aikina nane ai gwara ni ba namiji na kawo dakina ba,Tambayarta yayi a nutse Raudat mu daina irin wannan kina so na ko bakya so na? Tsayawa tayi tana tunani Kawai ya juya ya Fara tafiya abinsa tace wait bai tsaya ba ta bishi da sauri tace Ina sonka kayi hakuri,tsayawa yayi cak Yana murna,gabansa ta dawo ta tsaya tace Ina sonka wlh kayi hakuri,sabo da murna ma kasa magana yayi,takardunta ya karba yace mu je na Zama mijjn Kan tace suna tafiya abinsu Suna hira abinsu amma kishin masifa ne da Raudat duk da haka tana zargin Affan ko suna shiri da Safara'u.