← Book details Ƙanwar Maza Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 47 OF 47

Sashe 47

Ƙanwar Maza Complete Hausa Novel · about 3 min read

Jabir ya ce "Easy Adam, yarinya ce ƙarama, ki na ji ki san abin da zaki din ga rubutawa a social media, wanda ya baki waya ma shi ne babban mai laifi, da ya bawa under age waya. Babban mutum ne sannane, ɗan gidan marigayi Galadiman Kano ne, bashi da alaƙa da siyasa, amma kin yi masa ƙazafi shi mahaifinsa basarake ne, kuma ɗan kasuwa ba kuɗin tal.....

"Shut up Jabir, na meye zaka din ga yi mata wani bayani"

"A'a ka yi haƙuri, kin ga bashi haƙuri komai ya wuce" wani kallon zaka bushe ruma tayi masa, ta ƙara gyara jakarta ta ɗauke kanta gefe guda.

Mamaki ne ya cika Adam, shi da yake dodo ko a cikin manyan mutane, amma shi wannan 'yar shilar ke rainawa hankali, yana yi mata magana amma ta mayar da shi É—an iska.

Jabir ya jinjina kai ya ce "Lallai gaba da gabanta, anya wannan yarinyar ba mahaukaciya bace ba?"
Kallon Jabir tayi ta galla masa harara, haka kawai tana ganinsa ta ji ta tsaneshi, wani mugun haushinsa ya kamata, ya fiye shishshigi.

Adam rasa abin yi ma yayi, dama wata babbace he knows how to deals with her, amma wannan ya hukunta ta ya ce ya yiwa wa?.

Ruma ta miƙe tsaye da jakarta, tana kallon wanda suka kawota, jinjina kai kawai suke, da ganin namijin ƙoƙarin da ubangidansu yayi.

Cikin ƙunƙuni ta ce "Ni a mayar da ni in da aka ɗauko ni" tayi maganar tana nufar ƙofar fita.

"Ku kamata ku É—aure mini ita, sannan a nemo mini waye ubanta, in nuna wa babanta banbancin arziki da tsiya, shine dai-dai yi na, dan na fuskanci bayan talauci har da rashin tarbiyya a tare da ita.

Ba tare da ta waiwayo ba ta tsaya, dan ma kar ta kalleshi ya yi mata kwarjini ta ce "Shi baban nawa sai ka bishi kabari ka nuna masa ka fishi kuÉ—i, kuma Alhamdilillah ni dai an yi mini tarbiyya dai-dai gwargwado, kuma wallahi sai na saka yayyena sun yi maka bugun sakwara, har DPO na unguwarmu sai na gaya masa, ba sunanka Adam ba É—an galadima ko wambai to wallahi sai na faÉ—a ka saceni ka kawoni cikin maza" tuni ya daskare a wurin, jikinsa ya hau tsuma, ga zafin maganganu da fitsarar Ruma, ga razani na jin muryar da take ta addabar kunnuwansa.

Cikin azama ya fizgota, ya juyo da ita gabansa, ya riƙe hijjabinta tare da rigar uniform ɗin ta. Kallon hannun takawa tayi, da ya sanya wani agogo mai kyawun gaske, amma babban abin da ya razana ruma, yadda ya riƙota ta wuya hannun ƙaton namiji a jikinta kan ƙirjinta, abin da aka ce ta ɓoye ta tattala, kar wani ya kai hannu wurin, idan ba haka ba za tayi ciki, amma hannun wani ƙato a wurin !!!

(Saura page É—aya mu kammala book1, wanda za su sai book 2, an fara payment 500 ne, in sai an gama document 800.

0009450228
Aisha Adam
Jaiz bank.
Sai a turo shedar biya ta 08081012143)

Ayshercool
08081012143
Chapter 47 · 0% Book details