Sashe 46
Ƙanwar Maza Complete Hausa Novel · about 8 min read
A washegari Mummy ta shirya ta tafi gidan Galadima mai ci a yanzu, wato gidan su Jabir.
Hajiya Lubabatu na ganinta suka yi wata shewa, tare da gaisawa da junansu.
Hajiya Lubabatu ta ce "Ya akwai labari ne?"
"Da É—umi-É—uminsa ma kuwa, mu shiga daga bedroom.
Cikin É—aki suka shiga, Mummy ta ce "Ya jikin Galadima ne?"
Hajiya Lubabatu ta ce "To ni me ma zance miki ne, a ƙarshen watan nan dai nake son ko ni ko jabir wani ya je, ance dai da sauƙi"
"To Allah ya ƙara afuwa, amma gaskiya Yakamata ki miƙe ki ɓata alaƙar da ke tsakanin Adam da Jabir, kin san idan babansu ya rasu sarauta gidanmu za ta dawo, ke sai ki zuba ido shikenan babu makoma, idan sarauta ta dawo hannun Adam waya san lokacin da zai mutu balle Jabir ɗin ma yayi sarautar, duk da ina ta ƙoƙarin ƙara rura wutar gaba tsakaninsa da Mahmud, sai dai Mahmud wawa ne, ya ƙi mayar da hankali a kan Sarautar, ba ta gabansa ".
Hajiya Lubabatu ta yi murmushi ta ce "Jamila kenan, ai kema kin san ba a zaune nake ba, kuma da sannu dukkaninmu zamu yi nasara, ai ke dama ba kya burin sarautar ta dawo gidanku"
"Ƙwarai kuwa, shiyasa nake ta son komai ya ɓaci, ko kin san ashe Adam bai warke daga wannan larurar da yayi ba yana yaro, mai kamar farfaɗiyae nan ba?"
"Haba dai, ya aka yi ki ka sani?"
"Samha ce ta zo ta titsiyeni, wai ta gani a sashin su, wai ko ina da hannu a rashin lafiyar ta sa, na ce mata ni babu ruwana, da ciwonsa na ganshi"
Hajiya Lubabatu ta ce "Kai samha ma akwai bin ƙwaƙwƙwafi, shareta kawai ai aiki yana kyau sosai"
"Haaa ke dai bari, idan har ina raye ko zan tafi tsirara sai Binta ta É—anÉ—ana kuÉ—arta in Allah ya yarda sai ciwon nan ya zame masa hauka tuburan, na kaÉ—a sauran yaran nata tare da wannan shegiyar yarinyar mai kama da larabawa"
Hajiya Lubabatu ta yi dariya ta ce "Shi dai wannan É—a abu ya zame masa goma da ashirin, da hauka ko in ce farfaÉ—iya, ga kuma maita duk shikaÉ—ai"
"Hmm ke dai bari, ina jiran lokacin da zan kwatsa zancen nan a cikin masarautar Kano, É—an da suke ji da shi maye ne, da ya sha a nonon uwarsa, ta ta ba ta baiyyana ba sai ta shi"
Cike da rashin imani suke ƙyaƙyace dariya, kamar ba za su bar duniya ba.
Cikin dare da misalin ƙarfe biyu da rabi, Baba uwani ce ke sanɗa kamar 'yar fashi, ta buɗe babbar ƙofar sashen Ammi ta fita, kai tsaye ta nufi sashen Mummy, tana tura ƙofar sashin ta buɗe, ta kutsa tana waige-waige.
Hanyar kitchen ta bi, ta tarar da Mummy a wani É—aki a zaune tana jiranta.
Baba uwani ta duƙa ta gaida Mummy, Bata amsa ba ta dubeta ta ce "Kin san dalilin da ya sanya na nemekk?"
Ta girgiza kai alamar a'a.
"An ce mini É—an uwar É—akinki Adam, haryanzu bai warke ba, ciwon nan da yayi da yarinta yana nan yana fama, jiya ma ya tashi haka ne?"
Baba uwani ta ce "Wallahi ban sani ba uwar É—akina, jiya ta aikeni, kuma ina tunanin babu wanda ya sani, saboda da na dawo ban ji labari ba".
"Ba tambayarki nake dogon labari ba, ance mini akwai wani abu da aka shafa masa, ya tashi da wuri, wannan abin nake son ki sanya ido ki É—auko mini"
"Ranki ya daÉ—e, ai ban san a in sa suke ajiyewa ba, ba ta sanya ni a sabgar neman maganin sa ba"
"Bai shafeni ba uwani, ki aikata abin da na ce kawai, tashi ki bani wuri"
Haka baba uwani ta taso, tana tunanin ta in da zata fara aiwatar da wannan aiki mai mugun hatsari.
****
Yau ruma fakar idon Yasir ta yi, ta ɗauki wayar nan ta jefa a jakar makarantar ta, ta yiwa mama sallama ta tafi makaranta. Sai dai da ta je makarantar babu wanda ta iya nunawa wayar, gudun kar yaran su tona mata asiri a ƙwace wayar, sai dai ta na jin kanta riƙe wayar nan da take yi, duk da ba wayar kirki ba ce ba.
Yau mama ba ta nan, ta je cikin gari za su kai wani kayan lefe na wani ɗansu, dan haka ruma sai lissafi take a kan ba zata islamiyya ba, ƙulewa za ta yi a ɗaki ta yi kallo a waya, kuma ta sha baccinta.
Ta tsaya ta sai gyaÉ—a a hanya, tana tafe tana ci, kamar ba É—iya mace ba, dan ruma duk wani abu na jan aji na mata ruma ba ta iya ba, haka nan take rayuwarta kamar namiji.
Ƙarar mota ta ji a bayanta, sai dai kan ta kauce, ta ga an sha gabanta da motar, wasu ƙarti ne suka fito suka ce "Shiga mota"
"In shiga aje ina kamar a film É—in indiya"
Cikin tsawa É—ayan ya ce "Ki shiga mota na ce"
Ruma ta cake ta riƙe ƙugu ta ce "Wai saboda me, in shiga ka kai ni ina?"
"Kai dalla dannota kawai, za ta ɓata mana lokaci" sau ɗaya ya tankaɗa ƙeyar ruma, ta hantsila cikin motar.
Aikuwa ta din ga kurma ihu "Al'ummar É—orayi an saceni, dan Allah ku kawo mini agaji" rufe motar suka yi, suka ja dama motar tint ce, sai dai ruma ta cika musu kunne da kururuwa.
"Ke, kin ishemu, zamu yanka ki da da wuƙa a motar nan"
"Wallahi ba zan yi shiru ba, kun satoni kun sakani a tsakiyarku bayan ku ba muharramaina bane ba".
Wanda yake tuƙa motar, ya dubi na kusa da shi, cikin harshen turanci ya ce "Anya kana ganin wannan yarinyar ce kuwa?"
"Oho, mu kai masa ita dai, shi zai tantance ".
"To ai gani na yi yarinya ce sosai, yaushe wannan zata iya wannan abu?"
"Kai wannan sai ta aikata, ji yadda take wa mutane ihu, dan ya ce ban da cin zarafi da sai na sakata a silent yanzun nan".
"Wallahi idan baku buɗe mini motar nan na fita ba, sai na tara muku jama'a, ashe ma ku ƙananan 'yan kidnapping ne, da kuka sace ni, to wallahi ni ƙanwar maza ce, idan yayyena suka gano ku, sai kun raina kanku" babu wanda ya kulata cikinsu, har suka isa in da zasu je, ba ta yi shiru ba ko na mintuna. Haka zalika idan za a kasheta ba ta san ta in da aka bi ba, saboda baƙin glass ne a motar.
Ita dai ta ji an tsaya, aka buÉ—e mota aka ce ta fito. Fitowa ta yi tana kallon harabar da aka paker motar.
Ingiza ruma suka yi, ta ƙanƙame jakarta tana kalle-kalle.
Wani falo aka shiga da ita, suna shiga wani irin sanyi ya daketa, ta ce "Wayyo sanyi" duk sai da suka kalleta kamar wata 'yar ƙauye.
Ita ba kawotan ne ya dameta ba, tsaruwar gidan da yadda aka narka masa dukiya ne ya burgeta take ta kallo.
Sanyin Ac ne ya fara damunta, saboda haryanzu babu wanda ya ce mata komai, tunani ta fara yi, idan mama ta dawo ta tarar bata nan fa, gaba É—aya hankalinta ya tashi yayi gida, a yadda take jin labarin kidnapping dai ba haka ake yin sa ba, ko da yake dai ai babu maraba.
Miƙewa tayi ta dubi mutumin da yake zaune a bakin ƙofa ta ce "Bawan Allah dan Allah ku zo ku sallameni, kar babata ta dawo ta ga bana gida"
"Wuce ki zauna, kafin na fasa kanki da harsashi"
"A'a da bom zaka fasa mini kai, ni me na yi muku ne?"
"Wallahi ki ka cigaba da yi mana hayaniya, sai na saka igiya na É—aureki"
"Kamar ya ya ka É—aureni da igiya, sai ka ce ragon layya? Dan Allah ku zo ku mayar da ni"
Cikin tsawa ya ce "Ki koma ki zauna na ce".
Tsaki ta ja ta koma ta zauna, bin ruma ya yi da kallo jin yadda ta yi masa tsaki.
Zama ta yi ta ɗauko gyaɗarta ta cigaba da ci, tana ɓata wurin, mai gadin na ta kallonta yake, ita kamar ma ba ta damu da ɗaukotan nan da suka yi ba, gaba ɗaya ba ta da wata damuwa.
Ta gama cin gyɗarta, ta buɗe jakarta ta ɗauko rake. Duk ta ɓata wurin, ta gama ta gaji tayi shiru ta zubawa sarautar Allah ido.
Surutan mutane suka ji, alamar za a shigo. A cikin mutanen da suka shigo su uku, tana yiwa É—aya kallon sani, sai dai ta manta a ina ma ta sanshi.
"Tana ina?" Ya faɗa a taƙaice.
"Gata nan a gabanka sir, ita muka samo, kuma ta faÉ—i wasu abubuwa da ya sake tabattar da ita ce" cewar É—aya daga cikin wanda suka kawo ruma.
Mamaki ne ya kama shi, ta ina ƙaramar yarinya kamar wannan, ta samu waya, har ta iya yi masa wannan comment ɗin.
Ya zauna ya na ƙare mata kallo, sai wani haɗe rai take tana basarwa, tana harare-harare ta gefen ido.
Jabir ya ce "ka bi komai a sannu Please, ka ga ƙarshen abin ma ashe yarinya ce, dama haƙura kai kamar yadda na gaya maka da farko".
"Me na yi miki ki ka kirani da ɓarawo?" Yayi maganar yana tsareta da ido.
Mamaki ne ya kama ruma, ita a ina ta sanshi da zata kira shi da ɓarawo. Ya sake maimaita maganar amma tayi banza taƙi magana.
Jabir ya ɗauko wayarsa, ya shiga account ɗin da ruma tayi comment da shi ya nuna mata, ya ce "ke ki ka yi wannan comment ɗin?" Ta zubawa Jabir ido, shima ta ƙi kulashi, sai dai a yanzu ta gane in da ta taɓa ganin Adam, a Instagram taga hotonsa tayi comment.
"Wai kurma ce ne?"
"Sir wallahi ba kurma bace, yanzu ta gama magana iskanci ne, ka bari a casata kawai".
"Am talking to you, me na yi miki ki ka ci mutuncina, wai na saci kuÉ—in talakawa, ance miki ni É—an siyasa ne?"
Hajiya Lubabatu na ganinta suka yi wata shewa, tare da gaisawa da junansu.
Hajiya Lubabatu ta ce "Ya akwai labari ne?"
"Da É—umi-É—uminsa ma kuwa, mu shiga daga bedroom.
Cikin É—aki suka shiga, Mummy ta ce "Ya jikin Galadima ne?"
Hajiya Lubabatu ta ce "To ni me ma zance miki ne, a ƙarshen watan nan dai nake son ko ni ko jabir wani ya je, ance dai da sauƙi"
"To Allah ya ƙara afuwa, amma gaskiya Yakamata ki miƙe ki ɓata alaƙar da ke tsakanin Adam da Jabir, kin san idan babansu ya rasu sarauta gidanmu za ta dawo, ke sai ki zuba ido shikenan babu makoma, idan sarauta ta dawo hannun Adam waya san lokacin da zai mutu balle Jabir ɗin ma yayi sarautar, duk da ina ta ƙoƙarin ƙara rura wutar gaba tsakaninsa da Mahmud, sai dai Mahmud wawa ne, ya ƙi mayar da hankali a kan Sarautar, ba ta gabansa ".
Hajiya Lubabatu ta yi murmushi ta ce "Jamila kenan, ai kema kin san ba a zaune nake ba, kuma da sannu dukkaninmu zamu yi nasara, ai ke dama ba kya burin sarautar ta dawo gidanku"
"Ƙwarai kuwa, shiyasa nake ta son komai ya ɓaci, ko kin san ashe Adam bai warke daga wannan larurar da yayi ba yana yaro, mai kamar farfaɗiyae nan ba?"
"Haba dai, ya aka yi ki ka sani?"
"Samha ce ta zo ta titsiyeni, wai ta gani a sashin su, wai ko ina da hannu a rashin lafiyar ta sa, na ce mata ni babu ruwana, da ciwonsa na ganshi"
Hajiya Lubabatu ta ce "Kai samha ma akwai bin ƙwaƙwƙwafi, shareta kawai ai aiki yana kyau sosai"
"Haaa ke dai bari, idan har ina raye ko zan tafi tsirara sai Binta ta É—anÉ—ana kuÉ—arta in Allah ya yarda sai ciwon nan ya zame masa hauka tuburan, na kaÉ—a sauran yaran nata tare da wannan shegiyar yarinyar mai kama da larabawa"
Hajiya Lubabatu ta yi dariya ta ce "Shi dai wannan É—a abu ya zame masa goma da ashirin, da hauka ko in ce farfaÉ—iya, ga kuma maita duk shikaÉ—ai"
"Hmm ke dai bari, ina jiran lokacin da zan kwatsa zancen nan a cikin masarautar Kano, É—an da suke ji da shi maye ne, da ya sha a nonon uwarsa, ta ta ba ta baiyyana ba sai ta shi"
Cike da rashin imani suke ƙyaƙyace dariya, kamar ba za su bar duniya ba.
Cikin dare da misalin ƙarfe biyu da rabi, Baba uwani ce ke sanɗa kamar 'yar fashi, ta buɗe babbar ƙofar sashen Ammi ta fita, kai tsaye ta nufi sashen Mummy, tana tura ƙofar sashin ta buɗe, ta kutsa tana waige-waige.
Hanyar kitchen ta bi, ta tarar da Mummy a wani É—aki a zaune tana jiranta.
Baba uwani ta duƙa ta gaida Mummy, Bata amsa ba ta dubeta ta ce "Kin san dalilin da ya sanya na nemekk?"
Ta girgiza kai alamar a'a.
"An ce mini É—an uwar É—akinki Adam, haryanzu bai warke ba, ciwon nan da yayi da yarinta yana nan yana fama, jiya ma ya tashi haka ne?"
Baba uwani ta ce "Wallahi ban sani ba uwar É—akina, jiya ta aikeni, kuma ina tunanin babu wanda ya sani, saboda da na dawo ban ji labari ba".
"Ba tambayarki nake dogon labari ba, ance mini akwai wani abu da aka shafa masa, ya tashi da wuri, wannan abin nake son ki sanya ido ki É—auko mini"
"Ranki ya daÉ—e, ai ban san a in sa suke ajiyewa ba, ba ta sanya ni a sabgar neman maganin sa ba"
"Bai shafeni ba uwani, ki aikata abin da na ce kawai, tashi ki bani wuri"
Haka baba uwani ta taso, tana tunanin ta in da zata fara aiwatar da wannan aiki mai mugun hatsari.
****
Yau ruma fakar idon Yasir ta yi, ta ɗauki wayar nan ta jefa a jakar makarantar ta, ta yiwa mama sallama ta tafi makaranta. Sai dai da ta je makarantar babu wanda ta iya nunawa wayar, gudun kar yaran su tona mata asiri a ƙwace wayar, sai dai ta na jin kanta riƙe wayar nan da take yi, duk da ba wayar kirki ba ce ba.
Yau mama ba ta nan, ta je cikin gari za su kai wani kayan lefe na wani ɗansu, dan haka ruma sai lissafi take a kan ba zata islamiyya ba, ƙulewa za ta yi a ɗaki ta yi kallo a waya, kuma ta sha baccinta.
Ta tsaya ta sai gyaÉ—a a hanya, tana tafe tana ci, kamar ba É—iya mace ba, dan ruma duk wani abu na jan aji na mata ruma ba ta iya ba, haka nan take rayuwarta kamar namiji.
Ƙarar mota ta ji a bayanta, sai dai kan ta kauce, ta ga an sha gabanta da motar, wasu ƙarti ne suka fito suka ce "Shiga mota"
"In shiga aje ina kamar a film É—in indiya"
Cikin tsawa É—ayan ya ce "Ki shiga mota na ce"
Ruma ta cake ta riƙe ƙugu ta ce "Wai saboda me, in shiga ka kai ni ina?"
"Kai dalla dannota kawai, za ta ɓata mana lokaci" sau ɗaya ya tankaɗa ƙeyar ruma, ta hantsila cikin motar.
Aikuwa ta din ga kurma ihu "Al'ummar É—orayi an saceni, dan Allah ku kawo mini agaji" rufe motar suka yi, suka ja dama motar tint ce, sai dai ruma ta cika musu kunne da kururuwa.
"Ke, kin ishemu, zamu yanka ki da da wuƙa a motar nan"
"Wallahi ba zan yi shiru ba, kun satoni kun sakani a tsakiyarku bayan ku ba muharramaina bane ba".
Wanda yake tuƙa motar, ya dubi na kusa da shi, cikin harshen turanci ya ce "Anya kana ganin wannan yarinyar ce kuwa?"
"Oho, mu kai masa ita dai, shi zai tantance ".
"To ai gani na yi yarinya ce sosai, yaushe wannan zata iya wannan abu?"
"Kai wannan sai ta aikata, ji yadda take wa mutane ihu, dan ya ce ban da cin zarafi da sai na sakata a silent yanzun nan".
"Wallahi idan baku buɗe mini motar nan na fita ba, sai na tara muku jama'a, ashe ma ku ƙananan 'yan kidnapping ne, da kuka sace ni, to wallahi ni ƙanwar maza ce, idan yayyena suka gano ku, sai kun raina kanku" babu wanda ya kulata cikinsu, har suka isa in da zasu je, ba ta yi shiru ba ko na mintuna. Haka zalika idan za a kasheta ba ta san ta in da aka bi ba, saboda baƙin glass ne a motar.
Ita dai ta ji an tsaya, aka buÉ—e mota aka ce ta fito. Fitowa ta yi tana kallon harabar da aka paker motar.
Ingiza ruma suka yi, ta ƙanƙame jakarta tana kalle-kalle.
Wani falo aka shiga da ita, suna shiga wani irin sanyi ya daketa, ta ce "Wayyo sanyi" duk sai da suka kalleta kamar wata 'yar ƙauye.
Ita ba kawotan ne ya dameta ba, tsaruwar gidan da yadda aka narka masa dukiya ne ya burgeta take ta kallo.
Sanyin Ac ne ya fara damunta, saboda haryanzu babu wanda ya ce mata komai, tunani ta fara yi, idan mama ta dawo ta tarar bata nan fa, gaba É—aya hankalinta ya tashi yayi gida, a yadda take jin labarin kidnapping dai ba haka ake yin sa ba, ko da yake dai ai babu maraba.
Miƙewa tayi ta dubi mutumin da yake zaune a bakin ƙofa ta ce "Bawan Allah dan Allah ku zo ku sallameni, kar babata ta dawo ta ga bana gida"
"Wuce ki zauna, kafin na fasa kanki da harsashi"
"A'a da bom zaka fasa mini kai, ni me na yi muku ne?"
"Wallahi ki ka cigaba da yi mana hayaniya, sai na saka igiya na É—aureki"
"Kamar ya ya ka É—aureni da igiya, sai ka ce ragon layya? Dan Allah ku zo ku mayar da ni"
Cikin tsawa ya ce "Ki koma ki zauna na ce".
Tsaki ta ja ta koma ta zauna, bin ruma ya yi da kallo jin yadda ta yi masa tsaki.
Zama ta yi ta ɗauko gyaɗarta ta cigaba da ci, tana ɓata wurin, mai gadin na ta kallonta yake, ita kamar ma ba ta damu da ɗaukotan nan da suka yi ba, gaba ɗaya ba ta da wata damuwa.
Ta gama cin gyɗarta, ta buɗe jakarta ta ɗauko rake. Duk ta ɓata wurin, ta gama ta gaji tayi shiru ta zubawa sarautar Allah ido.
Surutan mutane suka ji, alamar za a shigo. A cikin mutanen da suka shigo su uku, tana yiwa É—aya kallon sani, sai dai ta manta a ina ma ta sanshi.
"Tana ina?" Ya faɗa a taƙaice.
"Gata nan a gabanka sir, ita muka samo, kuma ta faÉ—i wasu abubuwa da ya sake tabattar da ita ce" cewar É—aya daga cikin wanda suka kawo ruma.
Mamaki ne ya kama shi, ta ina ƙaramar yarinya kamar wannan, ta samu waya, har ta iya yi masa wannan comment ɗin.
Ya zauna ya na ƙare mata kallo, sai wani haɗe rai take tana basarwa, tana harare-harare ta gefen ido.
Jabir ya ce "ka bi komai a sannu Please, ka ga ƙarshen abin ma ashe yarinya ce, dama haƙura kai kamar yadda na gaya maka da farko".
"Me na yi miki ki ka kirani da ɓarawo?" Yayi maganar yana tsareta da ido.
Mamaki ne ya kama ruma, ita a ina ta sanshi da zata kira shi da ɓarawo. Ya sake maimaita maganar amma tayi banza taƙi magana.
Jabir ya ɗauko wayarsa, ya shiga account ɗin da ruma tayi comment da shi ya nuna mata, ya ce "ke ki ka yi wannan comment ɗin?" Ta zubawa Jabir ido, shima ta ƙi kulashi, sai dai a yanzu ta gane in da ta taɓa ganin Adam, a Instagram taga hotonsa tayi comment.
"Wai kurma ce ne?"
"Sir wallahi ba kurma bace, yanzu ta gama magana iskanci ne, ka bari a casata kawai".
"Am talking to you, me na yi miki ki ka ci mutuncina, wai na saci kuÉ—in talakawa, ance miki ni É—an siyasa ne?"