Sashe 21
Aisha Saddiqah Part 4 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Daga bisani ta gaida Oummana da fulatanci, Oummana ta amsa ta kuma tanbayeta lafiyar su Ummanta da Babanta da iyalin Baba Barau. Siddiqah ta amsa duka, kanta a sunkuye, murya a ladabce. Anan Oummana tace maqasudin kiran nata dama don tayi mata nasiha ne. Nan tace Hamma ya basu wuri. Hamma yace "Nani abin harda kora?" Tace "ai zan kiraka ne inna gama da ita, akwai abinda ba sai ka ji ba".
Prince ya shige dakinsa ya barsu. Oummana ta fara yiwa Aisha fada da nasiha kamar ita ta haifeta.
Nasiha ce ta manya sannan mai shiga jikin yaro, inda tace wa Aisha.
"Idan kana aure yana nufin ka girma. Abubuwa da yawa zasu iya faruwa a rayuwar auren mace, musamman da dangin miji, to idan irin haka ta faru ba komai ake fadawa iyaye ba Indo, sabida gudun bacin ransu.
Sannan shi aure rai ne dashi. In zama bai kare ba mace da mijinta sai su dawo su shirya, su manta komai cikin dan lokaci, amman iyaye basa mantawa.
Don haka toh a kiyaye irin haka anan gaba, kuma koda wani abu ya faru to Aysha kizo ki sameni ni Oummana ko Nennen ku, na tabbatar hukuncin da zamuyi wallahi Umman ki baza tayi ba. Kinji ko Indo?
Sabida Allah shine shaidata, yadda nake jin Hammansu a raina haka nake son ki babu bambanci a wurina, kinji?
Shiyasa nake so nan gaba ba fata ake ba abin Allah ya kiyaye, ko da wani abu irin haka ya faru toh dan Allah Aisha ki koyi magance shi tsakanin ki da mijin ki.
Musamman irin wannan da ya faru da Taiwo, mijin ki na matukar son ki, har Taiwo ta isa tasa kice kin bar auren ki?
Allah yayi maki albarka ya kawo muku yara masu albarka. Shi wannan da baya son sarautar nan tamu, wato ya gado ubansa, Allah yasa ya haifo min wanda zai so sarauta.
A zuciyar Aisha tace "Amin". Sai lokacin ta gane Hamma baya falon ya basu wuri itada Oummana.
Da ya tashi fitowa ba kayan da ya fita dasu ne a jikinsa ba, ya canza su zuwa kananan kaya farar shirt LV da bakin wandon Jeans. Yace "toh Oummana dare ya fara zan maidata" Oummana tace "Aisha nagode Allah ya kara albarka" nan Aisha ta mikawa Oummana sakon Ummanta. Ga Oummana da son Sandal da Oud. Nan tayi ta godiya,ta kuma sa aka miko mata babbar jakar data shiryawa Aisha tsarabar da zata tafi dashi gida.
A hanyarsu ta dawowa ma Prince na makale da kafadun Aisha Malam Buhari na tuki, ya sassauta murya yace "Ayshah! Kin ce bazaki je gida na ki gani ba ko? Koda akwai abinda bai miki ba a canza don shine gidanki da
yanmu anan Gombe". Da sauri Siddiqah tace "Don Allah Hamma Abdul a'ah, ba sai naje ba, zan gani next time". Hammah yace "ai shikenan. Kin dade baki je ba.
Wanda ya jure yayi rainon Dan shillansa wajen shekara guda, ai jiran kwana bakwai bazai gagareshi ya fige abinsa ba".
Da haka suka kawo kofar gidan su Siddiqah.
Taimakon da Allah yayima Siddiqah ta fito nan da nan shine Malam Buhari dake cikin motar nan, wanda ya kure radio yana sauraron wata tsohuwar waqa ta Sani Aliyu Dandawo. Da Prince bazai barta hakannan ba sai ya kara cakudata.
Duk da haka cike da damuwa Hammah ya rike hannunta yace.
"Babyyyyy. I will miss you kin sani ko?"
Siddiqah ta dube shi idanunta narai narai tace dashi cikin harshen yarbanci "I will Miss you more Hamma....". Ba zato taji ya kai hannunta ga bakinsa ya sumbata. Da kyar ta samu ta zare hannunta daga cikin nasa ta shige cikin gida ba ko waiwaye. Don gabadaya Hamma ya saka mata wata irin kasala (by just mere looking into his blurred eyes).
Umma da Abba sun sha labarin Nani Oummana, irin kirkinta da karamcinta daga bakin Aisha. Ta fidda kayan da Oummana ta bata har da alkhyabba ta mata da manyan turamen super guda uku da manyan lesika uku. Ga bandir din filtex na Abban Aisha da Baba Barau.
A ranar sai can dare Siddiqa ta bar dakin Ummanta zuwa nata dakin, sun raba dare suna hira don ji suke kamar gobe-gobe ne Petel zata tafi ba kwana shidda masu zuwa ba.
Don Hamma ya tabbatar ma Abban Aisha in sun tafi zasu jima basu waiwayi gida ba, don hutun shekara ya kammala harda kari mai yawa.
Wajejen karfe 12 na dare Siddiqah ta gama komai na shirin kwanciyar ta. Hammah ya kira ta, Siddiqah ta daga hatta muryarta ta canza don barci take ji sosai tace.
"Hammah, baka kwanta ba?" Yace "na kasa barci ne Baby.... Ina missing furar kinnan da kindirmo..." Aisha ta rufe ido tana jin kunya kamar Hamma na kallonta, tana kuma tuna incident din na yau da ya kasa bacewa daga idanunta, feelings din kuma sababbi suka kasa barin ranta. Hamma yace "Baby you know what?" Ta girgiza kai kawai kamar Hamma na kallonta.
Hamma yace "ban taba jin eagerness a rayuwata irinna ranar da zaki dawo min ba. I will be patiently waiting for you and your annoying Jamb.
Daga ranar da kika dawo ne zamu fara rayuwa. Kinsan rayuwar mu ta Argentina babu komai cikin ta sai introduction na AISHA zuwa cikin lonely and pitiful rayuwar KEHINDE.
I reserved the day for you only, as I reserved myself for 43 years waiting for the day. Please Baby, ki bani dukkan go ahead da juriyar ki da zan bukata, kinji?"
Kunya kamar ta kashe Aisha. Prince ya cigaba da kashe Aisha da kalamai masu dadi yana gaya mata irin tanadin soyayyar da yayi mata daga ranar data dawo, har zuwa karshen rayuwar su.
Ashe dai Ishaq da take ji a ranta akan yana gaya mata kalamai da suke zauna mata a rai bai iya komai ba. Ga inda kalaman fatar baki kadai ke neman narkar da zuciyarta a take. Har hakan ya saka mata (nervousness) akan zuwan ranar tarewarta dinnan da Prince ke ta maimaitawa, ba tareda Prince ya san ya saka mata nervousness din ba.
A daren yau Hammah ya gaya mata maganganu masu matukar nauyi. A ciki ya gaya mata cewa throughout the 43 years of his life he had never had a sex with anyone. Waiting for her
. his dream wife.
As a hopeless romantic, ya jira zuwan true love dinsa tsayin wannan lokacin, and today, he thank the Exalted Lord Almighty for bringing her to his life.
(Duk da Haseenah ta so ta saka Prince ya kauce hanya Kehinde bai taba yin abinda ya wuce kissing na shan minti da ita ba. Wanda a yau, wancan abinda ya dan gitta a tsakaninsu ma regretting dinsa yake yi, yana kara istigfari).
Ya yarda ba wata soyayya ta kwanciyar hankali da sakewa da jin dadi mara misaltuwa kamar ta auren Sunnah.
Da sanyin muryar Prince dake kasheta da dadadan kalamai cikin kunnenta Aisha tayi barci akan wayar, sai ji yayi numfashin ta ya canza a hankali mai nuna tayi barci ta bar shi da wayarsa, batareda ta san lokacin da barcin ya sace ta ba. Shine dai yaga wayar na cigaba da reading kuma bai kara jinta ba. Dole ya kyaleta ya kwanta shima. Amma kam yau Prince yayi wahalallen barci na azaba wanda ko zamanin samartakarsa dana tashen balagarsa baiyi irinsa ba.
Firdaus ta taba gayawa Nenne a cikin gorin da Maman Kiki tayi wa Aisha harda na 'Lefe'. Ashe Nenne bata manta wannan ba abin yana tsaye a ranta.
Don haka tun ranar da suka koma Lagos ta kira Hamma Abdulrasheed suka gaisa.
Prince ya shige dakinsa ya barsu. Oummana ta fara yiwa Aisha fada da nasiha kamar ita ta haifeta.
Nasiha ce ta manya sannan mai shiga jikin yaro, inda tace wa Aisha.
"Idan kana aure yana nufin ka girma. Abubuwa da yawa zasu iya faruwa a rayuwar auren mace, musamman da dangin miji, to idan irin haka ta faru ba komai ake fadawa iyaye ba Indo, sabida gudun bacin ransu.
Sannan shi aure rai ne dashi. In zama bai kare ba mace da mijinta sai su dawo su shirya, su manta komai cikin dan lokaci, amman iyaye basa mantawa.
Don haka toh a kiyaye irin haka anan gaba, kuma koda wani abu ya faru to Aysha kizo ki sameni ni Oummana ko Nennen ku, na tabbatar hukuncin da zamuyi wallahi Umman ki baza tayi ba. Kinji ko Indo?
Sabida Allah shine shaidata, yadda nake jin Hammansu a raina haka nake son ki babu bambanci a wurina, kinji?
Shiyasa nake so nan gaba ba fata ake ba abin Allah ya kiyaye, ko da wani abu irin haka ya faru toh dan Allah Aisha ki koyi magance shi tsakanin ki da mijin ki.
Musamman irin wannan da ya faru da Taiwo, mijin ki na matukar son ki, har Taiwo ta isa tasa kice kin bar auren ki?
Allah yayi maki albarka ya kawo muku yara masu albarka. Shi wannan da baya son sarautar nan tamu, wato ya gado ubansa, Allah yasa ya haifo min wanda zai so sarauta.
A zuciyar Aisha tace "Amin". Sai lokacin ta gane Hamma baya falon ya basu wuri itada Oummana.
Da ya tashi fitowa ba kayan da ya fita dasu ne a jikinsa ba, ya canza su zuwa kananan kaya farar shirt LV da bakin wandon Jeans. Yace "toh Oummana dare ya fara zan maidata" Oummana tace "Aisha nagode Allah ya kara albarka" nan Aisha ta mikawa Oummana sakon Ummanta. Ga Oummana da son Sandal da Oud. Nan tayi ta godiya,ta kuma sa aka miko mata babbar jakar data shiryawa Aisha tsarabar da zata tafi dashi gida.
A hanyarsu ta dawowa ma Prince na makale da kafadun Aisha Malam Buhari na tuki, ya sassauta murya yace "Ayshah! Kin ce bazaki je gida na ki gani ba ko? Koda akwai abinda bai miki ba a canza don shine gidanki da
yanmu anan Gombe". Da sauri Siddiqah tace "Don Allah Hamma Abdul a'ah, ba sai naje ba, zan gani next time". Hammah yace "ai shikenan. Kin dade baki je ba.
Wanda ya jure yayi rainon Dan shillansa wajen shekara guda, ai jiran kwana bakwai bazai gagareshi ya fige abinsa ba".
Da haka suka kawo kofar gidan su Siddiqah.
Taimakon da Allah yayima Siddiqah ta fito nan da nan shine Malam Buhari dake cikin motar nan, wanda ya kure radio yana sauraron wata tsohuwar waqa ta Sani Aliyu Dandawo. Da Prince bazai barta hakannan ba sai ya kara cakudata.
Duk da haka cike da damuwa Hammah ya rike hannunta yace.
"Babyyyyy. I will miss you kin sani ko?"
Siddiqah ta dube shi idanunta narai narai tace dashi cikin harshen yarbanci "I will Miss you more Hamma....". Ba zato taji ya kai hannunta ga bakinsa ya sumbata. Da kyar ta samu ta zare hannunta daga cikin nasa ta shige cikin gida ba ko waiwaye. Don gabadaya Hamma ya saka mata wata irin kasala (by just mere looking into his blurred eyes).
Umma da Abba sun sha labarin Nani Oummana, irin kirkinta da karamcinta daga bakin Aisha. Ta fidda kayan da Oummana ta bata har da alkhyabba ta mata da manyan turamen super guda uku da manyan lesika uku. Ga bandir din filtex na Abban Aisha da Baba Barau.
A ranar sai can dare Siddiqa ta bar dakin Ummanta zuwa nata dakin, sun raba dare suna hira don ji suke kamar gobe-gobe ne Petel zata tafi ba kwana shidda masu zuwa ba.
Don Hamma ya tabbatar ma Abban Aisha in sun tafi zasu jima basu waiwayi gida ba, don hutun shekara ya kammala harda kari mai yawa.
Wajejen karfe 12 na dare Siddiqah ta gama komai na shirin kwanciyar ta. Hammah ya kira ta, Siddiqah ta daga hatta muryarta ta canza don barci take ji sosai tace.
"Hammah, baka kwanta ba?" Yace "na kasa barci ne Baby.... Ina missing furar kinnan da kindirmo..." Aisha ta rufe ido tana jin kunya kamar Hamma na kallonta, tana kuma tuna incident din na yau da ya kasa bacewa daga idanunta, feelings din kuma sababbi suka kasa barin ranta. Hamma yace "Baby you know what?" Ta girgiza kai kawai kamar Hamma na kallonta.
Hamma yace "ban taba jin eagerness a rayuwata irinna ranar da zaki dawo min ba. I will be patiently waiting for you and your annoying Jamb.
Daga ranar da kika dawo ne zamu fara rayuwa. Kinsan rayuwar mu ta Argentina babu komai cikin ta sai introduction na AISHA zuwa cikin lonely and pitiful rayuwar KEHINDE.
I reserved the day for you only, as I reserved myself for 43 years waiting for the day. Please Baby, ki bani dukkan go ahead da juriyar ki da zan bukata, kinji?"
Kunya kamar ta kashe Aisha. Prince ya cigaba da kashe Aisha da kalamai masu dadi yana gaya mata irin tanadin soyayyar da yayi mata daga ranar data dawo, har zuwa karshen rayuwar su.
Ashe dai Ishaq da take ji a ranta akan yana gaya mata kalamai da suke zauna mata a rai bai iya komai ba. Ga inda kalaman fatar baki kadai ke neman narkar da zuciyarta a take. Har hakan ya saka mata (nervousness) akan zuwan ranar tarewarta dinnan da Prince ke ta maimaitawa, ba tareda Prince ya san ya saka mata nervousness din ba.
A daren yau Hammah ya gaya mata maganganu masu matukar nauyi. A ciki ya gaya mata cewa throughout the 43 years of his life he had never had a sex with anyone. Waiting for her
. his dream wife.
As a hopeless romantic, ya jira zuwan true love dinsa tsayin wannan lokacin, and today, he thank the Exalted Lord Almighty for bringing her to his life.
(Duk da Haseenah ta so ta saka Prince ya kauce hanya Kehinde bai taba yin abinda ya wuce kissing na shan minti da ita ba. Wanda a yau, wancan abinda ya dan gitta a tsakaninsu ma regretting dinsa yake yi, yana kara istigfari).
Ya yarda ba wata soyayya ta kwanciyar hankali da sakewa da jin dadi mara misaltuwa kamar ta auren Sunnah.
Da sanyin muryar Prince dake kasheta da dadadan kalamai cikin kunnenta Aisha tayi barci akan wayar, sai ji yayi numfashin ta ya canza a hankali mai nuna tayi barci ta bar shi da wayarsa, batareda ta san lokacin da barcin ya sace ta ba. Shine dai yaga wayar na cigaba da reading kuma bai kara jinta ba. Dole ya kyaleta ya kwanta shima. Amma kam yau Prince yayi wahalallen barci na azaba wanda ko zamanin samartakarsa dana tashen balagarsa baiyi irinsa ba.
Firdaus ta taba gayawa Nenne a cikin gorin da Maman Kiki tayi wa Aisha harda na 'Lefe'. Ashe Nenne bata manta wannan ba abin yana tsaye a ranta.
Don haka tun ranar da suka koma Lagos ta kira Hamma Abdulrasheed suka gaisa.