Sashe 24
Abnur Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ni asalina ba ɗan ƙasar nan bane, mahaifina da mahaifiyata duka ƴan Dubai ne, ƙaddara ita ta haɗani da Yusuf a makaranta, ɗan Nigeria ne da yake karatu a Dubai, sakamakon scholarship da ya samu, tunda na haɗu da Yusuf, muka shaƙu sosai, har ya zamana kamar shine best friend ɗina, sannan ina matuƙar sha'awar Yaren Yusuf wato Hausa, da Yusuf yaga ina so, sai ya fara koya min, kasancewar ina da saurin koyan abu, cikin lokaci ƙalilan na fara gane Yaren Hausa, amma sam iyayena basason abota na da Yusuf, a ganinsu shi bak'ar fata ne, ɗan Nigeria, wanda Ni sam bai dame Ni ba.
Kullum Idan Yusuf ya tashi zuwa Nigeria ganin iyayensa, sai naji kamar na biyosa, saboda yadda nakeson ƙasar a raina, amma ina tsoron iyayena.
Ana haka sai muka gama makaranta, Yusuf yace min idan ya tafi ba lallai ne ya sake zuwa ba, alokacin na masa alƙawarin zanzo Nigeria gurinsa, Yusuf ya dinga jin daɗi.
Bayan tafiyan Yusuf, sai na rasa me zan ce ma iyayena, su barni na zo Nigeria, kasancewar Ni architecture ne yasa nace musu na samu wani contract, da zai iya ɗauka na aƙalla wata shida, a wata ƙasa, amma banyi kuskuren ce musu a Nigeria ba.
A zatona, wata shida ya isheni, in San Nigeria, da komai nata, in iya yarenta, sannan in zauna da Yusuf Abokina.
Iyayena basuyi kokonto ba, suka barni na tafi, tunda nazo Nigeria na ringa mamakin irin gidan da Yusuf ke ciki, gida ne ƙarami, mai ɗakuna biyu kacal, kuma a unguwar talakawa, hakan yasa na kama mana apartment guda muka zauna, a cikin garin Kaduna.
Kullum sai mun je mun zaga gari, mun ga abubuwa iri-iri, farinciki nakeyi sosai, kasancewar wannan shine abinda nake so.
Ana haka Yusuf yace min zaije ganin iyayensa, amma bazan iya zuwa ba, saboda a ƙauye ne, ai kuwa nace bai isaba, ko a jejine sai naje.
Haka muka shirya, muka nufi Baulawa, wanda shine ƙaddarar haɗuwa ta da Fatima.
Yusuf ɗan mai gari ne,hakan yasa muka sauƙa a gidan mai gari, amma kullum sai mun fita, ganin gari, saboda yadda garin keda matuƙar kyau.
Tun ganin farko da nayi ma Fatima a wani bikin shekara da ake yi a ƙauyen, Allah ya ɗaura min matuƙar sonta, har mamaki nakeyi, tayaya za'a yi na so ɗan Nigeria, iyayena baza su taɓa amincewa ba.
Amma babu ruwan zuciya, tun ina binta bata yarda, har itama ta fara kulani, soyayya mai matuƙar tsafta ta shiga tsakani na da ita, duk da sati ɗaya mukazo yi da Yusuf,amma sai nace masa Ni bazan tafi ba, Yusuf yayi ta min dariya, yana faɗin
"ka dai ga Æ´ar fara kyakkyawa"
sai dai kawai nayi murmushi.
Babu yadda na iya bayan mun cika kwana goma, haka na tafi na bar masoyiyata Fatima, tare da alƙawarin zan dawo idan Yusuf zai sake zuwa, dan kuwa makarantar da Yusuf ke koyarwa sun nemesa.
Hankali na bai tashi ba, sai da na yi waya da mahaifiyata, kwana biyu bayan dawowan mu daga Baulawa, ita take sanar dani wai kar nakai wata shida na dawo, za'a haÉ—ani da Æ´ar uwata Nadiya aure, saboda yadda take mutuwar sona.
A take nace mata, Ni bana sonta, amma sai ta ce min, ai sun riga sun amince.
Ƙarshe sai ce mata nayi, ai bazai yiwu in dawo ba tunda contract ne, su jira six months ɗin.
Haka suka aminci badan ransu ya so ba.
Ni na uzura ma Yusuf, muka sake komawa Baulawa.
tunda naga Fatima, nasa a raina, bazan iya rayuwa babu ita ba, kasancewar a hannun matar mahaifinta take, sam bata samun kulawa.
Ai kuwa ina zuwa na zame mata cingam, ko ina zata je sai na bita, har mutane suka fara saka mana ido.
Ranar da bazan taɓa mantawa ba, a rannan ina zazzaɓi, hakan yasa banje ko ina ba, tun safe bamu haɗu da Fatima ba.
Yusuf kuma yaje gurin mai gari, ina kwance, sai naji an buga ƙyauren a hankali, miƙewa nayi da ƙarfin hali, na buɗe, ga mamakina sai naga Fatima.
Dana ce ta shigo, sai naga kaman tana tsoro, sai nace mata babu komai ta shigo, idan bata shigo ba bazan kulata a wajen ba, dan jiri nakeji bazan iya tsayuwa ba, hakan yasa ta shigo, kwanon abinci ta ajiyemin, tace wai ta kawo min inci, murmushi nayi na É—auka ina ci muna hira da ita, amma duk ta kasa sakewa.
Can kuma sai ta miƙe tace min, ita zata tafi, hakan yasa nima na rakota ƙofa.
Mutanen da muka gani a bakin ƙofa ya sani matuƙar mamaki, dan kuwa kusan rabin ƴan garin suna bakin ƙofar mu.
Haka suka ƙeƙashe suka ce wai ɓata mata tarbiyya nakeyi ai sun jima da ganin take-takena, abun ya bani mamaki, alokacin sai ga Yusuf, shima yayi iya ƙoƙarinsa ya fahimtar da su amma sam suka ƙi fahimta, a nan take suka ce sai dai muje a ɗaura mana aure, dan su ba'a ɓata musu yara a zauna lafiya,
Bayan ɗauki ba daɗi da akayi tayi, ganin Fatima na kuka, kuma nasan Ni na janyo mata, kuma ina sonta yasa na amince, ai kuwa ba'a ɗau lokaci ba aka ɗaura mana aure wanda nake jinsa yamin banbaraƙwai, su wasu irin mutane ne, babanta bai damuba, haka ma kishiyar mahaifiyarta, washe gari muka bar ƙauyen, muka taho cikin Kaduna, anan muka zauna.
Wani irin tsabtataccen soyayya muke shimfiÉ—awa, wanda har nakejin rayuwata tafi ko yaushe daÉ—i, bana son tuno cewa wata shida nayi da mahaifana.
Kwanci tashi, har wata shida, ya wuce, amma bana tunanin komawa gida, iyayena sunyi kira har sun gaji bana É—auka, a wata na takwas na samu mail daga baba na, yayi bincike ya gano ina Nigeria, kuma idan har ban koma ba a cikin sati na gaba, shikadai yasan abinda zai min.
Nasan halin mahaifina, yana da matuƙar zuciya, hakan yasa na yanke shawaran komawa, but zan je in shayo kan iyayena, in dawo in tafi da Fatima.
Na yi ma Fatima bayanin komai, ta amince, amma ta sa nayi mata alƙawarin zan dawo gareta.
Nayi iya yi na, inga na fahimtar da iyayena, amma sam suka nuna basu san da maganar ba, har ƙoƙarin tsine min sukayi idan har na cigaba da wannan maganan.
Sannan basu ɓata lokaci ba suka ɗaura min aure da Nadiya, sannan sai da mahaifina ya tabbatar ya goge duk wani abu da zai haɗa Ni da Yusuf, bare har inji lafiyan Fatima, bayan haka, mahaifina da mahaifiyata, suka ce, idan har na taka ƙafa na a Nigeria, to wallahi bazasu taɓa yafe min ba.
na shiga wani hali, har sai da na kwanta a asibiti, amma kasancewar bani da mafita ya sa na hakura na auri Nadiya, Wanda Alhamdulillah yanzu muna da ya'ya har uku da ita.
Yusuf kam ganin kuɗin gida ya ƙare, kuma bazai iya sake biyaba, yasa ya tattara Fatima ya mayar da ita Baulawa, amma acikin kuɗi mai yawan da na bashi kafin na tafi, sai ya siya mata gida, sannan yace musu nayi tafiya ne kuma zan dawo.
Sam bansan akwai cikinki ba, ita kaÉ—ai tayi renon cikinki ta haife ki.
A yanzu haka da nake faɗa miki, mahaifiyata da mahaifina, sun rasu a wani plane crash a hanyar su ta zuwa Iraq, Amma kafin tafiyarsu sun tabbatar min zan iya zuwa Nigeria. Naji matuƙar daɗi ashe sune zasu barni, dan tafiyan da basu dawo ba kenan.
Sai dai kash, ina zuwa sai mai gari ya sanar da Ni Fatima ta rasu, ke kuma kinyi Aure.
a wajensa na samu hoton ki, na bazama nemanki, amma na rasa ki, sai bawan Allah khamal ya kirani yace kina wajensa."
Ya faÉ—a ya share hawayen idanunsa.
Itakam Noor kuka take wiwi, ita kanta Nadiya kuka takeyi, dan bai taɓa bata labari ba, kenan Nenne yake zanawa duk kwanan duniya?
A hankali ta taso ta É—ago Noor tana faÉ—in
"kiyi haƙuri Noor, insha Allah zan maye miki gurbin Nenne."
Da mamaki yake kallonta, kafin yayi murmushi yace
"Nadiya na gode."
Sai da suka É—an lafa, kafin ta sake basu labarin tasowarta da rasuwar Nenne, zuwa aurenta da Zannur har kawo yau.
Duk shiru sukayi suna jinjina al'amarin, kafin Noor tace
"To papi Ammi da su Farhaana kuma a ina suka iya Hausa?"
Murmushi Ammi tayi tana faÉ—in
"ai kowa ya zauna da shi sai ya iya Hausa, sai da ya tabbatar mun iya"
ta faÉ—a tana dariya,
Shima dariyar yayi.
A ranan sun wuni cikin farinciki a gidan, jifa jifa takan tuno Zannur, amma sai ta kauda a ranta, dan bataso tana tunoshi.
Rayuwar Noor a gidan iyayenta, rayuwa ce mai cike da kulawa, gata, da soyayyah, babu abinda ta nema ta rasa, hakan yasa ta sake kyau, ta sake zama Æ´ar gayu, dan kuwa, Ammi basuga wannan shopping center É—in, basuga wannan.
Zannur kam.......
Maimoon#
*💖*ABNUR*💖*
*By Maimoon*
*Elegant online writers* 📚📖
*Page 22*
Zannur kam, gaba É—aya ya rasa me ke masa daÉ—i, ya canza kamar ba shine Zannur the master of All ba, tun Maami na É—auka da wasa, har hankalinta ya soma tashi, kwata kwata ya daina walwala, ko magana ba yayi sai dole.
sometimes Maami har kuka takeyi, sai dai Abbu ya rarrasheta, zuwa yanzu shima abin ya fara damunsa.
Yasira ta rasa yanda zatayi, gabaÉ—aya komai ya kufce mata, ita sam ba haka ta so ba, to yaushe ma Zannur ya soma son Noor har haka?, lallai tayi mugun sake.
Amina da Asabe kansu sun rage walwala, da yake yanzu Amina ce chief of kitchen staffs, kullum ta gansa, cikin damuwa take ganinsa, duk da cewa a da ma ba wani shiga harkarsu yakeyi ba, sai dai TaufeeÆ™, amma yanzu daga shi har TaufeeÆ™ sun zama wasu iri, hakan yasa gidan kowa baya cikin farinciki.
*******
"Habibi wai meyasa yanzu baka jin maganata ne?, rabonka da abinci tun yaushe?, Please Habibi kaci abinci kaji?" ta faÉ—a da alamun damuwa a tattare da ita
Bai ɗago ba, bare tasa ran zai tanka, hakan yasa ta ajiye tray ɗin akan center table na ɗakin ta juya ta bar ɗakin tare da ja masa ƙofa.
Kullum Idan Yusuf ya tashi zuwa Nigeria ganin iyayensa, sai naji kamar na biyosa, saboda yadda nakeson ƙasar a raina, amma ina tsoron iyayena.
Ana haka sai muka gama makaranta, Yusuf yace min idan ya tafi ba lallai ne ya sake zuwa ba, alokacin na masa alƙawarin zanzo Nigeria gurinsa, Yusuf ya dinga jin daɗi.
Bayan tafiyan Yusuf, sai na rasa me zan ce ma iyayena, su barni na zo Nigeria, kasancewar Ni architecture ne yasa nace musu na samu wani contract, da zai iya ɗauka na aƙalla wata shida, a wata ƙasa, amma banyi kuskuren ce musu a Nigeria ba.
A zatona, wata shida ya isheni, in San Nigeria, da komai nata, in iya yarenta, sannan in zauna da Yusuf Abokina.
Iyayena basuyi kokonto ba, suka barni na tafi, tunda nazo Nigeria na ringa mamakin irin gidan da Yusuf ke ciki, gida ne ƙarami, mai ɗakuna biyu kacal, kuma a unguwar talakawa, hakan yasa na kama mana apartment guda muka zauna, a cikin garin Kaduna.
Kullum sai mun je mun zaga gari, mun ga abubuwa iri-iri, farinciki nakeyi sosai, kasancewar wannan shine abinda nake so.
Ana haka Yusuf yace min zaije ganin iyayensa, amma bazan iya zuwa ba, saboda a ƙauye ne, ai kuwa nace bai isaba, ko a jejine sai naje.
Haka muka shirya, muka nufi Baulawa, wanda shine ƙaddarar haɗuwa ta da Fatima.
Yusuf ɗan mai gari ne,hakan yasa muka sauƙa a gidan mai gari, amma kullum sai mun fita, ganin gari, saboda yadda garin keda matuƙar kyau.
Tun ganin farko da nayi ma Fatima a wani bikin shekara da ake yi a ƙauyen, Allah ya ɗaura min matuƙar sonta, har mamaki nakeyi, tayaya za'a yi na so ɗan Nigeria, iyayena baza su taɓa amincewa ba.
Amma babu ruwan zuciya, tun ina binta bata yarda, har itama ta fara kulani, soyayya mai matuƙar tsafta ta shiga tsakani na da ita, duk da sati ɗaya mukazo yi da Yusuf,amma sai nace masa Ni bazan tafi ba, Yusuf yayi ta min dariya, yana faɗin
"ka dai ga Æ´ar fara kyakkyawa"
sai dai kawai nayi murmushi.
Babu yadda na iya bayan mun cika kwana goma, haka na tafi na bar masoyiyata Fatima, tare da alƙawarin zan dawo idan Yusuf zai sake zuwa, dan kuwa makarantar da Yusuf ke koyarwa sun nemesa.
Hankali na bai tashi ba, sai da na yi waya da mahaifiyata, kwana biyu bayan dawowan mu daga Baulawa, ita take sanar dani wai kar nakai wata shida na dawo, za'a haÉ—ani da Æ´ar uwata Nadiya aure, saboda yadda take mutuwar sona.
A take nace mata, Ni bana sonta, amma sai ta ce min, ai sun riga sun amince.
Ƙarshe sai ce mata nayi, ai bazai yiwu in dawo ba tunda contract ne, su jira six months ɗin.
Haka suka aminci badan ransu ya so ba.
Ni na uzura ma Yusuf, muka sake komawa Baulawa.
tunda naga Fatima, nasa a raina, bazan iya rayuwa babu ita ba, kasancewar a hannun matar mahaifinta take, sam bata samun kulawa.
Ai kuwa ina zuwa na zame mata cingam, ko ina zata je sai na bita, har mutane suka fara saka mana ido.
Ranar da bazan taɓa mantawa ba, a rannan ina zazzaɓi, hakan yasa banje ko ina ba, tun safe bamu haɗu da Fatima ba.
Yusuf kuma yaje gurin mai gari, ina kwance, sai naji an buga ƙyauren a hankali, miƙewa nayi da ƙarfin hali, na buɗe, ga mamakina sai naga Fatima.
Dana ce ta shigo, sai naga kaman tana tsoro, sai nace mata babu komai ta shigo, idan bata shigo ba bazan kulata a wajen ba, dan jiri nakeji bazan iya tsayuwa ba, hakan yasa ta shigo, kwanon abinci ta ajiyemin, tace wai ta kawo min inci, murmushi nayi na É—auka ina ci muna hira da ita, amma duk ta kasa sakewa.
Can kuma sai ta miƙe tace min, ita zata tafi, hakan yasa nima na rakota ƙofa.
Mutanen da muka gani a bakin ƙofa ya sani matuƙar mamaki, dan kuwa kusan rabin ƴan garin suna bakin ƙofar mu.
Haka suka ƙeƙashe suka ce wai ɓata mata tarbiyya nakeyi ai sun jima da ganin take-takena, abun ya bani mamaki, alokacin sai ga Yusuf, shima yayi iya ƙoƙarinsa ya fahimtar da su amma sam suka ƙi fahimta, a nan take suka ce sai dai muje a ɗaura mana aure, dan su ba'a ɓata musu yara a zauna lafiya,
Bayan ɗauki ba daɗi da akayi tayi, ganin Fatima na kuka, kuma nasan Ni na janyo mata, kuma ina sonta yasa na amince, ai kuwa ba'a ɗau lokaci ba aka ɗaura mana aure wanda nake jinsa yamin banbaraƙwai, su wasu irin mutane ne, babanta bai damuba, haka ma kishiyar mahaifiyarta, washe gari muka bar ƙauyen, muka taho cikin Kaduna, anan muka zauna.
Wani irin tsabtataccen soyayya muke shimfiÉ—awa, wanda har nakejin rayuwata tafi ko yaushe daÉ—i, bana son tuno cewa wata shida nayi da mahaifana.
Kwanci tashi, har wata shida, ya wuce, amma bana tunanin komawa gida, iyayena sunyi kira har sun gaji bana É—auka, a wata na takwas na samu mail daga baba na, yayi bincike ya gano ina Nigeria, kuma idan har ban koma ba a cikin sati na gaba, shikadai yasan abinda zai min.
Nasan halin mahaifina, yana da matuƙar zuciya, hakan yasa na yanke shawaran komawa, but zan je in shayo kan iyayena, in dawo in tafi da Fatima.
Na yi ma Fatima bayanin komai, ta amince, amma ta sa nayi mata alƙawarin zan dawo gareta.
Nayi iya yi na, inga na fahimtar da iyayena, amma sam suka nuna basu san da maganar ba, har ƙoƙarin tsine min sukayi idan har na cigaba da wannan maganan.
Sannan basu ɓata lokaci ba suka ɗaura min aure da Nadiya, sannan sai da mahaifina ya tabbatar ya goge duk wani abu da zai haɗa Ni da Yusuf, bare har inji lafiyan Fatima, bayan haka, mahaifina da mahaifiyata, suka ce, idan har na taka ƙafa na a Nigeria, to wallahi bazasu taɓa yafe min ba.
na shiga wani hali, har sai da na kwanta a asibiti, amma kasancewar bani da mafita ya sa na hakura na auri Nadiya, Wanda Alhamdulillah yanzu muna da ya'ya har uku da ita.
Yusuf kam ganin kuɗin gida ya ƙare, kuma bazai iya sake biyaba, yasa ya tattara Fatima ya mayar da ita Baulawa, amma acikin kuɗi mai yawan da na bashi kafin na tafi, sai ya siya mata gida, sannan yace musu nayi tafiya ne kuma zan dawo.
Sam bansan akwai cikinki ba, ita kaÉ—ai tayi renon cikinki ta haife ki.
A yanzu haka da nake faɗa miki, mahaifiyata da mahaifina, sun rasu a wani plane crash a hanyar su ta zuwa Iraq, Amma kafin tafiyarsu sun tabbatar min zan iya zuwa Nigeria. Naji matuƙar daɗi ashe sune zasu barni, dan tafiyan da basu dawo ba kenan.
Sai dai kash, ina zuwa sai mai gari ya sanar da Ni Fatima ta rasu, ke kuma kinyi Aure.
a wajensa na samu hoton ki, na bazama nemanki, amma na rasa ki, sai bawan Allah khamal ya kirani yace kina wajensa."
Ya faÉ—a ya share hawayen idanunsa.
Itakam Noor kuka take wiwi, ita kanta Nadiya kuka takeyi, dan bai taɓa bata labari ba, kenan Nenne yake zanawa duk kwanan duniya?
A hankali ta taso ta É—ago Noor tana faÉ—in
"kiyi haƙuri Noor, insha Allah zan maye miki gurbin Nenne."
Da mamaki yake kallonta, kafin yayi murmushi yace
"Nadiya na gode."
Sai da suka É—an lafa, kafin ta sake basu labarin tasowarta da rasuwar Nenne, zuwa aurenta da Zannur har kawo yau.
Duk shiru sukayi suna jinjina al'amarin, kafin Noor tace
"To papi Ammi da su Farhaana kuma a ina suka iya Hausa?"
Murmushi Ammi tayi tana faÉ—in
"ai kowa ya zauna da shi sai ya iya Hausa, sai da ya tabbatar mun iya"
ta faÉ—a tana dariya,
Shima dariyar yayi.
A ranan sun wuni cikin farinciki a gidan, jifa jifa takan tuno Zannur, amma sai ta kauda a ranta, dan bataso tana tunoshi.
Rayuwar Noor a gidan iyayenta, rayuwa ce mai cike da kulawa, gata, da soyayyah, babu abinda ta nema ta rasa, hakan yasa ta sake kyau, ta sake zama Æ´ar gayu, dan kuwa, Ammi basuga wannan shopping center É—in, basuga wannan.
Zannur kam.......
Maimoon#
*💖*ABNUR*💖*
*By Maimoon*
*Elegant online writers* 📚📖
*Page 22*
Zannur kam, gaba É—aya ya rasa me ke masa daÉ—i, ya canza kamar ba shine Zannur the master of All ba, tun Maami na É—auka da wasa, har hankalinta ya soma tashi, kwata kwata ya daina walwala, ko magana ba yayi sai dole.
sometimes Maami har kuka takeyi, sai dai Abbu ya rarrasheta, zuwa yanzu shima abin ya fara damunsa.
Yasira ta rasa yanda zatayi, gabaÉ—aya komai ya kufce mata, ita sam ba haka ta so ba, to yaushe ma Zannur ya soma son Noor har haka?, lallai tayi mugun sake.
Amina da Asabe kansu sun rage walwala, da yake yanzu Amina ce chief of kitchen staffs, kullum ta gansa, cikin damuwa take ganinsa, duk da cewa a da ma ba wani shiga harkarsu yakeyi ba, sai dai TaufeeÆ™, amma yanzu daga shi har TaufeeÆ™ sun zama wasu iri, hakan yasa gidan kowa baya cikin farinciki.
*******
"Habibi wai meyasa yanzu baka jin maganata ne?, rabonka da abinci tun yaushe?, Please Habibi kaci abinci kaji?" ta faÉ—a da alamun damuwa a tattare da ita
Bai ɗago ba, bare tasa ran zai tanka, hakan yasa ta ajiye tray ɗin akan center table na ɗakin ta juya ta bar ɗakin tare da ja masa ƙofa.