← Book details Abnur Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 28

Sashe 21

Abnur Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"hakane, amma duk da haka ai bazamu biye mata ba, yarintace kawai ke damunta, amma shima yaron dole na zauna dashi, kafin na bashi Noor, dole ne a aure ya zama akwai cikakken yarda da aminci, ai ba'a haka, yanzu so nake mu cire anfanin gona, idan mun siyar, kuÉ—in sai muyi anfani dashi mu maidata gidan mijinta, dan shine mutuncinta."

"Hakane kam Malam, Allah dai ya saka maka da alkhairi."

"Ya saka mana gaba É—aya uwar Æ´aÆ´ana"

ya faÉ—a yana kallonta da murmushi.

Itama Murmushin tayi tana miƙewa tace bari

"naje na ƙarasa girki."

Daga haka ta fice a É—akin.

***********

*_Kaduna Nigeria*_

What? Papi ya faɗa yana miƙewa tsaye,

"banganeba, me kake nufi?, papi ya faÉ—a yana ja da baya,

"Abinda kunnuwanka suka jiye maka nake faÉ—a."

Mai gari ya faɗa yana miƙewa shima.

"Yarinyar nan da ka gudu ka bari, ta rasu shekara biyu kenan sannan Æ´arta tayi aure, ta auri wani É—an Balarabe É—an birni da ya zo garinnan, ya tafi da ita mu kan mu bamu san ina ya tafi da ita ba."

Girgiza kai papi ya shiga yi idanunsa sun kaÉ—a sunyi jajir

"Kana nufin Fatima tana É—auke da cikina sanda na tafi na barta?, kana nufin ina da wata Æ´ar bayan su farhaana?, pleaaaaase ku faÉ—a min ina Æ´ata take É—an Allah, ita É—in jinin Fatima ce, matar da nafi so fiye da kowa a duniya."

A fusace Ammi ta miƙe tana faɗin,

" ba sai ka cigaba da maimaita cewa baka sona a gaban kowa ba razaÆ™ Abdulkarim, laifina ne dana so ka, sannan na biyoka Nigeria."

Daga haka ta miƙe daga kan tabarmar da take, tana riƙe hannun sudais,ta bar wajen.

Kasa cewa komai papi yayi, sai wasu zafafan hawaye dake sauƙa akan fuskarsa.

Farhaana ce ta ƙaraso inda yake, a hankali tace

"Papi zamu sameta insha Allahu, zamu nemo ƴar uwata a duk inda take a duniya, kuma Ammi zata sauƙo, but Please papi Kar kayi kuka."

Rungume ta kawai yayi, baice komai ba, shi kaɗai yasan me yake ji a cikin ƙirjinsa.

A hankali ya É—ago jajayen idanunsa, yana kallon mai gari,

"Dan Allah ko kuna da koda hoton Æ´a ta ne, zan nemo ta duk inda ta shiga a duniya."

ya faɗa yana share hawayen da ya sauƙo masa.

Shiru mai gari yayi kafin yace,

"ai kuwa kayi matuƙar Sa'a, dan kuwa yaron da ya aure tan yana ɗaukan hoto, kuma bikin shekaran da akayi,
a shekaran da yazo garinnan ya musu hotunan, ina tunanin Noor É—in na ciki, kuma ya kawo min wasu daga cikin hotunan, bari dai na duba, dan kuwa na adanasu dan tarihi ne."

"Noor!" papi ya maimaita sunan,

*kenan sunan Æ´ata da Fatima ta haifamin Noor"
sai kuma ya lumshe ido, sabbin hawaye na zirya akan farar kyakkyawar fuskarsa.

Miƙewa mai gari yayi, ya nufi cikin gida, can kuma sai gashi ya dawo da hotuna a hannunsa, sai da ya kalli hoton yaga da Noor kafin yayi wani Murmushi,

"aikuwa harda ita a ciki amma dai kam sai ka siya, dan bazan baka kyauta ba."

Da sauri papi yace

"zan siya ko da ace da dukkan kuÉ—in dana mallaka ne, pleaaaaase ka bani inga Æ´a ta."

"Ah ah sai na fara ganin kuÉ—in"

da sauri ya miƙe yana zaro dukkanin kuɗin aljihunsa yana zube su gaban mai gari

"Idan basu isa ba, zan ƙara maka, akwai wasu a mota, a can mukayi parking sai naje na ƙaro maka."

papi ya faɗa yana miƙewa tsaye da alama baya cikin hayyacinsa.

Zaro ido mai gari yayi ganin bandir É—in kuÉ—i har huÉ—u, ai baisan sanda ya watsar da hoton ba ya rungumi kuÉ—aÉ—e,

tsugunnawa papi yayi ya É—au hoton yana kallo.

"Subhanallah, laa haula wala ƙuwwata illa Billah."

Babu inda Noor ta barsa, sai dai yanayi na Fatima data É—auko.

Wasu hawaye Masu ɗumi ne suka wanke masa fuska, kafin ya miƙe, ba tareda yabi ta kan mai gari ba ya juya ya bar wajen Farhaana na biye dashi.

A jikin mota suka tarar da Ammi, ta cika tayi pam.

Bai bi takanta ba ya shiga Mota, suma shiga sukayi kafin ya tada motar ya bar garin gabaki É—aya, a zuciyarsa yana tunanin ta inda zai fara neman Noor!.

************

Idan akwai abinda yafi tashi hankali, Zannur ya shigesa, gaba É—aya ya rasa sukuni, ya rame, kamar ba Zannur ba, sai suma da ya tara har ya masa yawa.

Aƙalla yau watan Noor uku kenan babu ita babu labarin ta, yayi Neman har ya fara cire rai.

An sallami TaufeeÆ™ a asibiti, bayan jinya da yayi, a yanzu ya warke rass, sai dai baya cewa komai, sai an daÉ—e yake buÉ—e baki ya ce wani abu,

gaba ɗaya Zannur ya fita hayyacinsa, a yanzu ya ma daina neman wanda ya yi yunƙurin kashe Taufeeƙ, gabaki ɗaya hankalinsa naga inda zai ga Noor.

Yasira kam, komai ya jagule mata, dan kuwa Zannur ya koreta a aiki a matsayin chief staff na kitchen, hakan yana nufin, batada hurumin zuwa inda yake, sai dai zata zauna a gidan albarkacin TaufeeÆ™, sai dai batada hurumi da mai gidan, dama da hakan take fakewa tana kallonsa tana jin sanyi a ranta, gashi yanzu TaufeeÆ™ ya toshe duk wata hanya da zata gansa, kwata kwata,

gabaɗaya tá rasa mai zatayi, tsoronta kaɗai kar ya faɗama Zannur, duk da a halin da Zannur yake a yanzu, bazai saurari kowa ba, dole ne tayi gaggawan ɗaukan mataki, kafin lokaci ya ƙure mata.

Yauma, a zaune Zannur yake a dakin Noor, Wanda ya jima da tarewa anan, Camera ne a gabansa, ya zuba ma hotunan ta ido yana kallo ko ƙiftawa bayayi.

Gashin kansa ya sauƙa gefe da gefen fuskar sa, he look pale, but duk da haka ya ƙara haske da wani irin kyau kamar wanda yake cikin kwanciyar hankali, ramar dayayi ne kaɗai zai tabbatar maka da halin da yake ciki.

"Habibi!" yaji an faɗa da ƙarfi

ÆŠagowa yayi yana kallon Maami with suprise Dan baisan zatazo ba, Abbu da ya gani a kusa da Maami sai ya sake basa mamaki, amma sai baice komai ba, ya mayar da kansa wasu hawaye na taruwa a idanunsa.

Da sauri Maami ta yasar da jakanta, tana ƙarasowa gabansa, ɗago fuskarsa tayi

"Habibi talk to me, miye duka hakan?, TaufeeÆ™ ya kira mu yace muzo bakada lafiya me ya sameka, kaga yanda ka rame kuwa rabin raina?, meyasa bazaka faÉ—a wa Maami ba?."

Kasa cewa komai yayi, kawai dai ya rungume ta sosai yana sauƙe ajiyar zuciya.

A hankali ya buɗe bakinsa daya ƙafe yana faɗin

"Maami Noor ta tafi ta barni, Maami bansan ta ina zan fara nemanta ba, Maami where can I find Noor?, I need to apologise, idan wani abu ya sameta bazan yafewa kaina ba.

Shafa kansa tayi tana faÉ—in

"Habibi calm down, TaufeeÆ™ ya faÉ—a min komai, zamu sameta da izinin Ubangiji, ka kwantar da hankalinka."

cigaba tayi da shafa kansa, har taji sauƙar numfashinsa alamun bacci ya ɗauke sa, a hankali ta gyara masa kwanciyarsa a kan gadon.

Hannunta ta sa a cikin na Abbu dake miƙa mata hannunsa.

A hankali ya miƙar da ita suka fice a ɗakin, suka nufi ɗakin Maami, sai da suka isa ɗakin kafin Maami ta fashe da kuka

"Abbu ka ga Habibina kuwa?, meyasa Noor ta tafi tanar min yarona a haka?, kashe min shi takeso tayi ne?.

Ta faÉ—a tana sake fashewa da kuka.

rungumeta Abbu yayi yana shafa kanta, karki damu Hilwa, Zannur will be alright, kuma za'a sami yarinyar, ki kwantar da hankalinki Please."

Haka Abbu yayi ta rarrashin Maami, har sai da yaga ta samu nutsuwa kafin shima nashi hankalin ya kwanta.

************

Khamal ne ya shigo gidan yauma da saurinsa, da jarida a hannunsa, tun daga tsakar gida yake ƙwala kiran

"Noor! Noor! Ina kike?

A tare suka fito da umma, jin kiran yaƙi ƙarewa

"Khamal lafiyanka?"

Umma ta tambaya tana kallonsa.

"Umma bayan mijin Noor da ke nemanta, yau kuma wani ne yake nemanta, wanda yake ikirarin shi mahaifinta ne, gashinan dai hotonta ne ɓaro ɓaro akan jaridar, sannan yasa kuɗi mai tsoka ga duk wanda ya san koda labarinta ne."

Ya karashe zancen yana mikawa umma hoton.

A hankali Noor ta jawo ƙafar ta ta ƙara so gaban Umma, hannu ta saka ta amshi jaridan tana kallo sai kuma tayi wani murmushi tana tafa hannunta

"Kai a tunaninka kana da wayo ko?, umma ba fa mahaifina bane, Zannur ne zai raina min wayo, shine kaÉ—ai yake da wannan hoton, shine ya É—aukeni, ta yaya za'a yi mahaifina da koni kaina bansansaba zai samu wannan hoton, a tunaninsa idan yace mahaifina zan dawo ne hmmm."

sai kuma ta ajiye jaridar ta yi wucewarta É—aki

Daga khamal har umma da kallo kawai suka bita, kafin khamal yace,

"Ummah kina ganin a barta kawai?, a gaskiya Nikam zan kira numbar da aka saka dan nemanta, in sanar dasu inda take, idan ma mijinnata ne gwara yazo a sasanta komai ta koma gidanta ko ya kuka ce."

"To khamal me zance maka, ka dai jira Malam ya dawo muji ta bakinsa koh?"

Bai sake cewa komai ba ya juya ya bar gidan.

Maimoon#

*💖ABNUR💖*

*By Maimoon*

*Elegant online writers* 📚📖

*Page 20*

Kamar yadda Umma tace kuwa, Baba na dawowa, khamal ya zo ya samesa da maganan

"Khamal gaskiya kayi tunani mai kyau, amma kaÉ—an jira kaÉ—an,yarinyar tana cikin damuwa, kuma nima ina tunanin mijin nata ne yace mahaifinta, dan yasan zata so haÉ—uwa da mahaifinta."

"Shikenan Baba, babu damuwa, duk sanda kuka ga ya dace a sanar da su, sai a sanar dasu."

"Yauwa khamal Allah yayi maka albarka."

"Ameen Baba" daga haka yayi ma Baba sallama ya bar É—akin.

**********

"Abdul kaji yadda mukayi da Baba, Amma gaskiya ya kamata ta koma ga mijin ta, bana tunanin zamanta anan shi yafi"
khamal ya faÉ—a yana kallon Abdul da ke zaune a gefensa ya zuba masa ido.

Gyara zama Abdul yayi kafin yace

"to kai miye damuwarka ne, tunda ba akanka take ba, ka barta mana ai zasu maidata koh?"
Chapter 21 · 0% Book details