← Book details Abin Cikin Kwai Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 53 OF 63

Sashe 53

Abin Cikin Kwai Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wayata naji tana ƙara ina ɗauka naga baƙuwar number ce na ɗaga.muryar Shahid naji yana ce wa to khairat na je har wajen aikin Abbinku ya bani damar tsayawa da ke."sosai na yi mamakin daya sanni haka ina cikin mamakin ya ce"leƙo ina ƙofar gida."

Da sauri na yi hanyar waje ina fita na gansa a ƙofar gidanmu,ya yi wani irin mugun kyau cikin irin kayanmu na hausawa shadda ya saka baƙa me mugun tsada da kyau,kasancewarsa fari sosai ba ƙaramin kyau suka yi masa ba,na ƙarasa inda ya ke a hankali ina murmushi.shima murmushin ya mayar min sannan ya ce"our wlcm my Hayatee".

dai dai nan motar Yaya Bilal ta sanyo kai yaci wani irin mugun burki ya fito,idanuwansa duk sun ƙanƙance saboda ji da masifa.

*Sirrinki*

RAGE KIBA DA TUMBI DA GURJI DA SAURAN AMFANINSA

Gurji na dauke da sinadaran magance gautsin fata sannan yana taimakawa wajen sanya fata sheki da laushi. Kashi casa’in da biyar na gurji na dauke da ruwa don haka yana da kyau a kasance wajen cin gurji domin samun lafiyar jiki da kuma maikon da ke toshe magudar gumi wadda hakan yakan haifar da fesowar kuraje wadda sai an dage kafin a rabu da su. Wannan kayan lambun na taimakawa wajen rage kiba ga mace idan har ta kasance cin sa shi kadai da kuma rage cin abinci masu nauyi wadanda ke gina jiki.

MATAKAI:  

1)-Domin rage kiba ko tumbi; a samu gurji sannan a fere bawonsa sannan a yayyanka shi kanana sannan a zuba a na’urar markade a markada shi sai a tace ruwansa sannan a zuba cokali biyu na zuma a ciki sannan a zuba a kwalba a jijjiga kwalbar. Sannan a hada da ruwan lemun tsami da citta sai a rika sha yana rage kiba da tumbi.

2)- kurajen fuska; a markada gurji da ruwa zalla bayan an fere bawonsa sannan a samu auduga a rika shafawa  a fuska sau biyu a rana domin magance kurajen fuska da kuma sanya sulbin fata.

3)- Hasken fata; a markada gurji sannan a matse ruwan lemun tsami a ciki a rika shafawa a fuska da wuya kamar sau biyu a rana ya yi a kalla mintuna goma sha biyar kafin a wanke a kullum.

4)- Kodewar fata; a markada gurji sannan a zuba kindirmo da garin alkama cokula biyu sannan a kwaba a rika shafawa a inda fatar ta kode sakamakon kunar rana ko yawan shiga rana. A bari a fuska na tsawon mintuna goma sha biyar kafin a wanke.

5)- Yankunewar fata; a markada ruwan gurjin sannan a samu kwai a cire kwanduwar ayi amfani da farin ruwan a ciki sannan a matse lemun tsami a kwaba a rika shafawa a wajajen da fatar ta yankune. Sannan a bari na tsawon mintuna talatin kafin a wanke. Ana so a rika yin wannan hadin kamar sau biyu a rana a kullum.

6)- Domin samun gashi mai tsayi; a markada gurji da ruwa sannan a tsaga gashin kai a shafa a fatar har a cikin gashin kai ya ji sosai. Sannan a samu leda a rufe kan na tsawon mintuna talatin kafin a wanke da man wanke gashi. Yin hakan na dada tsayin gashi a kai.

 

*Miss green ce*
[23/09, 16:30] Miss Green🍀: 91. . . . . . .92

. . . . . . .nunawa na yi kamar bansan abinda suke ba,na yi wuce wata gaba zuwa wajsn masoyi na,fuskata Ɗauke da murmushi,wani irin kallo me cike da soyayya ya ke yimin yadda yaga na komar kamar Ƴar shekara goma yarinta na ta Ƙara fitowa sosai,ga wani irin mugun Ƙamshin dana ke fitarwa me gigita namiji,ai kuwa shahid ya gigice Ɗin sosai amman duk da haka hankalinsa na kan Bilal wanda ya Ɗaga iman sama yana yi mata wasa.

Ya ce"hayatee wannan shine baban lovely children ÆŠina"?.sosai gabana ya faÆŠi ahankali na ce"eh shine na manta ban faÆŠa maka ba,yaya ya ke gare ni".sai naga fuskarsa ta haÆŠe nan da nan,na lura shahid shima namijin kishi ne sosai,daman kuma ance larabawa sunfi kowa kishi.

Ya ce"ayya kada ki damu don na tambaye ki ki yi haƘuri,amman wannan yayan na ki wata macece za ta ce bata sonshi?babu abinda Allah bai yi Masa ba,amman na yi mamakin rabuwarku,kuma kema khairat nasan ba zai so rabuwa da ke ba,sai dai Ƙaddara amman duk namijin daya sakeki khairat wallahi ya yi asara gaskiya".

Murmushi kawai Na yi don bani da amsar da zan bashi,don kada yabi inda muke sai ya Ɗauki Ƴarsa suka yi gaba abinsu.Ina jinsa yana tambayarta Ƴan uwanta,sai kuwa iman ta ce"dady mamanmu ta Ƙara yi mana wani dadyn ka ganchi cen ma".ta fara nuno inda Muke.Bilal bai san lokacin da wasu hawaye masu zafi suka fara zubo masa ba ya yi saurin gogewa ya wuce.

to ranar dai da Ƙer shahid ya barni na wuce gida na lura bai gajiya da kallona,idan na biye masa kuma sai muyi ta tsayuwa awajen,don haka na ce"habibee ni zan tafi gida fa mun daƊe".na faƊi hakan cikin shagwaƁa,sosai na burgesa ya ce"ah lallai baki so kije gida yanzu,ni wannan shagwaƁar taki tafi komai tafiya dani",yauwa khairat ki yi haƘuri ni dinner bata cikin tsarina sam,duk kuwa kuƊin da na ke dashi,amman mu al'adarmu a musulunce shine bayan anyi aure ana walima washe gari,to ni dai hakan yafi Ƙwantamin".

murmushi na yi sannan na ce"kada Ka damu nima duk wannan bidi'ar bata gabana albarkar auren shi na keso".sosai na burgesa amman fa muna cikin zancen naji alert Ɗin kuƊi awayata na ce"habibee naga ka turomin kuƊi me zanyi dasu haka"?.murmushi ya yi sannan ya ce"ki yi wani abin dasu,amarya ta me sirrin kyau".ya faƊi hakan yana murmushi,bai bani damar Ƙara magana ba ya yi shigewarsa cikin mota ya yi gaba.

Sosai na keson shahid,ba don kuƊinsa ko kyau ba,a'ah sai don tsare mutuncinsa,sam bai taƁa koda taƁa hannuna da sunan wasa ba,balle kuma wata maganar banza,muna mutunta kanmu mu duka,anan na ke jan hankalin Ƴan mata da zawarawa adinga riƘe mutunci da kyau,saboda ke mace duk abinda ki ka yi bai Ɓoyuwa namiji kuwa ko zai yi sau Ɗari ba'a Ganewa,kuma a musulunce ma hakan sam ba shida kyau kuma ma ba tarbiyya bace.kuma matuƘar ki ka sadaukar da mutuncinki ga wani to fa wannan mijin koda tare ku ka yi lalatar bazai taƁa ganin darajarki ba,balle kuma akaiga zancen mutuntawa,don shi aure anfison ayisa da ganin mutuncin juna.

da kai na na ware kuƊi masu yawa aka sakewa hajiya kaka sabbin kayan Ɗaki aka yi mata sabon fenti,mama na itama aka sake yi mata furnitures duk da basu daƊe ba,sannan mama ta faƊawa babana duk kuƊin da shahid ya ke bani,baiyi mamaki ba ko kaƊan don yaron yasan tarihinsa tun farko har zuwa yanzu,mahaifiyarsa da mahaifinsa suna da kuƊi sosai kuƊi kuma masu mugun yawa,shi da kansa shahid a iya nigeria ma yana da company's sunfi ashirin,ga kuma na Ƙasashen waje,uwa uba kuma likita ne me zaman kansa me kuma lasisin kowacce Ƙasa,likitan zuciya ne shi,mahaifiyarshi kuma unguwar xoma ce.kuma ba Ƙaramin kuƊi suke samu ba.

ranar daya rage saura Ƙwana biyu gidanmu ya cika Ɓam kamar auren budurwa,son hatta ankon biki,sai da shahid ya turomin kuƊi wai abawa kowa,wai su haka suke yi naƘi amsa sai gashi ya lallaƁa yaje wajen hajiya kaka,itama da farko taƘi amsa amman da taga ransa ya Ɓaci sai ta amsa,ai kuwa kowa sai daya samu ankon biki,ranar Ne kuma amminsa tazo gidanmu mata mai mutunci da sanin darajar mutane,ta Ɗakko wata mata wai za ta yimin gyaran jiki na larabawa.

daga ganin matar ma balarabiya ce wataƘil Ɗakkota aka yi,,harda Ƙanwarta tazo ita ammin,duk suna da mutunci sosai naƘi fitowa wai ina jin kunyarsu ta ce"a'ah khairat mufa bama jin wannan kunyar gwarama tun yanzu ki saba don shahid ba shida kunya wallahi".murmushi kawai na yi ai kuwa aranar aka fara yimin gyaran jikin,wowo hmm wai ko tsagar gida ma hanani fita matar ta yi sai dai ina Ɗaki ina shan a/c,Mutanen gidanmu suka dinga zuwa ganin ammin shahid,shima tun daga ranar ammin ta hanashi xuwa saboda gudun saƁawa Allah don taga yadda Ƙirar khairat Ɗin take,ba kowani namiji ne xai iya kallonta ya kyale ba,duk da ta yarda da Ɗanta mutum ne me kana kansa sosai,da tsantsae tsoron Allah,,shiyasa a kullum take godewa Allah da kyautar da ya yi mata na samun Ɗa kamar shahid,daman kuma ba yawan yara akeso ba albarkarsu ake nema.

kullum muna maƘale awaya ni da shahid ana zuba soyayya na lura su larabawa mayun soyayya ne,kamar laila majnun.

Baba na ya saka aka kirawo masa Bilal ya ce"Bilal kasan me yasa nasa ka aka kirawomin kai?".girgiza kawai ya yi,idanuwansa sunyi ciki duk ya rame abin tausayi ya ce"ina son ka yarda da Ƙaddara me kyau ko mara kyau,ka cire komai aranka kamar ma ba'ayi ba,kai Ɗinnan dai yayan khairat ne kuma uban ƳaƳanta har huƊu,to kaga aƘwau akaƘa me Ƙarfi a tsakaninku,don haka yanzu ma na kiraka ne don ka zamo waliyyin khairat,don ance babban wa uba koda ace yanzu mu faƊi mu mutu kai ne babansu su duka".

sosai wata zufa ta shiga tsattsafo masa,ya goge ta cikin dauriya da Ƙarfin hali ya ce"ba bu komai baba na gode da bani shawara da ka yi."baba yaji daƊi sosai suka cigaba da hirarsu amman can cikin zuciyarsa yana jin wani abu yana yi masa yawo sosai,ranar dai Bilal kusan Ƙwanan zaune ya yi,saboda tsananin tashin hankali,gobe khairat Ɗinsa xa ta Ɗaura aure?da wani ba shi ba?za ta tafi gidan wani?yanzu shikkenan sun rabu har abadan?tuni ya dinga kuka kamar ba shi ba,tabbas yanzu yaga illar rashin yin bincike kafin Ɗaukar mataki,kuma yanzu yaga illar yin saki har uku,da Ɗaya ya yi mata ko biyu da yanzu suna nan zamansu gwanin sha'awa.

Anan nake jan hankalin maza akan mu kula mu daina yanke hukunci cikin fushi,an sani kuma an yarda ita rayuwar aure tana zuwa da Ƙalubale daban daban kuma sai anyi haƘuri sannan ake samun abinda ake so,don haka mu kasance masu haƘuri ako ina kuma aduk halin da muka tsinci kanmu.
Chapter 53 · 0% Book details