Sashe 14
Abin Cikin Kwai Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ina shiga na kalli mai aikinta na ce"bata ce ki ɗora mata komai ba"?.ta ce"eh gaskiya bata ce ba don idan tana bacci har sai ta tashi sannan a ke yi".ɗan taɓe baki a yi sannan na tashi na shiga ɗakin da ke kusa da na ta.wa'iya zubillah ɗakin duk ƙura haka na ajje kayana a waje na cire wanda nazo dasu na yi ɗaurin ƙirji na hau aiki tas-tas na gyara ɗakin sannan na kunna burner ta ƙamshi na shiga bayin ma na wanke shi tsaf na kunna na'urar busar da banɗaki wacce ke cire duk wani bacteria idan da aƙwai.
Ina fitowa na ce"mama iya farlo kawai ta ce ki dinga gyarawa ne"?ta ce"eh wallahi bata bani umarnin gyara ɗakinta ba kawai iya farlo ne,shima ada sai bayan ƙwana biyu sannan na ke sharewa wai bata don ƙura".mamaki sosai abin ya bani na wuce kawai ɗaki na faɗa wanka ina tunanin halin da yaya Aliyu ya ke,sam bai son ƙazanta don bai taso ya samu mamanmu na yi ba,tsaf za ta gyara ko ina har ɗakin Babanmu in dai ranar ƙwananta ne zakaji ko ina ƙamshi kuma ko ina tsaf,ga ladabo da biyayya ga haƙuri,shiyasa baka taɓa jin kansu matuƙar har idan ba Hajiya kaka ba ce ta haɗosu,mahaifinmu da kanshi ya ce yafi jin daɗin zama da mahaifiyarmu saboda babu ruwanta ita haka rayuwarta take,kuma duk ita mukayo da rashin son magana Salim ne kawai shegiyar zuciya kamar ta kuturu wannan kuma zuciyar babanmu yayo.
ina gama wankan na fito na shafa maina me shegen ƙamshi da kama jiki sannan na wuce zuwa kitchen shima dai ƙazantar ce fal acikinsa ga abinci nan wanda ba a cinye jiya ba duk kyankyasa sun hau kai,kamar zanyi amai a haka na toshe bakina na gyarasa tsaf na saka air freshner ya hau ƙamshi sannan na shiga tsore na ɗebo dankalin turawa da kayan miya nazo na gyara na yi blnending ɗin kayan miyan sannan na ɗakko nama a fridge na wanke shi tsaf na tafasa shi sannan na ɗakko wata tukunyar daban na zuba mai na soya naman da kayanmiyan sannan na ɗan tsar da ruwa kaɗan na zuba curry da mai ɗanɗano yana tafasa na zuba dankaline wanda na feraye sa na wanke na yankasa a slice amman da kauri sosai saboda kada ya narke na zuba tafarnuwa da ƴar citta.haba sai ga girki ya hau ƙamshi sosai,na buɗe fridge na ciro mango ƙato na zo na wankesa tsaf na cire ɓawon sannan na cire tsokar na saka a blender ta markaɗa fruit yana markaɗuwa na zuba ruwa mai sanyi na faro harda ƙanƙara na ƙara blending sannan na juye na ta ce sa sosai,na juye a jug sannan na zuba suger enouph sosai ya fara ƙamshin mangwaro mai warin gawasa.girkina yana yi na sauke na zuba a babbar kula shima lemon mangwaron na saka sa a fridge sannan na wanke ƙwanukan tsaf na goge kitchen ɗin sannan na fito har lokacin bata tashi ba na yi mamakin mugun baccinta ace tun sanda nazo kusan awa uku mutum yana bacci,na zuba abincina na ci cikin ƙwanciyar hankali nasha lemon mangwaro na ina lumshe ido.sai ga ta ta fito daga ita sai rigar bacci iya guiwa duk gashin kanta a warwatse,na kalleta a fakaice na gaisheta ta amsa da ɗan wani guntun murmushi ta ce"au ashe ma kinzo?daman tunda zai tafi ya ce min kema yau zaki xo saboda bani da lafiya ne".sannu na ce mata kawai na cigaba da shan lemona ina kallo.ta ɗan kalleni duk sai taji kunya ta ce"kai rabonda naji ƙamshi mai daɗi har haka har na manta wallahi,gidan ya yi tsaf wallahi ban iya aikinne saboda wannan ciwon da ya sako ni agaba".ta faɗi hakan tana buɗe wamers na abinci ta ce"ta ce wow so delicious bari inci daman tun jiya banci komai ba duk abinda naci dawowa ya ke".duk zubar da take ance mata ƙala ba sai sannu dana ce mata don ni na tsani mace ƙazama duk sai najo ta fice min araina,to da ta ke ce wa ba tada lafiya ta kasa aiki ita me aikin me ye amfanin ta da baza ta iya yi ba sai wani goge farlo saboda wato shi mutane zaso gani.
buɗe cikinta ta yi sosai taci abinci kamat wata sabuwar mahaukaciya tasha lemon sosai tana gamawa ta ce"kai Khairat kin samu ladana wallahi rabon da naci abinci haka har na manta wallahi".ni dai bance komai ba ko da ta tashi daga baccin ko brush bata yi ba ina kallonta amman wai tazo har ta iya cin abinci gaskiya Yaya Aliyu yana ƙoƙari.
***
"Umma wallahi Alhaji Damas ya tsaya sosai akan wai sai mun sayar masa da gidannan,kin san wannan mutumin yana da hatsari sosai wallahi,shiyasa muke binsa a hankali".
Hajiya kaka ta kalli Abdul malik sannan ta ce"kai ni fa aduniyar nan ina ganin ikon Allah ace mutum ya dinga tsoron mutum?a i'na aka taɓa haka?ashe duk zafin zuciyarka na banza ne?shi dan ubansa ya isa ya karɓi gidan ya siya to wallahi kuce masa inji uwarku ƴar ƙasar uman bai isa yazo ya ce zai wani amshi gida awaje na ba,da a uman ne da banu shakka sai an garƙame shege,ɗan arnan kan dutse kawai".
*GAWURTATTU BIYAR,5🤚TAFIYAR TA MUSAMANCE*
1, *MU GANI A ƘASA..🔥*
_Ummu Affan_
2, *ABIN CIKIN ƘWAI..🥚*
_Ummu Maher_
3, *GUNTUN GORO..*💥
_Mom Islam_
4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎
_Mrs Bukhari_
5_ *AUREN WATA TARA👩â€â¤ï¸â€ðŸ‘¨*
_Miss Hajo_
Guda É—aya N300
Guda biyu N500
Guda uku N600
Guda huÉ—u N700
Guda biyar 1k
*ZAKU TURA KUƊINKU TA WANNAN HANYAR👇*
Fatima Rabiu Sunusi
0037219728
StanbicIBTC Bank.
Shaidar biya tanan 👇
0810 433 5144
Masu tura katin MTN👇
0814 179 9224
...........🥚👩â€â¤ï¸â€ðŸ‘¨ðŸ’¥ðŸŒŽ....
*ƳAN NIGER GA HANYOYIN BIYAN KUƊINKU👇
Guda biyar 1000f
Guda huÉ—u 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda É—aya 300f
Kai tsaye ku tura da katin Airtel ta wannan number👇
+227 84 50 64 76
*MUN GODE DA KASANCEWA DA GAWURTATTU TAKUN FARKO*
[23/09, 16:17] Miss GreenðŸ€: *🥚ABIN CIKIN ƘWAI🥚*
MALLAKAR
*ummu maher(miss green)*ðŸ€ðŸ
masu buƙatar talla 2k Ne,zamu dinga Ɗora muku a dukkanin shafukanmu a kowani social media don samun costumer cikin sauƘi.
*Sirrinmu*
yawan bin ƙwaƙƙwafin miji ma'ana yi masa bincike a ma'ajiyarsa ko a wayarsa yana saka kullum a zauna zargi kuma kunsan aure da zargi haramunne don haka don Allah mata mu kiya ye.
21🟪22
.. . . . .a ƙofar ɗaki na tsaya na bashi jakar na wuce don shiryo masa abinci,ko da ya shiga ɗakin ya hangeta cen nesa da gado tana ta sharɓar baccinta abinta harda yawun bacci,san baiyi mamakin ganin gidan fes ba saboda yadan khairat tana nan,yana shigowa yaji gidan ko ina sai tashin ƙamshi ya ke,tunda sukayi aure da khadija zai iya ce wa bai taɓa ganinta dai-dai da rana ɗaya ta ɗauki tsintsiya ta yi shara ba,kulli yaumin bacci,babu abinda ta iya sai bacci kamar kasa musamman ma da ta samu ciki duk sai abin ya ƙara jagulewa,filon ya fara ɗan bugawa a hankali ta buɗe idanuwanta ta yi miƙa ta buɗe hammatarta gashin nan ya cunkushe sosai ya kauda kansa yana jin rashin daɗi har cikin zuciyarsa ya ce"ke wai me yasa ko da yaushe babu abinda ki ka iya sai baccine?kuma ga ƙazanta ko da khairat tazo ai ba yana nufin ki sakar mata aikin komai bane?musamman yanzu da ki ke da ciki,ai ba'a son yawan ƙwanciya ko ka jibge waje ɗaya kama ta ya yi ace ki dinga ɗan exercise saboda kema zaki fi jin daɗi amman sai ki jibge ki yi ta bacci kamar kasa".
yana gama faɗar hakan ya fita ta kallesa ta baya ta ɗan hararesa ta ce"to ai ya dawo kuma yanxu babu zaman lafiya,wato don ƙanwarsa tana aiki kada ta yi?to wallahi ina ganinta bazanyi aikin komai ba,ƴaƴan ne tsafta duk ta lalatu da wani tsafta-tsafta a damu mutum kawai".tana faɗar hakan ta tashi ta fito waje da kayan jikinta tun na bacci mai makon ta shiga banɗaki ta tsala wanka ta saka kaya masu ƙyau ko babu komai ko don mijinta ya gani yaji daɗi.
ina cikin jera abinci ta fito na kalleta ta gefe na gaisheta,ta amsa tana wani ya mutsa fuska azuciyata na ce"oh Allah ya haɗa yaya da gamonsa mace har mace amman babu tsatfa yadda kasan bola haka ta mayar da kanta,su asalin babarsu ma buzuwa ce,agidanmu ana saka ƴan ɗakinsu a jerin masu ƙyau fari da kyakkyawar halitta amman fa sai dai ƙazanta ce za ta yi maka sallama dasu suna dai ƴammata idan zasu fita idan suka ɗauki ado sai ka rantse ba ƙazai bane amman fa ƙazanta na nan cunkushe jikinsu.
Abincinta ta Zuba ita kaɗai tana ya mutsa fuska ta fara ci,yaya Aliyu ya kalleta ya ce"yanzu don Allah khadija ke bakiji kunyat kanki da kanki ba?yanzu fa ki ka tashi daga bacci ko alwala bakiyi ba bare brush sannan har kizo ki fara cin abinci a ture ma ta bani haƙƙina don bakisan haƙƙina da ke kanki ba sam".
ture abincin ta yi gefe tana tura baki ta ce"gaskiya honey kana takuramin wallahi?daga dawowarka ai ka bari ka huta ma?amman ka balbaleni da faɗa agaban ƙwanwarka salon ta rainani ko"?.
"raini kuma na nawa khadija?ai wallahi sai dai idan mutum bai san halinki,amman babu komai ki cigaba da wulaƙanta ibada wataran kema sai ta wulaƙanta ki".yana faɗar hakan ya fara cin abincinsa hankalinsa ƙwance,a zuciyata na ce Allah sarki yaya aƙwai haƙuri muddin kaga ya yi magana to abu ya ƙure ne musamman akan ibada,ko sanda kafin ya yi aure ba ƙaramin takura mana ya ke akan ibada ba,sai gashi Allah ya jarabcesa da mace mara ibada wacce sam hakan bai dame ta ba.
ko ajikinta sai ma ƙara lomar abincinta da ta yi tana ta lodawa cikinta abinci wanda ya fito sosai ina tunanin ma ta kusa haihuwa,ana haka ya ce "ƙanwata kun gama waec da Neco ko?".
"Eh yaya mun gama sai jiran sakamako a tayamu da addu'ah".ɗan murmushi ya yi sannan ya ce"to Allah ya baku sa'a ai nasan sister ɗina aƙwai ƙoƙari da bada himma insha Allah sai kin fito da good result".ya faɗi hakan yana murmushi.
Ina fitowa na ce"mama iya farlo kawai ta ce ki dinga gyarawa ne"?ta ce"eh wallahi bata bani umarnin gyara ɗakinta ba kawai iya farlo ne,shima ada sai bayan ƙwana biyu sannan na ke sharewa wai bata don ƙura".mamaki sosai abin ya bani na wuce kawai ɗaki na faɗa wanka ina tunanin halin da yaya Aliyu ya ke,sam bai son ƙazanta don bai taso ya samu mamanmu na yi ba,tsaf za ta gyara ko ina har ɗakin Babanmu in dai ranar ƙwananta ne zakaji ko ina ƙamshi kuma ko ina tsaf,ga ladabo da biyayya ga haƙuri,shiyasa baka taɓa jin kansu matuƙar har idan ba Hajiya kaka ba ce ta haɗosu,mahaifinmu da kanshi ya ce yafi jin daɗin zama da mahaifiyarmu saboda babu ruwanta ita haka rayuwarta take,kuma duk ita mukayo da rashin son magana Salim ne kawai shegiyar zuciya kamar ta kuturu wannan kuma zuciyar babanmu yayo.
ina gama wankan na fito na shafa maina me shegen ƙamshi da kama jiki sannan na wuce zuwa kitchen shima dai ƙazantar ce fal acikinsa ga abinci nan wanda ba a cinye jiya ba duk kyankyasa sun hau kai,kamar zanyi amai a haka na toshe bakina na gyarasa tsaf na saka air freshner ya hau ƙamshi sannan na shiga tsore na ɗebo dankalin turawa da kayan miya nazo na gyara na yi blnending ɗin kayan miyan sannan na ɗakko nama a fridge na wanke shi tsaf na tafasa shi sannan na ɗakko wata tukunyar daban na zuba mai na soya naman da kayanmiyan sannan na ɗan tsar da ruwa kaɗan na zuba curry da mai ɗanɗano yana tafasa na zuba dankaline wanda na feraye sa na wanke na yankasa a slice amman da kauri sosai saboda kada ya narke na zuba tafarnuwa da ƴar citta.haba sai ga girki ya hau ƙamshi sosai,na buɗe fridge na ciro mango ƙato na zo na wankesa tsaf na cire ɓawon sannan na cire tsokar na saka a blender ta markaɗa fruit yana markaɗuwa na zuba ruwa mai sanyi na faro harda ƙanƙara na ƙara blending sannan na juye na ta ce sa sosai,na juye a jug sannan na zuba suger enouph sosai ya fara ƙamshin mangwaro mai warin gawasa.girkina yana yi na sauke na zuba a babbar kula shima lemon mangwaron na saka sa a fridge sannan na wanke ƙwanukan tsaf na goge kitchen ɗin sannan na fito har lokacin bata tashi ba na yi mamakin mugun baccinta ace tun sanda nazo kusan awa uku mutum yana bacci,na zuba abincina na ci cikin ƙwanciyar hankali nasha lemon mangwaro na ina lumshe ido.sai ga ta ta fito daga ita sai rigar bacci iya guiwa duk gashin kanta a warwatse,na kalleta a fakaice na gaisheta ta amsa da ɗan wani guntun murmushi ta ce"au ashe ma kinzo?daman tunda zai tafi ya ce min kema yau zaki xo saboda bani da lafiya ne".sannu na ce mata kawai na cigaba da shan lemona ina kallo.ta ɗan kalleni duk sai taji kunya ta ce"kai rabonda naji ƙamshi mai daɗi har haka har na manta wallahi,gidan ya yi tsaf wallahi ban iya aikinne saboda wannan ciwon da ya sako ni agaba".ta faɗi hakan tana buɗe wamers na abinci ta ce"ta ce wow so delicious bari inci daman tun jiya banci komai ba duk abinda naci dawowa ya ke".duk zubar da take ance mata ƙala ba sai sannu dana ce mata don ni na tsani mace ƙazama duk sai najo ta fice min araina,to da ta ke ce wa ba tada lafiya ta kasa aiki ita me aikin me ye amfanin ta da baza ta iya yi ba sai wani goge farlo saboda wato shi mutane zaso gani.
buɗe cikinta ta yi sosai taci abinci kamat wata sabuwar mahaukaciya tasha lemon sosai tana gamawa ta ce"kai Khairat kin samu ladana wallahi rabon da naci abinci haka har na manta wallahi".ni dai bance komai ba ko da ta tashi daga baccin ko brush bata yi ba ina kallonta amman wai tazo har ta iya cin abinci gaskiya Yaya Aliyu yana ƙoƙari.
***
"Umma wallahi Alhaji Damas ya tsaya sosai akan wai sai mun sayar masa da gidannan,kin san wannan mutumin yana da hatsari sosai wallahi,shiyasa muke binsa a hankali".
Hajiya kaka ta kalli Abdul malik sannan ta ce"kai ni fa aduniyar nan ina ganin ikon Allah ace mutum ya dinga tsoron mutum?a i'na aka taɓa haka?ashe duk zafin zuciyarka na banza ne?shi dan ubansa ya isa ya karɓi gidan ya siya to wallahi kuce masa inji uwarku ƴar ƙasar uman bai isa yazo ya ce zai wani amshi gida awaje na ba,da a uman ne da banu shakka sai an garƙame shege,ɗan arnan kan dutse kawai".
*GAWURTATTU BIYAR,5🤚TAFIYAR TA MUSAMANCE*
1, *MU GANI A ƘASA..🔥*
_Ummu Affan_
2, *ABIN CIKIN ƘWAI..🥚*
_Ummu Maher_
3, *GUNTUN GORO..*💥
_Mom Islam_
4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎
_Mrs Bukhari_
5_ *AUREN WATA TARA👩â€â¤ï¸â€ðŸ‘¨*
_Miss Hajo_
Guda É—aya N300
Guda biyu N500
Guda uku N600
Guda huÉ—u N700
Guda biyar 1k
*ZAKU TURA KUƊINKU TA WANNAN HANYAR👇*
Fatima Rabiu Sunusi
0037219728
StanbicIBTC Bank.
Shaidar biya tanan 👇
0810 433 5144
Masu tura katin MTN👇
0814 179 9224
...........🥚👩â€â¤ï¸â€ðŸ‘¨ðŸ’¥ðŸŒŽ....
*ƳAN NIGER GA HANYOYIN BIYAN KUƊINKU👇
Guda biyar 1000f
Guda huÉ—u 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda É—aya 300f
Kai tsaye ku tura da katin Airtel ta wannan number👇
+227 84 50 64 76
*MUN GODE DA KASANCEWA DA GAWURTATTU TAKUN FARKO*
[23/09, 16:17] Miss GreenðŸ€: *🥚ABIN CIKIN ƘWAI🥚*
MALLAKAR
*ummu maher(miss green)*ðŸ€ðŸ
masu buƙatar talla 2k Ne,zamu dinga Ɗora muku a dukkanin shafukanmu a kowani social media don samun costumer cikin sauƘi.
*Sirrinmu*
yawan bin ƙwaƙƙwafin miji ma'ana yi masa bincike a ma'ajiyarsa ko a wayarsa yana saka kullum a zauna zargi kuma kunsan aure da zargi haramunne don haka don Allah mata mu kiya ye.
21🟪22
.. . . . .a ƙofar ɗaki na tsaya na bashi jakar na wuce don shiryo masa abinci,ko da ya shiga ɗakin ya hangeta cen nesa da gado tana ta sharɓar baccinta abinta harda yawun bacci,san baiyi mamakin ganin gidan fes ba saboda yadan khairat tana nan,yana shigowa yaji gidan ko ina sai tashin ƙamshi ya ke,tunda sukayi aure da khadija zai iya ce wa bai taɓa ganinta dai-dai da rana ɗaya ta ɗauki tsintsiya ta yi shara ba,kulli yaumin bacci,babu abinda ta iya sai bacci kamar kasa musamman ma da ta samu ciki duk sai abin ya ƙara jagulewa,filon ya fara ɗan bugawa a hankali ta buɗe idanuwanta ta yi miƙa ta buɗe hammatarta gashin nan ya cunkushe sosai ya kauda kansa yana jin rashin daɗi har cikin zuciyarsa ya ce"ke wai me yasa ko da yaushe babu abinda ki ka iya sai baccine?kuma ga ƙazanta ko da khairat tazo ai ba yana nufin ki sakar mata aikin komai bane?musamman yanzu da ki ke da ciki,ai ba'a son yawan ƙwanciya ko ka jibge waje ɗaya kama ta ya yi ace ki dinga ɗan exercise saboda kema zaki fi jin daɗi amman sai ki jibge ki yi ta bacci kamar kasa".
yana gama faɗar hakan ya fita ta kallesa ta baya ta ɗan hararesa ta ce"to ai ya dawo kuma yanxu babu zaman lafiya,wato don ƙanwarsa tana aiki kada ta yi?to wallahi ina ganinta bazanyi aikin komai ba,ƴaƴan ne tsafta duk ta lalatu da wani tsafta-tsafta a damu mutum kawai".tana faɗar hakan ta tashi ta fito waje da kayan jikinta tun na bacci mai makon ta shiga banɗaki ta tsala wanka ta saka kaya masu ƙyau ko babu komai ko don mijinta ya gani yaji daɗi.
ina cikin jera abinci ta fito na kalleta ta gefe na gaisheta,ta amsa tana wani ya mutsa fuska azuciyata na ce"oh Allah ya haɗa yaya da gamonsa mace har mace amman babu tsatfa yadda kasan bola haka ta mayar da kanta,su asalin babarsu ma buzuwa ce,agidanmu ana saka ƴan ɗakinsu a jerin masu ƙyau fari da kyakkyawar halitta amman fa sai dai ƙazanta ce za ta yi maka sallama dasu suna dai ƴammata idan zasu fita idan suka ɗauki ado sai ka rantse ba ƙazai bane amman fa ƙazanta na nan cunkushe jikinsu.
Abincinta ta Zuba ita kaɗai tana ya mutsa fuska ta fara ci,yaya Aliyu ya kalleta ya ce"yanzu don Allah khadija ke bakiji kunyat kanki da kanki ba?yanzu fa ki ka tashi daga bacci ko alwala bakiyi ba bare brush sannan har kizo ki fara cin abinci a ture ma ta bani haƙƙina don bakisan haƙƙina da ke kanki ba sam".
ture abincin ta yi gefe tana tura baki ta ce"gaskiya honey kana takuramin wallahi?daga dawowarka ai ka bari ka huta ma?amman ka balbaleni da faɗa agaban ƙwanwarka salon ta rainani ko"?.
"raini kuma na nawa khadija?ai wallahi sai dai idan mutum bai san halinki,amman babu komai ki cigaba da wulaƙanta ibada wataran kema sai ta wulaƙanta ki".yana faɗar hakan ya fara cin abincinsa hankalinsa ƙwance,a zuciyata na ce Allah sarki yaya aƙwai haƙuri muddin kaga ya yi magana to abu ya ƙure ne musamman akan ibada,ko sanda kafin ya yi aure ba ƙaramin takura mana ya ke akan ibada ba,sai gashi Allah ya jarabcesa da mace mara ibada wacce sam hakan bai dame ta ba.
ko ajikinta sai ma ƙara lomar abincinta da ta yi tana ta lodawa cikinta abinci wanda ya fito sosai ina tunanin ma ta kusa haihuwa,ana haka ya ce "ƙanwata kun gama waec da Neco ko?".
"Eh yaya mun gama sai jiran sakamako a tayamu da addu'ah".ɗan murmushi ya yi sannan ya ce"to Allah ya baku sa'a ai nasan sister ɗina aƙwai ƙoƙari da bada himma insha Allah sai kin fito da good result".ya faɗi hakan yana murmushi.