← Book details A Bakin Aurenki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 29

Sashe 16

A Bakin Aurenki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

T'saki Salma ta ja,kan tace ''Malam ban waje na
wuce,tuni ya kara kuluwa, shi take ma tsakin?..

Yai mata k'yau,kawai sai ya dungurar mata da
bokitinta ya shige band'aki,da sauri Bintu tai
kitchen ta d'akko mishi nata,koh ta kansu bata
kara bi ba ta zari bokitin ta kara mai,a ranta tana
"karamar y'ar iska kawai.

Sam Salma taki dad'i, dan fur taki bawa kowa
fuska a gidan,dan taga da mugun falli amaryar ta
shigo mata.

Har girkin amarya ya kare ya dawo ga Salma
amma ba sauki.

Zata gaidashi tai komai,amma ba magana
duguwa, sai ma haushin sa dake kara ziyartar ta.

Tuni ya kai kara gun Aunty A'i,wai Salma taki
sake masa fuska.

A ranar tai mata waya ta kare mata tass,tuni ta
hau kuka,wai ai dan ita bata kishiya ne,bazata
gane lamarin ba,ga kusan kullum Bintu na
chakalarta tana kaucewa.

Shiru Aunty A'in tayi,dole wannan ba zancen
waya bane,
"Ki bari zan zo koh zuwa gobe ne.

Ranar girkin Bintu ne,yau tun safe take fallin
fararo a t'sakar gida,sai ya6a mata haibaici take
ita kad'ai kamar sabon kamu.

Salman tana zaune kan taburma a kofar ta tana
yanke farce.

Harara ta sakar mata,kan taja t'saki,
"Wawiya kawai..

Shewa Bintun tayi harda guda.

"Kece babbar wawiya wacce zaman gidanta ke
mintsininta..

Ehee, naji komai ai,saki daya ya
rage miki duk a dalilin gantali gardi.

A masife ta tashi,sai dai nan da nan ta k'auda
bacin rai dan ya6a ma Bintu magana dai-dai ita.

"Ahaiyee,, naji,tunda banyi k'wantai a layi bare
ina bi ina tallan kaina agun d'a namiji ba ehee, ke
har kin isa ki ce kin san komai?. tunda dey ni ba
matar tushe bace ba...

Dan tuni akasan da matar
tushe dai bata k'warjini...

Karya uwar bin maza
kawai...

"Eh naji ki ce komai,igiya uku ce a kaina kinga na
fiki matsayi a...

"Ke...

Bana son shashancin banza wallahi..

Juyawa sukai danjin mai gidan yai shigar bazata.

"Ihu har titi mutanan unguwa ana jinku sai kace
wasu karnika?...

Harara Salma ta sau mishi da t'sabar tuhuma a
k'allonta.

"A ni ba karya bace, dan har gidan mu ka samo
ni..chan ka nemi karya tun wuri..

Jiki ta kad'e tai dakinta ta barshi baki a sake.

Ita kam Bintu lukwas tayi,tabbas Ja'afar kadai
zai iya fad'a ma Salma cewa ita tace tana
sonshi,da kuka tai d'aki dan bakin ciki.

Itama haka take gun Salman,sosai taji zafin
maganar Bintu,tasan kuma babu mai fad'a mata
sai Ja'afar.

Toh fa Ja'afar, ka shiga t'sakiya.

By
Feenat Ja'afar.
9/29/16, 9:16 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.
26_Kowa bin kofar dakinta yai da kallo, yana
murna ba'a rikicin mata biyu a gidanshi yau gashi
an fara,dole ne tun wuri yai ma tufkar hanci.

Har
yayi dakin Salman sai ya t'saya, dole ne ya nuna
mata kuranta, in da tai mishi fitsara ya k'yale toh
yanzu bazai d'auka ba,dan ba ita kadai bace a
gidan,kawai sai ya juya dakin Bintu.

Kuka take
yana ta fadanshi taki kulashi, chan kuma sai ya
sassauto, "Ni tashin hankali ne bana so a gidana
ne,tun wuri ma in zaku had'a kai ku had'a, dan
ba mai chazan hawan jini.

Kai ta dago tana mishi
k'allon tuhuma, "Au shine dalilin da yasa ka fad'a
wa matarka baka so na?..

Ni nace ina son ka
koh?..

A haka za ai zaman lafiyan?..

"Ke kinga
bana son iyayi,dawa nai wannan zancen?..

Da
sauri cikin kuka tace "da matarka man,wato
harda fad'a mata kwantai nayi nai ma tallan
kaina..

"Ban san anyi maganar nan ba Malama,ki
ma cire zargin ni na fad'a mata, bari na je zata
fad'a min yaushe muka fara y'ar sharri da ita...

Waje yayi zuwa dakin Salman.

Kai Bintu ta k'ada,
"ashe munafuka karya take dan ta had'ani fad'a
da Miji,toh karyarki taci karya,Allah sa ya k'wada
mata mari tukuicin sharri.

Ita kam tanajin bud'e
kofarshi ta mike tare kama k'ugu ta k'ank'ance
ido.

"Salma yaushe muka fara y'ar sharri dake a
gidan nan?..

Yaushe nace miki Bintu ce tai min
tallar kanta na aura?..

Harara ta sakar mishi da
k'allon kar ka rainan hankali.

"Ka nad'e taburmar
kunyar ka man ta haka,wato kayi amarya shine
ka zabi ka tuzartani agunta,karafkaf abinda ya
faru ta fad'a mini,toh da ka fad'a mata saura
igiya daya ta aurenka a kaina sai mey?..

Baki ya
saka cike da mamaki,lalle ya shiga tarkon kaidi
na mata, wato kowacce sharri take neman k'ulla
mishi a gun y'ar uwarta ashe?..

Bai da tace wa,
kawai sai ya juya zai fice, da sauri tace "a ka
fita man,dan nayi imani bazaka karyata cewar ba
kai ka fad'i ba...

"Idan kuma habaici da iyayi
kake neman matarka ta dinga min dan ka huce
haushinka na da toh bissmillah,dai dai nake dana
sa kafar wando daya da kowa a gidan nan
wallahi..

Juyowa yai yana kallonta, sai tai d'aki
ta barshi t'saye baki sake.

Titi ya fice ko ya
samu sa'ida, lalle yau ya jinjinawa sharrin
mata,amma kaf yafi jin haushin Salma,dan sam
yanzu ya fuskanci fitsararta tafi ta da yawa.

Tun
daga ranar ba jituwa t'sakanin matan, daya in
Bintu ta fad'awa Salma sai ta fad'a mata
dubu,daga karshe ta bige da kukan bakin ciki, har
mai gidan yazo ta kit'sa mai karya da
gaskiya,wani sai dai ya bata hakuri, dan a
ganinshi yanzu Salma tafi karfinshi,dan da ya
mata magana ita y'ar dika take,daga shi har
amaryar zata chake tass, sai dai yai abinda zaiyi.

Shi yasa shi kuma ya t'siri mata t'siya,in dai zata
kona mishi rai,toh shi kuma zai ta biyewa Bintu
suna ta mata feleke a t'sakar gida, daga karshe
kam sai yaci nasara,dan haka zata shiga d'aki tai
ta kukan bakin ciki,a nan zai ta mata dariyar
keta. ***** Sallama taji kamar ta Maman Ummi
da Maman Abba,lekawa tai ta window, sune
kuwa, "munafukan Allah ta'ala kawai...

Ta fada
tana kokarin ta fito rai 6ace,dan tai imani duk
abinda take fuskanta yanzu da sa hannun su
aciki...

Chak!

Taja ta t'saya rike da labule a
hannu ganin Bintu ta fito da gudu danjin sallamar
su.

"Sai yau Aunty Ladi zaki zo min?

Har nayi
fushi ai..

Baki sake Salma take k'allonsu,tana
k'allon suna nuno kofar dakin da baki suna ma
Bintun kuskus tai baya da sauri.

Ido ta rint'se
tare da cije le6e,lalle mutum mugun ice ne,yanzu
ta gane inda Bintu ta samo duk wasu
_information_ na zaman aure nata ba agun
Ja'afar ba,ido ta bud'e, ta d'au alhakin Ja'afar,
har rantsuwa yai mata amma taki yadda.

Karshe
har raba shimfida tai dashi akan maganar har sai
da ya gamo ta da Aunty A'i aka shirya.

Zama tai
tana jiyo shewarsu a dakin Bintun.

Har kullum
bazata daina nadama akan taraiyarta dasu
Maman Ummi ba,tasan duk fushin Ja'afar ne da
t'sinuwar mala'iku ke bibbiyarta.

Har hawayen
bakin ciki tayi yau,tai kuma alkawarin daina
sa6awa mijinta ko da taji haushin shi.

T'sakar
gida ta fito bayan ta g'yara fuskarta, tai sa'a
kuwa sun fito zasu tafi suna ta dariya.

Ganinta a
t'sakar gidan yai bala'in saita nutsuwar su,a
t'saye take k'yam tamkar wata soja ta had'e rai
tam,ido cikin ido take k'allonsu,tuni suka hau
inda-inda, "dama kina ciki?..

Sannun ku da gida..

Harara ta sakar musu,ba shiri sukai hanyar
waje,Bintu ce ta t'sayar su, "bari na raka ku
hanya Aunty,ina zuwa na kira mai gida izinin fita.

Duk tana k'allonsu,har tai ma Ja'afar waya wai
za tai rakiya waje ya bata izinin fita.

Bokiti ta
zaburo da sauri tai hanyar fita,da sauri sukai
waje sun zata kansu zata iyo,kawai sai ta ja
t'saki ta shige band'aki.

"A toh na zata koh rafka
mana zatayi ai,g'wara muyi ta kai ta kai,dan
wannan da gani zatai kishin hauka...

Dariya suka
sa tana jiyo su ta band'aki daga zauren sunki
tafiya.

Ruwanta na cika da ta tara ta bud'e
band'akin a hankali tai zaure, basu nufa ba sai jin
saukar ruwa sukai akansu har Bintun.

Bokitin ta
d'auka tai kansu dashi a sukwane, da ture ture
suka fita waje da gudu.

Tana haki ta leko kofar
gidan ''Ashe karyar munafurci kuke, da ku t'saya
na g'wada muku aikin mahaukaciya, shegu gadon
na aiya,a haka zaki kare Maman Ummi wallahi,
InshaAllah kema dubinki ta kusa cika.

"Ke kuma
yau mai rabani dake a gidan nan wallahi sai
Allah, yau zaki ga karyar iskanci.

Gida ta koma
tana hakin daga ruwa bucket guda da tsohon
ciki.

A t'sakar gidan ta zauna tana maida
numfashi a hankali, ta jima da zama kamin taji
tafiyar Bintu cikin sand'a, kofar ta zubawa ido
tana harara, kai ta leko dashi dan ganin koh
Salman bata nan sai suka had'a ido.

"Wallahi
baki isa ki ce zaki hanani shiga ba, in gaske ne ki
bari na shigo na shirya in fad'an ki ke nema dani
ba hauka ba.

Murmushi tai daga inda take, "Lalle
kinyi kuskure in kina zatan zan iya had'a jiki da
karya irin Bintu,haukar nake son sauke miki aka
yau ai, gaba kin d'aina irin kuskuren nan ina zuba
miki ido kawai,yau dole na fidda ki cikin gona ta.

Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 Jul 31
Feenat Ja'afar Novel's
"Karya ki ke wallahi ki iya koyan hankali Salma,ai
fad'a da makami tsoro ne,ki ajiye bokitin mu
gabza da hannu in kin is...

"Meye hakan ke kuma
Bintu?..

Juyawa tai da sauri,tana ganin Ja'afar ta
sau kukan munafurci harda kank'ame shi,wai
Salma tace in ta shigo sai ta kashe ta da duka
da bokiti bayan ta jika su ita da bakin da zata
raka...

Ciki yai gadan-gadan gun Salman,tana
ganinshi ta mike t'saye rike da bokiti,bai
watawataba kawai yai kanta da niyar mari tai
baya.

Kunci ta rike har tana halamar yin baya
zata fad'i, "Kin haukace ne Salma ko mey?..

Gidan ki ne da har zaki kafa dokar wa zai shiga
ko ya fita?..

Cike da mamaki ke d'auke a
fuskarta, ganin yadda ya rufe ido yake zazzaga
mata bala'i harda yunkirin mari.

"Ni zaka mara da
akan waccan karyar Ya Ja'afar?..

A tuzare yace
"eh wallahi, da da halin duka ma sai na
miki,kuma daga yau kar in sake jin kin kamanta
matata da sunan kare a gidan nan..

Kai ta k'ada,
kan tai baya tana g'yara t'sayuwa tai d'aki.
Chapter 16 · 0% Book details