Sashe 3
Zaman Kanta Take Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Satar kallon sa tayi, ta tabe baki ƙasa ƙasa tace '' ikon Allah sai kace wanda aka saka tsumagiya aka dake shi sai wani yin magana yake yi dakyar to ai ba dole akai maka ba.''
ɗago idon sa yayi ya kalle ta , shifa mamaki take bashi kwata kwata bata da tsoro.
Ungo ta faɗa tana dauko mai takardun'ta tare da littafin ta wanda ta tabbatar taci very good wani ma a ciki excellent taci.
amsa yayi yana kallon takardun nata ajiyewa yayi ya buɗe littafin karon farko yaci karo da very poor buɗe wani shafin yayi zane ne cike da fulawa kala kala ajiyewa yayi yace '' saboda me kike neman aiki...?.''
nimrah tace '' ina so na ɗinga cin abinci ina koshi.''
sosai abin ya ba shi dariya in banda kuruciya inhar ka samu kaci ai ba sai ka koshi ba babu ita ce barna yace '' za kiyi aikin rainon yara?.''
Nimrah kuka ta saka tace '' wannan wanne irin hulakanci ne shi yace min ba'kwa bukatar masu share share, kai kuma yanzu kace rainon yara kawai kuce bazan samu aiki ba shikkenan na hakura zan ci gaba da suyar a'wara a kofar gidan mu, kullum malam cewa yake nayi kwantai kaga ni yanzu inhar zaka bani abinci me dad'i irin na turawa da kaza, zan yi maka rainon yaran.''
sakar baki yayi yana kallon ta ikon Allah sai kallon ta yace '' bakya buƙatar kudi?.''
nimrah gyaɗa mai kai tayi to idan ta samu wa'yannan me kuma za tayi da kuɗi? daman ita matsalar ta , rashin abinci ko ta , taya hafsatu aikin gida kaɗan take bata , wata ran cewa take, ta kannan ta , take yi ba ta ita ba.
Saheer mamaki ne ya kama shi i gaskiya dole ya te'maki yarinyar nan baya so yaga rayuwar kananan yara ta gurɓata yanzu ace wani ta haɗu dashi ba shi ba yake nan ajiyar zuciya ya sauke yace '' ina ne gidan ku?.''
da sauri nimrah ta goge hawaye tace '' aikin rainon yaran ma sai na nuna maka gidan mu?.''
Saheer haɗe rai yayi yace '' tambayar ki nake kina tambaya ta.''
Nutsuwa tayi domin a kalla tasan babban mutum ne zai iya yin malam mahaifinta tace '' dan Allah karka kai karata gurin malam.''
wayar sace , tayi ringing kallon screen din wayar yayi sunan hidaya ne ya fara yawo a screen din wayar dauka yayi ya ƙara a kunne bece komai ba.
daga can ɓangaren hidaya tace '' har yanzu fa baka turo ba naji shiru ? kasan karshen wata yayi to na zuba ido ban ga alert ba.''
rintsai ido yayi besan wacce irin mace ya aura ba kudi shi ne gaba da komai a rayuwar ta , duk kwanan da take a cikin gidan nan kwanan kudi take kamar ba matar saba ba ƙaramin mamaki yayi ba da har ta iya bugo mai duk da Irin abin da tayi mai , ya samu wani magani ne to yana ganin kamar an dace ya fara samun lafiya da yaje gare ta kin yarda tayi dashi ta nuna mai sam ita bata yarda ita bata shirya yi ba.
Allah sarki A'isha Ubangiji Allah ya jikan ki haka ya raya wannan a cikin zuciyar sa afili kuwa sai yace '' okay.''
kashe wayar sa yayi a lokacin ya tura mata kudin ta ya ajiye wayar yana cewa ina jin ki.
Nimrah da ta , tafi tunani da sauri tace '' Ni?.''
wani kallo yayi mata da sauri tayi ƙasa da kan'ta tace '' a unguwar tudun bala nake nan kusa da taransifoma biyar kana zuwa idan kace a kai ka gidan su nimrah yar boko za'a kawo ka gidan mu.''
ajiyar zuciya ya sauke yace '' okay zaki iya tafiya.''
tashi tayi tace '' to ka dauke ni aikin ne gobe nazo? amma bani da kudin mota.''
ciro kudi yayi ya ajiye mata dubu biyar yace '' karki zo.''
dauka tayi ta dauki dubu biyu ta ajiye tace '' sun yi min yawa wannan ma me napep zan bawa idan be yi fushi ba ya tafi wannan sai na koma gida.''
Saheer haɗe rai yayi yace '' dauke .''
a'a ta faɗa tana girgiza kan'ta bata kula ba ta buge da kujera da sauri Saheer ya taso ya riƙe ta ganin tana shirin kifawa kasa dai-dai lokacin kuma aka turo kofar dukkan su kallon kofar suka yi wanda ya shigo babban mutum ne sai ya fara tafi yana cewa Saheer daman abin da kake kenan? .''
da sauri nimrah ta ja baya ta kalli mutumin kwata kwata tunanin ta da ƙwaƙwalwar ta be kawo mata komai ba.
Saheer yace '' Alhaji Nuhu kar ka yi kokarin danganta ni da kalmar da hat abada kasan bazan taɓa aika abin da kake zargi ba.''
Alhaji Nuhu bece komai ba ya saki wani malalacin murmushi ya fita.
Saheer kallon nimrah yayi yace '' daman aiko ki aka yi ko domin ki bata min suna?.''
a'a wallahi ban san sa ba ta faɗa tana ja baya ganin yadda ya koma mata.
Saheer cikin ɓacin rai ya wullo mata , takardun ta suka tarwatsai anan yace '' ki fitar min daga office tun kafin na balla ki.''
ko tsayawa daukan takardun ta ba , tayi ba ta fita da sauri tana share hawaye , sosai jikin ta yake rawa.
ganin kamar security din wajen suna kallon ta da gudu ta fita tana ganin me napep ɗin nan ta shiga jikin ta yana rawa tace '' dan girman Allah mu barnan kar su kama ni.'
Za kici kuttumar uban ki fito min da kudina fitar min daga mashin ai ke basan yar akuya bace wallahi ko wani na gani zai temake ki sai na hana shi.
dan girman Allah kai hakuri ga wannan nan mu tafi.
ta faɗa tana bashi kuɗin hannun ta.
karɓa yayi ya duba ya tura a aljihu yace '' a bakin titi zan ajiye ki.''
to, ta faɗa tana share hawayen ta.
A bangaren Saheer kuwa rasa ina zai saka kan'sa yayi ɓacin rai ya hana shi sakat,
sadam ne ya shigo da yake ya aika a kirawo shi yace '' kasan yarinyar nan...?.''
zama yayi yana cewa wallahi ban santa ba ni da farko na zata mahaukaciya ce lokacin da zamu shigo Company nan da Mahmud muka gan'ta da zan mata magana sai Mahmud ya hanani saboda mun gansu ita sa wani namiji ya biyo ta , yana zage zage.
wani irin sarawa kan Saheer yayi yace '' aiko ta aka yi.''
da sauri sadam yace '' oga wa'zai aiko ta?''
yanzu baka ga alhaji nuhu ya zo ba ? waya faɗa mai na dawo kasar nan ? ko yan jarida basu sani ba cikin dare na dawo ko hidaya bata san da dawowa ta ba sai yau da safe ta ganni motar da na fita da ita, taka ce abin da ya ban mamaki beyi sallama ba ya shigo min office kuma ya akai yasan ina wannan office ɗin? cije lips ɗin'sa yayi ya ci gaba da bashi labarin yadda abin ya faru.
kan sadam ne ya kulle yace '' gaskiya biri yayi kama da mutum, me ya saka tun farko ba mu dauki wani action ba, oga ga wata shawara.''
kai ya gyara mai alamar yana jin sa.
Sadam ne damu ba saboda ya saba da haka yace '' me zai hana kafin ya ɓata maka suna saboda banzan dalilin sa na son ku haɗa hannu ku gallazawa al'umma dole sai price din ku ya zo daya ka dinga kawo kaya mara inganci da yayi maka sharrin kana shigo da hodar ibilis a wannan karon sai ka toshe bakin sa , ka auri yarinyar nan ta haka za ka gano dukkan wata makarkashi da suke kullawa kasan zargin da muke yi motar ta sa kahau kai da Allah ya jikan rai bula maka tankin motar aka yi mai yake zuba a hankali har kai wannan hatsarin Allah ne yayi da kwanan ka a gaba da tuni ka mutu.''
sadam aure fa kace me zanyi da sa'ar autar mu wannan na tabbata ko ihsan ta girme ta baka ganin hakan abin kunya ne kamata na auri wannan yarinyar baka ganin za'a dinga maganganu...?''
gyara zama sadam yayi yace '' da ace kana neman yar cikin ka da ace ka auri yar cikin ka , wanne yafi wani muni ? aure ne , na dan wani lokaci kafin komai ya dai-dai ta , ka sake ta yanzu tun kafin ya , yaɗa wannan labarin nasan tun da ya fita to akwai abin da hakan yake nufi kayi maza ka dauki blogger's su fara rubutu suna cewa ana rade radin zaka ƙara aure, hakan zai dauki hankalin al'umma wasu ma suce ai kayi kaga bashi da hanyar fito da wannan maganar ita kuma yarinyar gurin iyayen ta zamu ayi komai a gama nasan Hajiya za ta iya nuna rashin amincewar'ta tun da tana kaunar Hajiya hidaya ka kwantar da hankalin ka a hankali ka fahimtar da ita.''
ajiyar zuciya ya sauke yace '' sadam na barma ka komai a hannun ka .''
inshallahu zan yi komai yadda muka tsara inshallahu haka komai zai tafi.
Saheer yace '' Allah ya yarda.''
amin ya Allah yace yana fita.
Wannan kenan.
tun da suka fara tafiya sai hankalin ta ya dawo jikin ta, tunowa tayi da takardun ta ɗora hannu aka tayi ta zunduma ihu.
da sauri me mashin ya juyo yana cewa lafiya..?.''
nimrah tace "' takarduna wallahi na baro su acan gashi ban san yadda za a yi na ƙara samun su ba shikkenan ba zan zama ma'aikaciya ba burina ba zai cika gaba.,,
a fusace matashin nan yace '' kuttumar uban ki haka kurum ki zunduma min ihu to sauka..?.''
nimrah tace '' bamu zo ba fa.''
wallahi sai kin sauka.
parking yayi, ta fita jikin ta yana rawa,
ɗago idon sa yayi ya kalle ta , shifa mamaki take bashi kwata kwata bata da tsoro.
Ungo ta faɗa tana dauko mai takardun'ta tare da littafin ta wanda ta tabbatar taci very good wani ma a ciki excellent taci.
amsa yayi yana kallon takardun nata ajiyewa yayi ya buɗe littafin karon farko yaci karo da very poor buɗe wani shafin yayi zane ne cike da fulawa kala kala ajiyewa yayi yace '' saboda me kike neman aiki...?.''
nimrah tace '' ina so na ɗinga cin abinci ina koshi.''
sosai abin ya ba shi dariya in banda kuruciya inhar ka samu kaci ai ba sai ka koshi ba babu ita ce barna yace '' za kiyi aikin rainon yara?.''
Nimrah kuka ta saka tace '' wannan wanne irin hulakanci ne shi yace min ba'kwa bukatar masu share share, kai kuma yanzu kace rainon yara kawai kuce bazan samu aiki ba shikkenan na hakura zan ci gaba da suyar a'wara a kofar gidan mu, kullum malam cewa yake nayi kwantai kaga ni yanzu inhar zaka bani abinci me dad'i irin na turawa da kaza, zan yi maka rainon yaran.''
sakar baki yayi yana kallon ta ikon Allah sai kallon ta yace '' bakya buƙatar kudi?.''
nimrah gyaɗa mai kai tayi to idan ta samu wa'yannan me kuma za tayi da kuɗi? daman ita matsalar ta , rashin abinci ko ta , taya hafsatu aikin gida kaɗan take bata , wata ran cewa take, ta kannan ta , take yi ba ta ita ba.
Saheer mamaki ne ya kama shi i gaskiya dole ya te'maki yarinyar nan baya so yaga rayuwar kananan yara ta gurɓata yanzu ace wani ta haɗu dashi ba shi ba yake nan ajiyar zuciya ya sauke yace '' ina ne gidan ku?.''
da sauri nimrah ta goge hawaye tace '' aikin rainon yaran ma sai na nuna maka gidan mu?.''
Saheer haɗe rai yayi yace '' tambayar ki nake kina tambaya ta.''
Nutsuwa tayi domin a kalla tasan babban mutum ne zai iya yin malam mahaifinta tace '' dan Allah karka kai karata gurin malam.''
wayar sace , tayi ringing kallon screen din wayar yayi sunan hidaya ne ya fara yawo a screen din wayar dauka yayi ya ƙara a kunne bece komai ba.
daga can ɓangaren hidaya tace '' har yanzu fa baka turo ba naji shiru ? kasan karshen wata yayi to na zuba ido ban ga alert ba.''
rintsai ido yayi besan wacce irin mace ya aura ba kudi shi ne gaba da komai a rayuwar ta , duk kwanan da take a cikin gidan nan kwanan kudi take kamar ba matar saba ba ƙaramin mamaki yayi ba da har ta iya bugo mai duk da Irin abin da tayi mai , ya samu wani magani ne to yana ganin kamar an dace ya fara samun lafiya da yaje gare ta kin yarda tayi dashi ta nuna mai sam ita bata yarda ita bata shirya yi ba.
Allah sarki A'isha Ubangiji Allah ya jikan ki haka ya raya wannan a cikin zuciyar sa afili kuwa sai yace '' okay.''
kashe wayar sa yayi a lokacin ya tura mata kudin ta ya ajiye wayar yana cewa ina jin ki.
Nimrah da ta , tafi tunani da sauri tace '' Ni?.''
wani kallo yayi mata da sauri tayi ƙasa da kan'ta tace '' a unguwar tudun bala nake nan kusa da taransifoma biyar kana zuwa idan kace a kai ka gidan su nimrah yar boko za'a kawo ka gidan mu.''
ajiyar zuciya ya sauke yace '' okay zaki iya tafiya.''
tashi tayi tace '' to ka dauke ni aikin ne gobe nazo? amma bani da kudin mota.''
ciro kudi yayi ya ajiye mata dubu biyar yace '' karki zo.''
dauka tayi ta dauki dubu biyu ta ajiye tace '' sun yi min yawa wannan ma me napep zan bawa idan be yi fushi ba ya tafi wannan sai na koma gida.''
Saheer haɗe rai yayi yace '' dauke .''
a'a ta faɗa tana girgiza kan'ta bata kula ba ta buge da kujera da sauri Saheer ya taso ya riƙe ta ganin tana shirin kifawa kasa dai-dai lokacin kuma aka turo kofar dukkan su kallon kofar suka yi wanda ya shigo babban mutum ne sai ya fara tafi yana cewa Saheer daman abin da kake kenan? .''
da sauri nimrah ta ja baya ta kalli mutumin kwata kwata tunanin ta da ƙwaƙwalwar ta be kawo mata komai ba.
Saheer yace '' Alhaji Nuhu kar ka yi kokarin danganta ni da kalmar da hat abada kasan bazan taɓa aika abin da kake zargi ba.''
Alhaji Nuhu bece komai ba ya saki wani malalacin murmushi ya fita.
Saheer kallon nimrah yayi yace '' daman aiko ki aka yi ko domin ki bata min suna?.''
a'a wallahi ban san sa ba ta faɗa tana ja baya ganin yadda ya koma mata.
Saheer cikin ɓacin rai ya wullo mata , takardun ta suka tarwatsai anan yace '' ki fitar min daga office tun kafin na balla ki.''
ko tsayawa daukan takardun ta ba , tayi ba ta fita da sauri tana share hawaye , sosai jikin ta yake rawa.
ganin kamar security din wajen suna kallon ta da gudu ta fita tana ganin me napep ɗin nan ta shiga jikin ta yana rawa tace '' dan girman Allah mu barnan kar su kama ni.'
Za kici kuttumar uban ki fito min da kudina fitar min daga mashin ai ke basan yar akuya bace wallahi ko wani na gani zai temake ki sai na hana shi.
dan girman Allah kai hakuri ga wannan nan mu tafi.
ta faɗa tana bashi kuɗin hannun ta.
karɓa yayi ya duba ya tura a aljihu yace '' a bakin titi zan ajiye ki.''
to, ta faɗa tana share hawayen ta.
A bangaren Saheer kuwa rasa ina zai saka kan'sa yayi ɓacin rai ya hana shi sakat,
sadam ne ya shigo da yake ya aika a kirawo shi yace '' kasan yarinyar nan...?.''
zama yayi yana cewa wallahi ban santa ba ni da farko na zata mahaukaciya ce lokacin da zamu shigo Company nan da Mahmud muka gan'ta da zan mata magana sai Mahmud ya hanani saboda mun gansu ita sa wani namiji ya biyo ta , yana zage zage.
wani irin sarawa kan Saheer yayi yace '' aiko ta aka yi.''
da sauri sadam yace '' oga wa'zai aiko ta?''
yanzu baka ga alhaji nuhu ya zo ba ? waya faɗa mai na dawo kasar nan ? ko yan jarida basu sani ba cikin dare na dawo ko hidaya bata san da dawowa ta ba sai yau da safe ta ganni motar da na fita da ita, taka ce abin da ya ban mamaki beyi sallama ba ya shigo min office kuma ya akai yasan ina wannan office ɗin? cije lips ɗin'sa yayi ya ci gaba da bashi labarin yadda abin ya faru.
kan sadam ne ya kulle yace '' gaskiya biri yayi kama da mutum, me ya saka tun farko ba mu dauki wani action ba, oga ga wata shawara.''
kai ya gyara mai alamar yana jin sa.
Sadam ne damu ba saboda ya saba da haka yace '' me zai hana kafin ya ɓata maka suna saboda banzan dalilin sa na son ku haɗa hannu ku gallazawa al'umma dole sai price din ku ya zo daya ka dinga kawo kaya mara inganci da yayi maka sharrin kana shigo da hodar ibilis a wannan karon sai ka toshe bakin sa , ka auri yarinyar nan ta haka za ka gano dukkan wata makarkashi da suke kullawa kasan zargin da muke yi motar ta sa kahau kai da Allah ya jikan rai bula maka tankin motar aka yi mai yake zuba a hankali har kai wannan hatsarin Allah ne yayi da kwanan ka a gaba da tuni ka mutu.''
sadam aure fa kace me zanyi da sa'ar autar mu wannan na tabbata ko ihsan ta girme ta baka ganin hakan abin kunya ne kamata na auri wannan yarinyar baka ganin za'a dinga maganganu...?''
gyara zama sadam yayi yace '' da ace kana neman yar cikin ka da ace ka auri yar cikin ka , wanne yafi wani muni ? aure ne , na dan wani lokaci kafin komai ya dai-dai ta , ka sake ta yanzu tun kafin ya , yaɗa wannan labarin nasan tun da ya fita to akwai abin da hakan yake nufi kayi maza ka dauki blogger's su fara rubutu suna cewa ana rade radin zaka ƙara aure, hakan zai dauki hankalin al'umma wasu ma suce ai kayi kaga bashi da hanyar fito da wannan maganar ita kuma yarinyar gurin iyayen ta zamu ayi komai a gama nasan Hajiya za ta iya nuna rashin amincewar'ta tun da tana kaunar Hajiya hidaya ka kwantar da hankalin ka a hankali ka fahimtar da ita.''
ajiyar zuciya ya sauke yace '' sadam na barma ka komai a hannun ka .''
inshallahu zan yi komai yadda muka tsara inshallahu haka komai zai tafi.
Saheer yace '' Allah ya yarda.''
amin ya Allah yace yana fita.
Wannan kenan.
tun da suka fara tafiya sai hankalin ta ya dawo jikin ta, tunowa tayi da takardun ta ɗora hannu aka tayi ta zunduma ihu.
da sauri me mashin ya juyo yana cewa lafiya..?.''
nimrah tace "' takarduna wallahi na baro su acan gashi ban san yadda za a yi na ƙara samun su ba shikkenan ba zan zama ma'aikaciya ba burina ba zai cika gaba.,,
a fusace matashin nan yace '' kuttumar uban ki haka kurum ki zunduma min ihu to sauka..?.''
nimrah tace '' bamu zo ba fa.''
wallahi sai kin sauka.
parking yayi, ta fita jikin ta yana rawa,