← Book details Yar Gidan Tsohowa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 26

Sashe 9

Yar Gidan Tsohowa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Yanuna khalil "Musamman kai khalil da bakowa kasani ba a cikin dangi, saboda baud'and'en ra'ayinka,
Amma kasan ko wacece dijama, kasan matsayinta a gidan nan,
Baka buk'atar na kuma yi maka wani dogon bayani a kanta."

Ya kuma maida hankalinshi a kan Mahmoud, yace "Mahmoud ga k'anwarka nan nasan kafi kowa farin cikin dawowarta gidan nan baki d'aya."

"Abunda nakeso daku Ku d'auketa kamar yanda kuka d'auki fateema a wurinku, kubata kulawa kamar yanda kuke bawa fateema,
kai inma son samune Kubata kulawa fiye da ynda kuke bawa fateema saboda Ummie marainiyace."

Sai a lokacin mahmoud yayi mgna yace "Abba meyasa ka d'auko mana dijama?"
Abba dijamar da kasani a da ayanxun ta canza hali,
Na rantse da Allah dijama tana iya tayarda gidan nan da unguwar nan gaba d'aya saboda hatsabiban cinta."

Nidai Abba dazakaji sha'warata da anmayar da dijama can Tofa Dan tafi ganewa can, kowa ma sai yahuta."

Dijama tayi saurin d'ago kai ta dubi yaya Mahmoud ta murgud'e mashi maki cike da tsiwa, ta karkace kai tace "lallai ma yaya nan wai a mayardani tofa to sannu."

Khalil yayi saurin nufarta ya sanya hannu ya buge mata baki, dama yana ganin take takenta saitayi rashin kunya."

Dijama tayi saurin rik'e baki, tana fad'in wayyo Allah na ya fasa mun baki"

"Yace k'azama 'yar k'auye, yaya muhmoud d'in kike yiwa rashin kunya?"

Abba ya doka masu tsawa cike da b'acin rai yace "kar in kuma ganin d'aya daga cikinku ya kuma dukanta, bana son hkan,
Na rantse akan Ummie zan iya sab'awa da kowa a cikinku,
domin ganin farin cikinta, na kuma rik'e Amanar d'an uwana."

Ya maida kallonsa zuwa wurin mahmuod yace "Kai Mahmoud yaushe kuka fara 'yar hakan da kaida Ummien taka?"
"To koma dai me takeyi a can k'auye ba ruwanku,
Domin yanxun ta baro k'auye ta shigo birni."
Rayuwarta zata canza, kuma banason tsangwama da hantara a tsakaninku."

"Idan Allah ya kaimu gobe kaje makarantar su fateema, Kasan yanda za'ayi ayo mata takardun shedan ta kammala primary sannan, sai a sanyata a jss1 sai suci gaba da karatunsu tare da fateema."

Kai kuma khalil kaje islamiyarsu fateema ka yanko mata form a d'unka mata uniform sai ta tafara zuwa."

Batare da sun musaba suka amsa da "to Abba."

Ya dubesu yace "Allah yayi maku Albarka."

Suka amsa da Amin."

Sannan ya dawo wurin fateema yace "fateema ga 'yar uwarki nan Ku had'a kanku, kiko ya mata wasu abubuwa wad'anda batasaniba,
Kuma ina so ki d'auketa tamkar 'yar uwarki Asma'u da kika rasa,
Allah ya jikan Asma'u da rahama suka amsa da amin gaba d'ayansu."

Sannan ya basu umurnin kowa ya tashi,
Bayan sunfita ne ya kuma kiran Mahmoud ya dawo ya tsuguna,
Yace "ya kukayi da baban naka Alhaji Atiku?"

Mahmoud ya sunkuyar da kai, yace "zuwan danayi Abuja wurinsa ya karramani sosai, sannan ya turani mukayi jaraba."

Yace kuma "nafad'a maka musanya ido daga nan zuwa wata biyu za'a lik'a sunayen mutanen da sukaci, sannan zai kirani mutafi wurin trening

Abba yayi murnushi yace "karka damu indai Alhaji Atiku ne kasanyawa rayuwarka har kazama soja."

Momy tace "Allah ya taimaka ya tayaka rik'o da gaskya."

Suka "Amsa da Amin."

Sannan yayi masu sallama yatashi ya fita."

Abba ya dubi momy da sai murmushi takeyi d'auke a kan fuskarta,
Yace momyn yara babu abunda zance maki a rayuwa sai dai Addu'a domin kinsamarmun farin ciki a cikin zuri'ata Allah ya barmu tare dake, babban burina shine na faranta maki har k'arshen rayuwarta."

Ya Matso daf da ita, yarik'a hannunta ya shiga murzawa yana kallonta had'ida kashe mata ido d'aya."

Yace "kinsan wani Abu kuwa?"
A kasalance ta dubeshi ta girgiza kai alamar A'a."

"A kullum idan ina tare dake jinakeyi tamkar ina tare da yarinya yar shekara 17,
saboda komai naki na dabanne a koda yaushe yarinya kike komawa."

Ya kuma shege mata a jiki yana shishinar daddad'an k'amshin jikinta,

had'ida sab'ule mata d'ankwalin kanta yana shafa gashin kanta dayasha gyara da mayunka masu Sanya laushin gashi da santsi uwa uba kuma k'amshi."

_Ina ganin hakan nayi saurin fitowa cike da mmkin su Abba da momy ba'a tsofa🤔_

Mahmoud yaje makarantarsu fateema yayi duk abunda Abba ya umurceshi,
ya k'arb'o mata uniform d'inta da littafanta yataho mata dasu,
Ranar Monday zata fara zuwa makaranta."

Da sallamarshi ya shigo cikin babban falon gidan,
ba kowa a cikinsa, sai tausin k'arar TV kawai yakeji yana tashi, gefe d'aya yaji sai dariya akeyi harda buga k'afa.'

Koba'a fad'a masaba yasan dijama ce."

Mmki yashigayi yanufi wurin TV yayi saurin kashewa,
Ya juya ya kalleta, sukayi ido biyu da ita,
ta turo baki tana hararsa k'asa k'asa."

Cikin fushi yace "lallai d'an k'auye yashigo birni yafara wayewa,
Tomu a nan gidan ba'a mana kallo a k'urema volume, anan gidan karatu akeyi a koda yaushe ba zaman shashnciba da rashin kunya, takwala kawai Wanda bata gane karatu."

Ya jefa mata ledar kayan makarantarta yace "gasu nan ki kwana da shiri gobe Monday zaki fara zuwa makaranta, kuma nizan kaiki da kaina, zan shaida masu cewa baki gane komai kwakwalwar kifi ce dake, kuma da zarar kinyi masu irin rashin kunyar da kikeyi a k'auye, zance suyi fata fata da naman jikinki su jefar dake a bula."
Dama tsohuwa ke tare maki yanxunfa?"

Kallonshi tayi idonta cike da hawaye domin a rayuwarta bbu abunda ta tsana irin yaya Mahmoud ya kirata da takkwala mai kwanyar kifi."

Shima yayi mmkin ganin zubar hawaye a idon dijama anan take lokaci d'aya."

Zata bud'a Baki tayi magana kenan ya matso daf da ita, yace "muddun kika bud'a baki kikayimun rashin kunya saina tattakaki."

Ta fasayin maganar ta sunkuyar da kanta k'asa tana aika mashi da Allah ya isa a zuciyarta.'

Mik'ewa tayi tsaye ta d'auki ledar uniform d'inta, saida ta kwatanci saiti wurin k'afarshi ta
sakar mashi remote d'in TV a babban d'an yatsan k'afa, sai da yayi sarin runtse idonshi yace "washh."
Saboda zafin dayaji wurin namasa."

Ta zuba da gudu ta haiye sama tanufi d'akinsu, taja tayi tsaya a bakin k'ofar d'aki, tana kallonshi tana burgud'a baki tace "kuma bani bace takwala sai dai inkaine."

Kuma tunda kakeyimun gorin karatu saina baka mamaki mugu kawai, dan kana ganin nazo gidanku, to kasani duk abunda kakeyimun a rubuce yake a kaina saina fad'awa tsohuwa."

Ganin ya nufota tayi saurin shigewa d'akin had'ida sanyawa k'ofar key."

Tsaye yayi yakasa tafiya yana kallon babban d'an ya tsanshi da ya somayin ja,
Yana tunanin dijama wato bata daina halintaba kenan lallai akwai aiki a nan gaba."

Yana nan tsaye wuri d'aya saiji yayi andafashi a bayanshi, Khalil yagani yace "brother lfy kayi tsaye a nan?"

Su momyn basu dawobane?"

Mahmoud yace "fita sukayi ne?

"Khalil yace "sunje gidan gaisuwa tare da Abba."

Ya mik'awa Mahmoud wani takarda Mahmoud ya karb'a yana dubawa yana cewa "takardar meye?"

Khalil ya yamutsa fuska yace form d'in islamiyar wnn bagidajiyar nan ne, wadda Abba yasanyani karb'owa, nagama cika komai sunanta ne kawai bansaniba,

Wlh bnsan abunda yasa Abba ya dawo da ita gidan nan ba, da zarar munyi ido biyu da ita jinakeyi kamar zanyi amai."

Mahmoud ya dubeshi yace "khalil 'yar uwarka face, gakya ya kamata ka canza hali Kuma ka canza rayuwa, kadaina ganin 'yan matan Jami"a kyawawa wayayi suna rud'arka har kake kyamatar jininka. To kasani asalinka k'auye a can Abbamu ya tashi a can ya girma har gobe mahaifansa suna k'auye."

Wani saurin ja da baya yayi yana duba bayansa, ganin baiga kowa a wurinba yace "haba brother bazaka gane bane, nagodewa Allah da bakowa a kusa dani lokacinda kake fad'in hakan daka sanyani naji kunya."

Ido Mahmoud ya tsora mashi yana mmkinsa domin yanda ya d'aukeshi sai yaga ya wuce nan."

Takarda ya mik'a mashi yace "ynda bakasan sunantaba nima bnsan sunantaba, kabari idan Abba ya dawo shida ya sanyaka saika tmbayeshi sunanta kagani sai ya fad'a maka."

Yana kawowa nan yayi tafiyarshi ya barshi nan tsaye zuciyarshi cike da mmkin khalil."

Khalil yabi mahmoud da kallo yace "ya za'ayi na tambayi Abba sunanta, nasan yanda yakejinta a gidan nan yana iya kafsamin a gabanta
Zan dai jira har lokacin da fateema dawo daga mkranta saina tambayeta."

Yajuya yanufi d'akinshi yana mamakin mohmuod ganin yanda shima yakeji da wann bagidajiyar a gidan nan☹
[28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅

Written
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Bashir_)

*13*

Da sauri shugaban mkranta ya nufo ajin har da tuntub'e. Yakeyi domin lbrin da ya isar mashi anjiwa 'yar ciyaman da 'yar kassila ciwo."

Ganin saurin da yakeyi yasa sauran malamai suka fahimci a akwai abunda ke faruwa, suka rufo mashi baya."

Ganin jinin dake zuba a bakukansu ya d'agawa malamai hankali. Anan take aka Shiga basu taimakon gaggawa."

Shugaban makaranta ya d'aga waya ya kira ciyaman da kassila yake shaida masu abunda ke faruwa."

Ko wannensu cikin tashin hankali suka bugawa jami'an tsaro waya, anan take mota biyu ta 'yan sanda kamar had'in baki, motar ciyaman da motar kassila."

Suka shigo cikin mkrantar sai jiniya kukeji kamar za'a tashi makarantar, 'yan sandan kowanensu da zungureriyar bindigarshi a hannunshi."

Sai tambaya sukeyi ina yarinyar da taji masu ciwo, a wuce da ita atafi da ita a hukuntata."

Dijama dake tsugune gefe d'aya sai Zarar ido takeyi ta karkace kai duk Wanda ke magana tana binshi da kallon tana kallon bakinshi."

Turanci kawai takeji yana tashi Wanda bata san abunda suke cewaba kallonsu kawai takeyi."

Can taga shugaban makaranta ya nunata da yatsa yana fad'i da Hausa yana cewa "kunganta can itace, yau yau d'in nan da zuwanta makarantar nan amma har ta fara dazamun bala'i."

Shekarata goma sha d'aya da bud'a makarantar nan hakan bata tab'a faruwa daniba sai zuwan wann fiti nan niyar yarinya."

Tsawa aka dokawa dijama Wanda yasa tayi saurin mik'ewa tsaye saboda ganin zungureriyar bindigar dake hannun d'an sandar."

Tashiga ja da baya tana "fad'in Dan Allah kuyi hak'uri karku harbeni sune suka fara tsokanata."

Fateema kuma babu abunda takeyi sai aikin kuka, Wanda a cikin mutanen wurin bbu Wanda ya lura da ita tana gefe d'aya a tsaye."

Kuma doka mata tsawa d'an sandar yayi, yace "ba kasheki zamuyiba tafiya zamuyi dake sai munji ko waye ubanki a garin nan snn mu d'aukar mki hukunci."
Chapter 9 · 0% Book details