Sashe 7
Yar Gidan Tsohowa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abba shima yashiga yimata fad'a kamar ya doketa abunda bai tab'a yi mataba tunda aka haifeta,
Kaka dake zaune gefe d'aya yace "gwara da Allah yasa ka nan a gaban idonka hakan ta faru,
Kullum a rana d'aya sai sama da mutum goma sunkawo k'ararta tsohuwa ke tare mata,bata son ganin b'acin ranta."
Amma tunda ynxun ka ganewa idonka sai ka d'auki mataki, akai,
Ga ganta nan Ko mkranta bata zuwa gaba d'aya makarantar biyu Arabic da boko duk ankorota, saboda hatsabibancinta gata bata gane komai sai fitina da rashin kunya. Yakai k'arshen maganarshi yana zungura mata sandar hannunshi."
Tsohuwa bata tanka masuba saima taja bakinta tayi shuru, domin yau itama dijama ta kaita bango."
Abba yayi kyaran murya ya dubi tsohuwa yace "inna kiyi hak'uri kibani dijama natafi da ita na nema mata ilimi Wanda zatayi dogaro da kanta tazama abar Alfahari a cikin Al'umma, yin hkan shi zai Sanya mana natsuwa a zuciyarmu ganin mun rik'e marainiyar Allah tsakani da Allah."
Kaka yayi karaf yace "aikuwa wlh da ka taimakemu ka taimaki mutanen garin nan mundun katafi da dijama kabar garin nan da ita,
ni wlh wani lkcin idan na tsaya ina tunanin inda dijama ta gado wnn halin nata sai inkasa tunano kowa a cikin zuri'armu, ina ganin wata k'ila a can cikin dangin mahaifiyarta tayi gadon wnn halin."
Tsohuwa tace "nidai ya isa haka malam kamata yayi kadinga yiwa dijama Addu'a ba aibatataba."
Kaka yace "ni Sam bana aibata dijama a kullum Addu'a ta d'aya Allah ya shirya mana ita, yabamu ikon rik'e amarta da Allah ya d'ora mana a kai."
Abba ya katse zancan da yace "to Ummie tashi kishiga ciki ki had'o kayanki mutafi marece yafara."
Tana murna tana tsalle zataje birni. Ta tashi tashiga d'aki ta fara had'a kayanta."
Tsohuwa bata son tafiyar dijama dan dai ba yanda zatayi ne, dole ta hak'ura tabari za'a tafi da ita."
Sai da ta shirya kayanta tsaf a jaka ta tallabo jakar tana dariya tana jin dad'i, ta fito."
Abba har ya kammala shirinsa ya fito had'ida yiwa su tsohuwa sallama dijama na gabansa Jakarta a hannunta suka nufi hanyar waje,
Tsohuwa dai Addu'a take masu Wanda takejin kanta duk ba dad'i an d'auke Mata dijamarta."
Kaka kuma saboda dad'i kamar ya zuba ruwa a k'asa yashi, domin yasan yau idan ya kwanta barci ba bak'ocin da zai tayar dashi domin kawo shedun dijama."
Har mota suka rakasu, suna yimasu add'o'i."
Mutanene cimjim gaban motar k'awayen dijama suna bangwana, Abba ya bud'a mota yashiga dijama itama tashiga gidan gaba sai wasar baki takeyi tana dariya tana d'agawa su suwaiba hannu."
Murmushi Abba yayi ya kunna mota ya fara tafiya, Dijama ta lek'o ta k'ofar marfin mota tace "suwaiba idan kukaje gonar Audu wurin satar gwaiba,
idan kukaga Buba kuce masa natafi birni amma zandawo don saina rama abunda yayi mun."
Abba yace Ummie na wai meye hkan? Ki zauna dai dai mana karda kiji ciwo."
Snn tayi saurin gyara zamanta Abba yaja mota
Yatafi yana dariyarta, suka d'auki hnyar kano."
_dijama a birni ikon Allah🤔_
[28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_😅)
Writing
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)
8⃣
Hassan dake waya da Husaini yanajinsa yana kalmar shahada a waya,
gaba d'aya hankalinsa ya tashi ya fito da saurin shi baibi ta kan kowaba ya shiga motarshi yajata da k'arfi ya mik'i hanya,
ya nufi wurin da yaji Husaini yace masa ya kawo."
Cikin minti talatin ya isa wurin ya d'aga wayarsa ya shiga kiran wayar husaini, d'aya daga cikin wad'anda suka kawo masu taimakon gaggawa, ya d'aga wayar yashiga yiwa Hassan bayanin abunda ya faru, ya shaida mashi da cewa gasunan Asibity, Had'ida yimashi kwatancen asibity dasuke."
Cikin tashin hankali Hassan yanufi Asibity idonsa yana zubar da hawaye kamar macce."
A Gaban gawarsu yake dur'kushe yana kuka yana jijjiga Husaini yana fad'in "Husaini katashi don Allah karka mutu kabarni rayuwata idan babu kai bnga amfaninta ba,
kai kad'ai ne d'an uwana jinina Wanda nake shawara dashi husaini katashi."
Kuka yakeyi sosai kamar ya d'auke numfashi yana jijjigar gawar Husaini."
Mutanen wurin suka tallabeshi suka bar wurin dashi ana bashi hkr,
Snn dga k'arshe yakira mahaifan Bilkisu da sauri suka zo, snn ya kira Kaka da tsohuwa, a tare sukazo asibity aka d'auki gawarsu aka nufi Kano da su gidan Hassan akayi masu wanka da sutura aka kaisu gidansu na gskiya."
A nan gidan Hassan akayi amsar gaisuwa,
Inda Dijama tana rungume a hannun tsohuwa tana bata madara."
Hassan yayita lallashin tsohuwa akan ta amince tabari Hajara taci gaba da shayar dasu tareda fateema,
Amma tsohuwa ta kafe tace "sam bazai yiwoba, kuma da anyi sadakar bakwai zatayi tafiyarta gida, tare da dijama tazata tafi Dan bazata bartaba."
Hankalin Hassan ya kuma tashi, ya shiga rok'on tsohuwa akan ta amince ta bar masa dijama zai kula da ita ya had'ata da 'ya'yanshi yanda bazata tab'ayin maraiciba."
Tsohuwa tace "Sam bazai yiwoba, itama ita zata dinga gani a gabanta tana jin sanyi tana d'ebe mata kewar Husaini da tarasa."
Hakan akayi bayan sadakar bakwai ta harhad'a kayanta ta goya Dijama zata tafi, direba yana jiranta."
Hassan da iyanlansa suka yomata rakiya, ko wannensu idonshi cike da hawaye domin ji sukeyi mutuwar Husaini ta kuma dawo masu sabuwa."
Mahmud kuka yakeyi sosai yana birgima yarik'e tsohuwa yana fad'in bazataje masa da dijamarsaba."
Kuka yakeyi sosai kowa ya tausaya masa, tsohuwa tace a had'o masa kayanshi sutafi tare idan hutunsu na mkranta ya k'are sai aje a d'aukoshi, tun da daman hutun makaranta sukeyi."
Haka kuwa akayi, aka had'awa Mahmud kayansa yana murna yana dariya, sukayi masu rakiya zuwa mota direba yazasu suka d'auki hanyar Tofa."
Wnn shine dalilin zaman dijama a wurin tsohuwa a cikin k'auyen tofa."
Tsohuwa bata son jin kukan dijama bata son ganin b'acin ranta,
Haka mahmud da zarar akayi masu hutun mkranta zai tsira fita a kan dole sai ankawoshi wurin tsohuwa yaga dijamarsa."
Itama dijama tun tana k'arama da zarar Mahmud yazo hutu,
bata kuma yarda da kowa sai mahmud a tare sukecin abinci a tare suke kwana, idan tayi kashi shike wanke mata, shike mata wanka,
zarar hutunsu ya k'are Idan direba yazo d'aukarshi, da kuka da komai suke rabuwa,
Tsohuwa tana jijjinawa wannan shak'uwa tasu, haka shima Abbah wato Hassan kenan shima yana jijjinawa wann soyayyar tasu."
Wnn dalilin ne yasa mahmud duk lokacin da suka samu hutu baya iya zama garin kano sai dai yatahowarsa Tofa yayi zamansa saboda dijama, har zuwa yanzun da girma yazo masa ya mallaki hnkalin kansa yashiga jami'a a yanzun yana zangonshi na k'arshe a dgree d'insa."
Tun tashin dijama a rayuwa babu abunda ta nema ta rasa, domin tsohuwa da Kaka da muhmud basu da wani buri da yawuce a koda yaushe su farantawa marainiya, basa son ganin kukanta."
Abba shike d'auke da karatunda da duk wani Abu da yashafi rayuwata, tunda tsohuwa ta kafe a kan cewa baxata bashi itaba, amma shi har ga Allah yaso ya d'auki dijama ya had'ata da yaranshi yabata gata Wanda yin hkan shi zai sanyashi ako da yaushe zai dinga ganin kamar Hussainin shi yana nan bai mutuba."
Tun tashin Mahmud shi mutum ne mai son a girmama shi, baya d'aukar raini a gida ko a waje,
K'annansa su fateema da zarar yashigo a gida kowa yake kama Kansa, idan ba hakan ba da zarar sunyi abunda ba dai dai ba a nan take zai hukuntasu. Ya azzabtar dasu yayi tafiyarsa."
Wnn dalilin ne yasa yaji ya tsani dijama saboda rashin jinta, gata bata gane karatu,
Kuma bata ganin girmanshi kwata kwata ta rainashi raininda ba Wanda ya tab'a yi mashi irinshi."
Tsohuwa bata ganin laifinta duk rashin kunyar da zatayi jan maganar da zatayi a waje tsohuwa bata ganin laifinta,
Wann dalilin yasa a rayuwarshi yaji ya tsaneta basa shiri kwata kwata.wani lokaci Sai ya d'auki niyar cewa bazai k'ara zuwa Tofa hutuba saboda rashin kunyar dijama,
Amma da zarar anyi masu hutun ko na kwana biyu ne baya iyawa sai yazo Tofa yayi hutunsa snn ya koma."
Kamar ynzun da Hutu yazo yayi, bai iyar da kammala hutun nashiba, ta had'ashi dasu Buba, ya tattara kayansa ya koma warsa gida Wanda tsohuwa tacika da mmki."
*Wnn kenan mudawo labari*
***************
Mahmud na komawa gida, kowa ya cika da mmki dan ganin hutunsu bai k'areba ya dawo."
Abba ne yakirashi a falonsa yana tare da momy mahaifiyarsu yashiga tmbayar sa, lafiya me yadawo dashi bayan ba hakan ya sababa hutunsu bai k'areba?"
Murmushi yayi ya sunkuyar da kansa yace " Ba komai Abba hakan nan kawai nadawo babu abunda ya faru."
Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "ina fatan kowa yana lafiya?"
Ya 'yata Ummie ina fatan tana cikin k'oshin lfy?"
Murmushi mahmud ya k'ak'aro yace kowa lfy Abba. Kaka ne kawai yake fama da ciwon k'afa, amma kuma yaji sauk'i sosai."
Abba yace subahanallahi!!! Ai kuwa zanje cikin _weekend_ d'in nan nadiboshi,
Momy tace "Allah yabashi lafiya."
Suka amsa da "Amin gaba d'ayansu."
Snn Abba yayi kyaran murya yadubi mahmud da kyau yace "dama ko baka dawoba zankira ka, a waya nace kadawo, domin Alhaji Atiku commonden d'in sojoji wnn abokin nawa yayo mun waya a kan cewa anfitarda form na sojoji ya d'aukar maka d'aya,
Saika had'a takardunka katafi Abuja cikin satin nan zakuyi jarabawa Allah yabada sa'a yasa a dace."
Suka Amsa da Amin."
Sannan Mahmud yayi masu sallama ya fito yanufi d'akinshi yana kuma jin haushin dijama a ranshi."
**************
Dijama zaune a kusa da tsohuwa tana turo baki, tsohuwa nayi mata fad'a akan ta fara gajiya da halinta kullum saita janyo mata fad'a da fitina a mak'ota."
Ta mik'a mata kud'i tace "gashi kitafi gidan jummai ki kai mata kud'in zubi, dan Allah dijama karki tsaya kuma karki kula kowa a hnya kiyi tafiyarki."
Mik'ewa tsaye tayi had'ida turo baki tana gun guni, sannan ta karb'i kud'in ta fita."
Tana tafiyarta cikin natsuwa abunda bata tab'a yiba, k'awayenta su lantana tagani sunfito daga rafi, suka had'a baki suna mata magana suna cewa "dijama 'yar gidan tsohuwa sai ina?"
Kaka dake zaune gefe d'aya yace "gwara da Allah yasa ka nan a gaban idonka hakan ta faru,
Kullum a rana d'aya sai sama da mutum goma sunkawo k'ararta tsohuwa ke tare mata,bata son ganin b'acin ranta."
Amma tunda ynxun ka ganewa idonka sai ka d'auki mataki, akai,
Ga ganta nan Ko mkranta bata zuwa gaba d'aya makarantar biyu Arabic da boko duk ankorota, saboda hatsabibancinta gata bata gane komai sai fitina da rashin kunya. Yakai k'arshen maganarshi yana zungura mata sandar hannunshi."
Tsohuwa bata tanka masuba saima taja bakinta tayi shuru, domin yau itama dijama ta kaita bango."
Abba yayi kyaran murya ya dubi tsohuwa yace "inna kiyi hak'uri kibani dijama natafi da ita na nema mata ilimi Wanda zatayi dogaro da kanta tazama abar Alfahari a cikin Al'umma, yin hkan shi zai Sanya mana natsuwa a zuciyarmu ganin mun rik'e marainiyar Allah tsakani da Allah."
Kaka yayi karaf yace "aikuwa wlh da ka taimakemu ka taimaki mutanen garin nan mundun katafi da dijama kabar garin nan da ita,
ni wlh wani lkcin idan na tsaya ina tunanin inda dijama ta gado wnn halin nata sai inkasa tunano kowa a cikin zuri'armu, ina ganin wata k'ila a can cikin dangin mahaifiyarta tayi gadon wnn halin."
Tsohuwa tace "nidai ya isa haka malam kamata yayi kadinga yiwa dijama Addu'a ba aibatataba."
Kaka yace "ni Sam bana aibata dijama a kullum Addu'a ta d'aya Allah ya shirya mana ita, yabamu ikon rik'e amarta da Allah ya d'ora mana a kai."
Abba ya katse zancan da yace "to Ummie tashi kishiga ciki ki had'o kayanki mutafi marece yafara."
Tana murna tana tsalle zataje birni. Ta tashi tashiga d'aki ta fara had'a kayanta."
Tsohuwa bata son tafiyar dijama dan dai ba yanda zatayi ne, dole ta hak'ura tabari za'a tafi da ita."
Sai da ta shirya kayanta tsaf a jaka ta tallabo jakar tana dariya tana jin dad'i, ta fito."
Abba har ya kammala shirinsa ya fito had'ida yiwa su tsohuwa sallama dijama na gabansa Jakarta a hannunta suka nufi hanyar waje,
Tsohuwa dai Addu'a take masu Wanda takejin kanta duk ba dad'i an d'auke Mata dijamarta."
Kaka kuma saboda dad'i kamar ya zuba ruwa a k'asa yashi, domin yasan yau idan ya kwanta barci ba bak'ocin da zai tayar dashi domin kawo shedun dijama."
Har mota suka rakasu, suna yimasu add'o'i."
Mutanene cimjim gaban motar k'awayen dijama suna bangwana, Abba ya bud'a mota yashiga dijama itama tashiga gidan gaba sai wasar baki takeyi tana dariya tana d'agawa su suwaiba hannu."
Murmushi Abba yayi ya kunna mota ya fara tafiya, Dijama ta lek'o ta k'ofar marfin mota tace "suwaiba idan kukaje gonar Audu wurin satar gwaiba,
idan kukaga Buba kuce masa natafi birni amma zandawo don saina rama abunda yayi mun."
Abba yace Ummie na wai meye hkan? Ki zauna dai dai mana karda kiji ciwo."
Snn tayi saurin gyara zamanta Abba yaja mota
Yatafi yana dariyarta, suka d'auki hnyar kano."
_dijama a birni ikon Allah🤔_
[28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_😅)
Writing
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)
8⃣
Hassan dake waya da Husaini yanajinsa yana kalmar shahada a waya,
gaba d'aya hankalinsa ya tashi ya fito da saurin shi baibi ta kan kowaba ya shiga motarshi yajata da k'arfi ya mik'i hanya,
ya nufi wurin da yaji Husaini yace masa ya kawo."
Cikin minti talatin ya isa wurin ya d'aga wayarsa ya shiga kiran wayar husaini, d'aya daga cikin wad'anda suka kawo masu taimakon gaggawa, ya d'aga wayar yashiga yiwa Hassan bayanin abunda ya faru, ya shaida mashi da cewa gasunan Asibity, Had'ida yimashi kwatancen asibity dasuke."
Cikin tashin hankali Hassan yanufi Asibity idonsa yana zubar da hawaye kamar macce."
A Gaban gawarsu yake dur'kushe yana kuka yana jijjiga Husaini yana fad'in "Husaini katashi don Allah karka mutu kabarni rayuwata idan babu kai bnga amfaninta ba,
kai kad'ai ne d'an uwana jinina Wanda nake shawara dashi husaini katashi."
Kuka yakeyi sosai kamar ya d'auke numfashi yana jijjigar gawar Husaini."
Mutanen wurin suka tallabeshi suka bar wurin dashi ana bashi hkr,
Snn dga k'arshe yakira mahaifan Bilkisu da sauri suka zo, snn ya kira Kaka da tsohuwa, a tare sukazo asibity aka d'auki gawarsu aka nufi Kano da su gidan Hassan akayi masu wanka da sutura aka kaisu gidansu na gskiya."
A nan gidan Hassan akayi amsar gaisuwa,
Inda Dijama tana rungume a hannun tsohuwa tana bata madara."
Hassan yayita lallashin tsohuwa akan ta amince tabari Hajara taci gaba da shayar dasu tareda fateema,
Amma tsohuwa ta kafe tace "sam bazai yiwoba, kuma da anyi sadakar bakwai zatayi tafiyarta gida, tare da dijama tazata tafi Dan bazata bartaba."
Hankalin Hassan ya kuma tashi, ya shiga rok'on tsohuwa akan ta amince ta bar masa dijama zai kula da ita ya had'ata da 'ya'yanshi yanda bazata tab'ayin maraiciba."
Tsohuwa tace "Sam bazai yiwoba, itama ita zata dinga gani a gabanta tana jin sanyi tana d'ebe mata kewar Husaini da tarasa."
Hakan akayi bayan sadakar bakwai ta harhad'a kayanta ta goya Dijama zata tafi, direba yana jiranta."
Hassan da iyanlansa suka yomata rakiya, ko wannensu idonshi cike da hawaye domin ji sukeyi mutuwar Husaini ta kuma dawo masu sabuwa."
Mahmud kuka yakeyi sosai yana birgima yarik'e tsohuwa yana fad'in bazataje masa da dijamarsaba."
Kuka yakeyi sosai kowa ya tausaya masa, tsohuwa tace a had'o masa kayanshi sutafi tare idan hutunsu na mkranta ya k'are sai aje a d'aukoshi, tun da daman hutun makaranta sukeyi."
Haka kuwa akayi, aka had'awa Mahmud kayansa yana murna yana dariya, sukayi masu rakiya zuwa mota direba yazasu suka d'auki hanyar Tofa."
Wnn shine dalilin zaman dijama a wurin tsohuwa a cikin k'auyen tofa."
Tsohuwa bata son jin kukan dijama bata son ganin b'acin ranta,
Haka mahmud da zarar akayi masu hutun mkranta zai tsira fita a kan dole sai ankawoshi wurin tsohuwa yaga dijamarsa."
Itama dijama tun tana k'arama da zarar Mahmud yazo hutu,
bata kuma yarda da kowa sai mahmud a tare sukecin abinci a tare suke kwana, idan tayi kashi shike wanke mata, shike mata wanka,
zarar hutunsu ya k'are Idan direba yazo d'aukarshi, da kuka da komai suke rabuwa,
Tsohuwa tana jijjinawa wannan shak'uwa tasu, haka shima Abbah wato Hassan kenan shima yana jijjinawa wann soyayyar tasu."
Wnn dalilin ne yasa mahmud duk lokacin da suka samu hutu baya iya zama garin kano sai dai yatahowarsa Tofa yayi zamansa saboda dijama, har zuwa yanzun da girma yazo masa ya mallaki hnkalin kansa yashiga jami'a a yanzun yana zangonshi na k'arshe a dgree d'insa."
Tun tashin dijama a rayuwa babu abunda ta nema ta rasa, domin tsohuwa da Kaka da muhmud basu da wani buri da yawuce a koda yaushe su farantawa marainiya, basa son ganin kukanta."
Abba shike d'auke da karatunda da duk wani Abu da yashafi rayuwata, tunda tsohuwa ta kafe a kan cewa baxata bashi itaba, amma shi har ga Allah yaso ya d'auki dijama ya had'ata da yaranshi yabata gata Wanda yin hkan shi zai sanyashi ako da yaushe zai dinga ganin kamar Hussainin shi yana nan bai mutuba."
Tun tashin Mahmud shi mutum ne mai son a girmama shi, baya d'aukar raini a gida ko a waje,
K'annansa su fateema da zarar yashigo a gida kowa yake kama Kansa, idan ba hakan ba da zarar sunyi abunda ba dai dai ba a nan take zai hukuntasu. Ya azzabtar dasu yayi tafiyarsa."
Wnn dalilin ne yasa yaji ya tsani dijama saboda rashin jinta, gata bata gane karatu,
Kuma bata ganin girmanshi kwata kwata ta rainashi raininda ba Wanda ya tab'a yi mashi irinshi."
Tsohuwa bata ganin laifinta duk rashin kunyar da zatayi jan maganar da zatayi a waje tsohuwa bata ganin laifinta,
Wann dalilin yasa a rayuwarshi yaji ya tsaneta basa shiri kwata kwata.wani lokaci Sai ya d'auki niyar cewa bazai k'ara zuwa Tofa hutuba saboda rashin kunyar dijama,
Amma da zarar anyi masu hutun ko na kwana biyu ne baya iyawa sai yazo Tofa yayi hutunsa snn ya koma."
Kamar ynzun da Hutu yazo yayi, bai iyar da kammala hutun nashiba, ta had'ashi dasu Buba, ya tattara kayansa ya koma warsa gida Wanda tsohuwa tacika da mmki."
*Wnn kenan mudawo labari*
***************
Mahmud na komawa gida, kowa ya cika da mmki dan ganin hutunsu bai k'areba ya dawo."
Abba ne yakirashi a falonsa yana tare da momy mahaifiyarsu yashiga tmbayar sa, lafiya me yadawo dashi bayan ba hakan ya sababa hutunsu bai k'areba?"
Murmushi yayi ya sunkuyar da kansa yace " Ba komai Abba hakan nan kawai nadawo babu abunda ya faru."
Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "ina fatan kowa yana lafiya?"
Ya 'yata Ummie ina fatan tana cikin k'oshin lfy?"
Murmushi mahmud ya k'ak'aro yace kowa lfy Abba. Kaka ne kawai yake fama da ciwon k'afa, amma kuma yaji sauk'i sosai."
Abba yace subahanallahi!!! Ai kuwa zanje cikin _weekend_ d'in nan nadiboshi,
Momy tace "Allah yabashi lafiya."
Suka amsa da "Amin gaba d'ayansu."
Snn Abba yayi kyaran murya yadubi mahmud da kyau yace "dama ko baka dawoba zankira ka, a waya nace kadawo, domin Alhaji Atiku commonden d'in sojoji wnn abokin nawa yayo mun waya a kan cewa anfitarda form na sojoji ya d'aukar maka d'aya,
Saika had'a takardunka katafi Abuja cikin satin nan zakuyi jarabawa Allah yabada sa'a yasa a dace."
Suka Amsa da Amin."
Sannan Mahmud yayi masu sallama ya fito yanufi d'akinshi yana kuma jin haushin dijama a ranshi."
**************
Dijama zaune a kusa da tsohuwa tana turo baki, tsohuwa nayi mata fad'a akan ta fara gajiya da halinta kullum saita janyo mata fad'a da fitina a mak'ota."
Ta mik'a mata kud'i tace "gashi kitafi gidan jummai ki kai mata kud'in zubi, dan Allah dijama karki tsaya kuma karki kula kowa a hnya kiyi tafiyarki."
Mik'ewa tsaye tayi had'ida turo baki tana gun guni, sannan ta karb'i kud'in ta fita."
Tana tafiyarta cikin natsuwa abunda bata tab'a yiba, k'awayenta su lantana tagani sunfito daga rafi, suka had'a baki suna mata magana suna cewa "dijama 'yar gidan tsohuwa sai ina?"