← Book details Yar Gidan Tsohowa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 26

Sashe 10

Yar Gidan Tsohowa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Haka aka sanya k'eyar dijama a gaba tare da shugaban mkranta aka sanyasu a mota aka tafi dasu."

Dijama sai Zarar ido takeyi wuk'i wuk'i a bayan mota, shugaban makaranta da juya ya kalleta sunyi ido biyu da ita sai ya wurga mata harara."

A zuciyarshi yana da yasani karb'arta da yayi a matsayin d'aliba."

Fateema na ganin antafi da dijama, ta kuma fashewa da kuka,
tayiwa wani malami magani tace "dan Allah uncle kabani Aron wayarka zankira Abba na na fad'a mashi abunda ke faruwa."

Zaro ido yyi cike da mmki yace "dama kinsanta ne?"

Ta d'aga kai alamar "eh tace yayata ce uwarmu d'aya ubanmu d'aya."

Uncle ya xaro ido waje yace "kina nufin 'yar Alhaji Hassan Adam CE?"

To ya akayi bansanta ba a cikin gidanku?"

Cike dajin haushin tambayarshi fateema ta turo baki tace "bazaka Santaba saboda ba'a garin nan takeba,
dan Allah uncle kabani aron wayar mana."

Yace "Ayyah fateema kiyi hak'uri banada waya a hannuna, amma nasan za'aje da ita ta nuna gidansu."

_kuyi hk'uri d wnn pls yau sai a hnkli_
[28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅

Written
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Bashir_)

*12*

7:30am. Shiri sukeyi domin zuwa makaranta,
tasanya uniform dinta, wad'anda sukayi mata kyau sunfito mata da fuskarta sak 'yar fillo."

Fuskar nan tata tasha hoda da jambaki,
fateema dake gefenta zaune,
ta dubeta tace "dijama ki goge wnn kwanliyar ta fuskarki tayi yawa sosai idan mukaje Anty tana iya sanya hijabinki fari ta goge mki ita."

Ta murgud'a baki tace "bazan gogeba, a hakan zanje kuma bata isa ta gogemun kwanliya taba."

Fateema zata kuma yin magana tajiyo sautin muryar yaya Mahmoud yana fad'in "wai bazaku fitoba lokaci fa na tafiya, Allah duk kuka kuskura kuka bari na hawo saman nan sai jikinku ya gaya maku."

Da sauri fateema ta d'auki school bag d'inta ta goya. Bata kuma bi takan dijamaba don tasan halin yaya Mahmoud ba sauk'i ne dashi ba."

Dijama da ke k'ok'arin sanya sendel a k'afarta tana turo baki cikin magana k'asa k'asa tace "to idan ka hawo karka barmu da rai ka kashemu."

Ido fateema ta zaro waje tace "yayan kike cewa hakan lallai dijama bakisan halin yaya Mahmoud bane, tana fad'in hakan tayi saurin bud'e k'ofa ta fita, tabar dijama na sanya takalmi."

Tana gama sanyawa itama ta biyo bayanta, ta fito tana tafiya harda wani rangwad'a takeyi wai ita 'yar boko."

Gaba d'anyansu Suna babban falo zaune suna Brest fast, Abba da shirinsa na zuwa Office khalil shima da shirinsa zuwa makaranta BUK."

Mahmuod a tsaye da key d'in mota a hannunshi yana jiran fitowarsu ya kaisu, yadawo yana da inda zaije, har sun b'ata mashi time."

Fateema ta fara fitowa sann dijama ta biyo bayanta,
Abba na ganinsu cikin uniform yaji dad'i sosai sai murmushi yakeyi a fuskarshi,
Momy itama murmushin takeyi tana fad'in "iye 'yan matana lallai kunyi kyau musamman 'yata ummie."

Mahmoud dake tsaye gefe d'aya yanayi yana kallon agogon gwal dake d'aure a hannunshi."

Khalil ya d'aga kansa yana ya mutsa fuska yana kallon dijama. Da take k'ok'arin k'arb'ar flast d'in break d'insu. Wanda momy ke mik'a masu,

Ido biyu yayi da fuskar dijama datasha kwalliya,
mai zaiyi idan ba dariya ba,

Dariya yakeyi yana nuna fuskarta yana fad'in tab "mutumin k'auye baiyi ba wlh ke wai kwanliyace kikayi hakan ko meye?"

Brother wlh karka bari wnn abar ta shigar maka mota, ai sai kuzama abunda kwatance duk inda kuka gifta."

Cikin zafin rai Abba ya doka mashi tsawa da k'arfi yace "khalil tashi kafita karna na sab'a maka wlh."

Momy Itama tabishi da harara tana fad'in "ni bansan irin rayuwar khalil ba a cikin gidan nan."

Ta jawo hannun dijama dake tsaye wuri d'aya tana cije baki had'ida girgiza kai, ranta ya b'aci matuk'a."

Mahmoud dake tsaye a inda yake, ya had'e fuska,
yayi saurin waigawa ya wurgawa khalil harara cike da jin haushinsa."

Mmy ta rik'o hannuta tace "zo nan 'yata na gyara maki fuskarki karki damu da abunda khalili yayi mki hka halinshi yake."

Momy tashiga gyara mata fuskarta, ta goge mata janbakin da 'yar gira, ta kuma rage mata hudar fuskarta,
Sauran kwallin da tashafa a idonta ne yak'i goguwa. Gudun karsuyi latti momy ta barta haka suka tafi."

Bayan sunfita ne Abba ya maida kallonsa ga momy yace "nafara ganin take taken khalil a gidan nan a kan ummie zan d'aukar mashi mummunan mataki idan hakan ta kuma faruwa a kan idona."

Inason Allah yabani iko da nisan kwana nacika Alk'awarin da nayiwa d'an uwana kafin ya mutu,
na aurawa muhmud Ummie idan ba hakan ba a yanda naga khalil na kyamatarta a gidan nan da bbu abunda zai hana na aura mashi ita, domin kawai naga iya karshi."

Hak'uri momy kawai take bashi domin ganin ranshi ya b'aci sosai."

A bayan mota suka shiga mahmud bai kulasuba, fuskarshi a had'e, ya tayar da
motarsa yaja yanufi makarantarsu."

Suna shiga cikin makarantar yayi parking d'in motar shi a cikin harabar makarantar,
, tun kafin ya fito dijama ta rigashi fitowa harwani sauri takeyi k'asa na tashi,
Da sauri ya doka mata tsawa yace "ke 'yar k'auye da Allah malama ki dawo ki tsaya."
Kina wata tafiya k'ura na tashi sallan ki b'atawa mutane jiki da k'asa, 'yar k'auye kawai
Takkwala mai kwanyar kifi, kamar da gske sai kace ganewa kikeyi.
To bari na fad'a mki nan ba k'auye bane mudun kikayiwa malamai rashin kunyar da kikeyi a k'auye tsinanen dukan tsiya zakici kuma ba Wanda zai rama maki."

Juyowa tayi tana kallonshi ta sunkuyar da kanta k'asa, a rayuwar ta bbu abunda ta tsana irin yaya Mahmud ya kirata da mai kwanyar kifi, ta d'aukarwa kanta Alk'awarin cewa zata maida hankali tayi karatu Wanda yaya Mahmud sai yayi mmkinta,
a lokacin zata bud'e baki ta mayar masa da raddin takkwalar da yake kiranta da ita."

A fusace ya juya wurin fateema da mmkinsa bai gantaba sai ma hangota da yayi ta kusan shigewa class."

Gaba ya shige dijama na biye dashi, office d'in shugaban mkranta ya shiga ya gabatar da dijama, sann daga k'arshe gaban idonsa aka kaita class,
Aji d'aya aka ajiyesu da fateema kamar yanda ya buk'ata, saboda fateema ta dinga koya mata wasu abubuwa wad'anda bata saniba."

Sai da yaga shigarta aji sann ya shiga motarsa ya dawo gida."

Da shigarta ajin d'alibai sai kallonta sukeyi ganin yanda ta tsurawa silin roba ido sai kallo takeyi, gaba d'aya sai k'arewa ajin kallo takeyi da kujerun dake ajiye a cikin class d'in."

Fateema ta hango a can zaune tayi saurin bud'e baki tare da d'aga murya tace "lah fati Ashe aji d'aya aka ajiyemu ai kuwa naji dad'i."

Gaba d'aya ajin suka tuntsere mata da dariya, wata 'd'iyar chiyaman d'in garin,
Wanda suke mak'otaka da Abba, tace "amma dai ke 'yar k'auyece wlh."

Suka kuma shek'e mata da dariya, wata d'aliba daga cikinsu tace "dubi yanda ta shafa kwanli a idonta, ta fad'i hakan had'ida nuna idon dijama suka kuma shek'ewa da dariya."

Dijama taji haushi sosai, fateema ta mik'e tsaye ta kama hannun dijama da tayi tsaye takasa zama saboda jin haushi, ta zaunar da ita a kan kujera kusa da ita."

Dijama taja wuri d'aya ta zauna tana sake sake a ranta,

Malam mai English ya shigo ya fara yi masu karatu ta kashe kunne ta kwantar da hankalinta tana saurare kuma tana fahimta."

K'araurawa taji an buga alamar antashi break fast, hakan yayi dai dai da fitar malma mai English, d'alibai suka fara fita waje domin cin abinci."

Da sauri dijama ta duro a kan kujera ta shagaban 'yar gidan chiyaman
karon farko mari ta fara kai mata, ta cire hijabin jikinta tasha d'amara cikin d'aga murya tace "ubnwa kike cewa 'yar k'auye?" Tashiga nusarta, baji bagani, saida bakinta ya fashe da jini,
gaba d'aya ta b'ata gaban hijabinta,
D'aya yarinya wanda harda ita wurin yi mata dariya,
ta matso wurin dijama ta cimuimuye mata riga a bayanta,

Dijama tasanya k'afa ta bayanta ta shure mata baki, aikuwa yarinya ta kwatsa ihu ta duk'e ta rik'e bakinta da jini yaketa zuba."

Ihu 'yan aji keyi da gudu suka fita suka kira shugaban makarantar."

Babu abunda fateema keyi sai aikin kuka,
Dama kuka baya mata wuya, saboda kwata kwata fateema bata da fad'a batason tashin hankali,
sanyin hali ke gareta."
[28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅

Written
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Bashir_)

*14*

12:30pm Abba ne zaune a Palo ya dawo daga office Mahmud zaune a gefensa yana shaida masa cewa Alhaji Atiku ya kirashi a waya akan cewa ya xama cikin shiri satin nan ya shirya kayansa ya sameshi Abuja domin sunansa ya fito zasu wuce wurin trening."

"Alhmdulillahi Abba yace,
Yana murmushi cike da jin dad'i da farin ciki, ya dubi Mahmud yace "Alhaji Atiku mutumin k'irkine abokina ne tare muka tashi mukayi makaranta d'aya dashi,
A rayuwata ta duniya bbu abunda Alhaji Atiku zai nema gareni banyi mashiba indai baifi k'arfinaba, saboda yanda yake nunamun k'aramci da k'auna."

Mahmud inaso idan kaje ka kula da kanka,
Kabishi sau da k'afa kayi mashi biyayya kamar yanda kasan kanayi mun Allah yayi mka Albarka."

Bai rufe bakinsaba fateema tashigo ko sallama bbu idonta yayi ja alamar taci kuka,har ta gaji."

Mahmud ya dubeta cike da kulawa yace "fateema meyasameki?"
Abba yace "ina Ummie take?"

Kafin tabasu amsa sukajiyo jiniyar motar 'yan sanda a k'ofar gida,
Saiga Baba maigadi yashigo da saurinsa ya zube k'asa gaban Abba yace "ranka ya dad'e 'yan sanda na sallama da kai a waje."

Abba ya zaro ido cike da mmki yace "yan sanda?"
Meyafaru?"

Mahmud shima hakan,
Fateema ta kuma fashewa da kuka tace "wlh sune,
Momy ta taso tashiga girgixata tana tambayarta "sune suwa?"
Meya faru?"

"Sune wad'anda suka kama dijama suka tafi da ita,
Mahmud yayi saurin juyowa ya kalleta, ya kuma kallon Abba da momy, yace "dijama tayi halinta kenan tajanyo mana fitina."

Suka d'unguma gaba d'ayansu suka fita,
Mahmud ke gaba sai Sauri yakeyi Abba na biye dashi snn momy da fateema."

Yana tukarar motar ya hango dijama zaune a bayan mota sai zarar ido takeyi"
Chapter 10 · 0% Book details