← Book details Yar Gidan Tsohowa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 26

Sashe 21

Yar Gidan Tsohowa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sulaiman yace nidai ina rok'on Alfarma da abani dijama na aureta nayi ta biyu da ita,
Koda dai nayiwa wife d'ina Alk'awarin baxan mata kishiyaba."

Mahmud yace "ai kuwa idan kanasonta na baka amma ka shirya rabuwa da matarka ta girma da arxiki idan ba hakan ba to zakuyi rabuwar rashin arziki,

Dan na rantse maka dijama saita cinnawa gidanka wuta dakai da mtarka da d'anka duk sai kun k'une tana gefe tana kallonku saboda fitina."

Sulaiman ya kuma sakin dariya yace " wnn dijama na matsu na ganta."

Mahmud yace ai ganinta zakayi, a hakan sukaci gaba da firar dijama har bacci ya d'aukesu gaba d'ayansu."

*******************

7:30am Mahmud ya kira Abba yake shaida masa yau ne akeyiwa su dijama Hutu atafi a d'aukota."

" Abba ya kalli momy suka saki murmushi,Abba yace "yi hak'uri Mahmud ynxun shirin da nkeyi kenan da kaina zanje na d'auko maka dijamarka."

Gaban mahmud ya yanke ya fad'i yace "Abba dijamata fa kace?" Tab Allah ya tsaran INA zan iya da fitinar dijama."

Abba yana murmushi yace "kuma fa hakan ne, bari kawai natafi na d'aukota sukayi sallama Mahmud ya kashe wayar,"

Khalil da shigowarsa kenan yaji Abba na waya yasan da Mahmud yakeyi irin ynda yaga yana sakin fuska yana dariya, maganar da taja hankalinsa gareshi itace "bari naje na d'auko maka dijamarka."

Gabansa yaji ya fad'i ransa ya b'aci "wato dijamarsa harma ta zama tasa?"

Yayi k'ok'arin saita Kansa, ya durk'usa k'asa ya gaidasu harda wani sunkuyar da Kansa k'asa,
Suka amsa mashi cike da kulawa."

Yace "Abba kabar shi natafi na d'aukota, Abba yasaki murnushi yace "ai na d'auka makaranta zaka tafi?"

Yace "bama da karatu ynxun sai zuwa 3pm Abba yace "OK to katafi ka d'aukota Allah ya tsare."

Fateema ta fito cikin kwanliyarta ta atamfa Wanda tayi mata kyau sai wani k'amshi humra take fitarwa mai d'aga hankalin lafiyayyan d'a namiji,"

Humra momy ce Wanda itama bata shafata sai idan zata kasance tare da Abba, saboda da zarar ya shak'i k'amshinta hankalinshi zai d'aga yajishi yana son ya kasance da ita."
tashiga d'akinta ta d'auka ta sanya momy bata saniba."

Tana k'arasowa wurin k'amshin humra ya kuma k'ara game pallon."

K'amshin yana dukan hancin khalil gaba d'aya hankalinshi ya yatashi cikin minti biyu idonshi ya rikid'e zuwa launin ja wata irin wutar sha'awa yaji ta taso masa."

A kasalance ya juya ya kalli fateema yace "ubnwaye yabaki wnn turaren da kika sanya?"
[28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_)😅

Writing
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)

*26*

Yayi kanta zai daketa, yana fad'in idan bakije kika cire kayan nan masu kamshin wnn turarenba saina k'akk'aryaki."

Momy tace "karka kuskura ka daketa, meta maka?" Ina ruwanka da turaren da tasanya,
Da Allah malam wuce katafi inda zakaje lokaci yana tafiya."

Abba ya tsura mashi ido yana kallonshi ganin ynda idonshi ya canxa, a nan take duk yafita hnyacinsa."

Bai kuma yin maganaba ya juya ya tafi,
Fateema tace Dan Allah yaya kayi hak'uri katafi dani yanxun zancire kayan,nayi ynda kace,
sai da ya kai bakin k'ofa snn ya juyo ya sakar mata harara yace "wlh bbu inda zanje da keba." Ya sa kai ya fita."

Gaba d'aya baya cikin hanyacinsa wata kalar sha'awa take fisgarsa, Wanda har yake tunanin baya iya zuwa inda zaitafi batare da ya samu sukunin abunda ke damunsa ba."

Ji yayi mararshi ta k'ulle mashi da sauri yayi parking gefen titi yana sauke numfashi a hankali, sai da ya samu ta lafa mashi snn ya d'aga waya yakira budurwan shi Ashanty baby yanzun itace budurwar da yakeji da ita kasan cewa shine mutum na farko da ya bud'eta a Leda."

Dama tana kusa da inda yake cikin minti goma ta iso wurinshi,
Yana ganinta kamar wani mayunwacin zaki, tun a motar ya fara shafarta yana tsotsar bakinta zuwa Brest d'inta jikinsa har wani rawa yakeyi kamar Wanda yaga nama."

A hankali ta cireshi daga jikinta ta lallab'ashi ya tayar da motar suka nufi gidan Ahmad."

Baibi ta kan Ahmad ba kai tsaye d'akinsa ya nufa inda yake holewarsa,
Gadan gadan yanufi Ashanty ya shiga cire mata kayan jikinta,
Ya kamota ya jefa a kan gado ya shiga aika mata da sak'onninsa."

Sai da ya gama biyan buk'atarshi yajishi ya samu natsuwa snn ya tashi yayi wanka ya Sanya kayanshi had'ida mik'awa Ashanty kud'i masu yawa,
Girgiza kai tayi tace "Khalil INA sonka kasani INA baka kaina ne Saboda soyayyar da nake maka ba dan kud'iba Dan Allah Khalil karka yau dareni."

Murmushi yayi ya shafa gemunsa yace "nima hakan karki damu dani dake mutuwa kad'ai ce zata rabamu."

Yana kaiwa nan ya ajiye mata kud'in a gefen gado, yace kiyi amfani dasu ki hau abun hawa. Sauri nkeyi Abba ne ya aikeni, bai tsaya yaji abunda zata fad'aba yayi tafiyarshi ya shiga motarsa ya nufi makarantar su dijama."

Dijama na can zaune wuri d'aya tana kallon wad'anda ake zuwa d'auka d'aya bayan d'aya,

Sanye take cikin uniform wad'anda sukayi mata kyau ta tufke gashin kanta a tsakiyar kai tayi acuci maxa,
Babu kwanliya a fuskarta amma da zarar ka ganta saita burgaka saboda _beautifull face_ d'inta,
idonta xara Zara farare fes da d'an k'aramin bakinta, k'atuwar _school bag_ d'inta goye a bayanta,
gefenta kuma akwatin kayanta ne."

Can ta hango Khalil ya shigo da mota, bai ganta ba tana ganin shine yaxo d'aukarta taja dogon tsaki had'ida murgud'a baki kamar yana ganinta, tace "wnn d'an rainin hankalin yazo d'aukata?"

Yi tayi kamar bata ganshi ba, shi kuma sai dube dube yakeyi yana tunin ina zai ganta?"

Cikin d'alibai yake kutsawa yana dube dube ko zai ganta, tana can gefe d'aya tana kallonshi tana harararshi tare da mere mashi baki☹."

Senior Rukayyah ta hangoshi ta nufoshi tana rangwad'a tace "ina yini yayanmu."

Lfy glau yace had'ida sauke ajiyar zuciya tare da shafe zufar da take fito mashi a fuska
Ya kalleta yace "banga dijama ba, nayi nemanta bn gantaba, pls Dan Allah tayani nemanta."

Murmushi tayi had'ida fari da ido, ta kalli inda dijama take zaune, ta nuna mashi ita,"

Bai kuma bi ta kantaba ya nufi wurin dijama da saurinshi."

Tana hangoshi ya nufo wurinta ta had'e fuska ta sunkuyar da kai k'asa tana duba wani littafin turanci dake rik'e a hannunta."

Kallon fuskarta yakeyi Wanda gaba d'aya ta tafi da imaninshi,
Har yazo dafda ita bai San lokacin da ya kai gurfane a gabanta ba, had'ida d'ora hannunshi a kan face d'inta yashafa yace "beauty kin wahalar dani wurin nemanki."

mik'ewa tayi da sauri ta taja da baya tana harararshi cike da tsiwa tace "wacece beauty?"
Sunana ne bakasani ba?"
Daka ce na wahalar da kai ai ina ganin ba dole nayi maka.
Danasan kai zakazo d'aukata dana shiga motar haya na koma gida da kaina."
Duk Wanda ya nuna maka tsana da rashin so komai zai iya aikata maka,
A shirye nake da duk abunda kayi mun sai na rama."

"Yi hak'uri yace da ita."
Tana kaiwa wnn taja a kwatinta tayi gaba,
Da sauri ya mik'e tsaye yanufeta harda d'an gudunshi ya karb'i akwatin ya rik'e yanufi mota dashi."

Bayan ya sanya akwatin a but
Ya zagaya ya bud'e mata k'ofa ta shiga snn ya shima yashiga zai tayar da motar kenan senior Rukayyah ta matso daf da murfin motar tana kashe murya tace "yaya Mahmud ko sallama bbu?"

Kallo ya bita da shi ya d'an saki fuskarshi yace "eyyah kiyi hkr na mnta bamuyi sallama ba, amma sai dai ba Mahmud bane, Khalil ne k'anin Mahmud."

Xaro ido tayi tana kallonshi tace "kai amma gskya Kuna kama sosai da junanku,
Bai bari ta kuma yin wata magana ba ya Ciro kud'i masu yawa ya mik'a mata yaja motarsa yayi tafiyarshi."

Tafiya sukeyi sannu a hankali Khalil yi yake yana kallonta jinsa yakeyi kamar ya sace ya gudu saboda yanda take burgeshi."

Dijama kuma ta kauda kanta gefe d'aya sai kallon titi takeyi,
Domin jinta takeyi kamar a k'aya, take ta matsu ta ganta a gida."

Ganin tsanarshi yayi a idonta ya fahimci bata son ta had'a ido dashi, kuma ba hakan take yiwa mahmud ba."

Yaja gefen hanya yayi parking, yana kallonta cikin wata siga Wanda yake yaudarar yan mata da ita."
Su yakeyi ta juyo su had'a ido, dashi amma tak'i."

Jin yayi parking a gefen titi tayi saurin jiyowa cike da tsiwa da kuma k'inshi a ranta, tace "malam lafiya meke faruwa?"

Ido ya k'ura mata yana kallon d'an k'aramin bakinta Wanda yakeji kamar ya kamota ya rungumeta ya tsotse mata shi, ya kashe murya had'ida langwab'e kai cikin murya k'asa k'asa yace "meyasa kika tsaneni?"
Meyasa bakyason had'a ido dani menamaki?"

Na rok'eki ki manta da duk wani abu da yafaru a can baya ki d'aukeni a matsayin d'an uwanki kamar yanda kika d'auki mahmud."
Danida Mahmud duk d'aya ne a wurinki, amma sai nake ganin tsananin tsanata a idonki."

Da sauri ta juyo ta kalleshi ta wurga mashi harara snn tace "ka daina had'a kanka da yaya Mahmud domin kuwa bai tab'a tsanata kamar yadda ka tsaneni ba,
bai tab'a nunawa duniya cewa baya k'aunataba kamar yadda kanunawa duniya baka k'aunata

Gaba d'aya rayuwarka babu abunda ka tsana sama dani,
Dan haka har abada bazan tab'a mnta k"iyayyarka gareniba."
Kasanyawa rayuwar ka na tsaneka kamar ynda kaima ka tsaneni."

Yaya Mahmud yafiye munkai, nesa ba kusaba, bazaka tab'a kaiwa matsayin yaya Mahmud a wurinaba."
Tana kaiwa nan taja dogon tsaki had'ida murgud'a baki ta kawar da kanta gefe d'aya."

Runtse idonsa yayi yana tunanin magagganunta domin sunyi mashi ciwo sosai ya rasa abunda zai furta mata Wanda zai ganar da ita cewa yanzun ya canza ya daina k'inta a ransa, asalima yanxun komai nata burgeshi yakeyi."

Ganin shurun yayi yawa baya da niyar tafiya ta kuma juyawa ta kalleshi cike da tsana tace "idan baka tashi tafiya ba ni zanfita na samu abun hawa na k'arasa gida.
Ko kuma wlh infita na Tara maka jama'a in sanya ayi maka dukan tsiya daga k'arshe kuma nayi tafiyata."

Tana k'ok'arin bud'e k'ofar ta fita,
sanin halinta da yayi yasa shi yayi saurin rik'o hannunta yana fad'in yi hak'uri dawo mutafi,."
Chapter 21 · 0% Book details