Sashe 2
Yar Gidan Tsohowa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ladiyo dayake tasan halin dijama bataji tsoroba illah ta mik'e a hasale tanufesu,
Suna ganinta tayo kansu suka zuba a guje suna dariya harda rik'e ciki, suna fad'in wasa mukeyi
macijin roba ne."
Yahaya gaye da saida yayi nisa sosai da wurin sannan ya tsaya yana zarar ido yana maida numfashi sama sama, a can yajiyo sautin dariyarsu dijama suna fad'in wasa mukeyi macijin roba ne."
A hasale shima ya nufesu, cike dajin haushin muzantashi da sukayi a gaban budurwanshi, bugu da k'ari ga gudun da yayi harda tusa yasaki."
Aikuwa ya tunkarosu gadan gadan, dijama na ganin haka ta d'aga murya da k'arfi tace "kowa yayi ta kansa."
Suka zuba da gudu ko wannensu yanemi hanyar tsira."
Juyawar da zatayi ta gudu, taji tayi karo da mutum a dai dai lokacin da yahaya gaye yanufota, aikuwa ta mak'alk'ale mutumin wanda batasan kowaye shiba,
D'aga idon da zatayi sai taga Ashe yaya Mahmud ne."
Mari ya kwad'a mata, ya rik'a hannunta ya mik'awa yahaya gaye yace "gata kaci ubanta,
Domin ko mu kanmu mungaji da ita, mungaji da hali irin nata, kayi mata dukan tsiya ninace."
Yahaya gaye babu abunda yakeyi sai ruwan masifa,
Ladiyo ta matso kusa da ita ta xungure mata kai tace "kinci darajar yayanki da yau sai na lahira yafiki jin dad'i,
Dijama da sai zarar ido takeyi tana kallon fuskar yahaya gaye tanaso tayi dariya amma ba hali."
Mahmud yaja hannunta yana rankwashinta a kai yana mata fad'a, sai da sukazo k'ofar gida ta kwace hannunta da k'arfi tashige gida tana fad'in Allah ya isa mugu kawai."
Da Sauri yabita cikin gidan yana Neman ya rik'ata, aikuwa ta fad'a d'akin tsohuwa da gudu,
tsohuwa na ganinta tayi saurin tashi zaune tace "babu Wanda zaibiyoki sai mamuda domin nasan shi kad'ai ke k'ok'arin yaganki bakya motsi, hakan yayi dai dai da zuwanshi k'ofar d'akin yana huci, tsohuwa tace "karka kuskura ka shigo min d'aki
kaji na fad'a maka."
Yaja yayi tsaye a k'ofar d'aki yana huci,
Saida dijama ta kalli fuskarshi ta tuntsire da dariya harda rik'e ciki, dariya takeyi sosai, sai ta kuma kallonshi ta kuma tuntsirewa da dariya,
Ya kuma hasala, tana ganin ya hasala sosai tace "yaya kasan ko menakeyiwa dariya?"
Ya wurga mata harara had'ida girgiza kai."
Tace "ba komai yake bani dariya ba sai yahaya gaye, yanda yasaki tusa ya zuba a guje."
Shima kanshi gudun da yaga yahaya gaye nayi sai da yabashi dariya kasan Cewar duk abunda sukeyi a kan idonshi,
Dariya taso sub'uce mashi yayi saurin barin wurin, yanufi d'akinshi, yana fad'in idan kingama dariyar saiki kawo min abincina ina jiranki."
Yitayi kamar bata jishiba, tashiga bawa tsohuwa labari suna dariya."
Tsohuwa tace "tashi kije ki d'auki abincin yayanki ki kaimasa yana can yana jiranki."
Ta turo baki tace "ni tsohuwa bazanjeba saboda duka na zaiyi."
Tsohuwa tace "baxai dokeki ba aina riga nayi mashi magana, nace karya dakeki kuma kinsan mamuda yanada jin maganar mutane, Wurin nan yana burgeni."
Sannan ta tashi tana turo bki tanufi kicin ta d'auki abincin shi tanufi d'akinshi,
Kai tsaye tashiga d'akin batare da tayi sallama ba,
ta tarar dashi zaune a kan katifarshi dagashi sai best da gajeran wando, jikinshi ko ta ina gashi gashine yayi kwance akan kyakkyawar fatar jikinkinshi fara fes.
hankalinta ya tashi jikinta yasoma rawa aduniya bata tab'a ganin namiji a hakanba,
Tsawa ya doka mata wadda tasanyata tadawo natsuwarta yace "ubnwaye yabaki izinin kishigo min d'aki batare da kinyi sallama ba?"
Maxa kikoma kiyi sallama sannan ki kuma shigowa."
Da Sauri ta juya ta koma jikinta na rawa."
Yana ganin fitarta yayi saurin mik'ewa tsaye ya d'auko jallabiyarshi ya sanya."
Sallama tayi sannan ya amsa mata had'ida bata umurnin shigowa, sannan ta shigo,
Kallon yabita dashi yana harararta domin cike yake da jin haushinta, yanuna mata wni tebur yace "wuce ki ajiye a can."
Kizo inaso zanyi magana dake, kuma kika kuskura kika gudu ko kika yimin ihu saina k'arye maki hannu d'aya idan na rik'aki."
Sum sum ta wuce ta ajiye harda wani sunkuyar dakai kamar ta Allah, tazo kusa dashi ta durk'usa had'ida sunkuyar da kanta k'asa."
Ya Matso daf da ita ya kama kunnenta ya murd'a sosai saida tasaki fitsari saboda azaba,
Yace "maimaita abunda kikace d'azun.
Ni kikeyiwa Allah ya isa baki yafeba?"
Rantse rantse tashigayi ita batayi Allah ya isaba"don Allah kayi hakuri karka ciremin kunne, banyi maka Allah ya isaba."
"Idan kika kuskura aka kuma sake kawo k'ararki a gidan nan saina farfasa maki baki kinyarda."
Tayi saurin d'aga kanta alamar "eh." Idanta na zubar da hawaye."
Ganin fitsarin dake d'iga a zanenta yasa yayi saurin sakinta yaja da baya da sauri ya d'auko bulala yanufota yace "koki goge fitsarin nan ko yanzun na lahira yafiki jin dad'i."
Da Sauri ta mik'e tsaye, saiga takarda ta fad'o a zanenta, ya doka mata tsawa yace "ke zonan takardar meye?"
zaro ido tayi waje takai durk'ushe tana matsar hawaye tana fad'in dan Allah yaya kayi hak"uri bazan sakeba."
Tsawa ya Doka mata yace "ba kuka nace kiyi ba tambayarki nayi."
Cikin rawar murya tace "Anty bushira ce antyn suwaiba k'awata tace nakawo maka."
Ya wurga mata harara yace "bud'e karanta abunda ke ciki,
Da sauri ta bud'e takardar tashiga karanta masa, jin kalaman soyayya ne alamar tana sonshi, yayi saurin doka mata tsawa yace "rufe min bakinki kiyi min shuru,
Bari nafaracin k'aniyarki ke 'yar aiken kamun naje ga Wanda ta aikoki."
Ke fitsararriya marar kunya ke ake aikowa da takarda kikawo min?"
Tashi ki kama kunnanki."
Tana hawaye tana fad'in "Dan Allah yaya kayi hak'uri bazan sakeba."
Yasin sai kin kama kunnenki, yayo kanta da bulala a hannunshi,
Tana ganin hakan tayi saurin mik'ewa tsaye takama kunnenta sai kuka takeyi tana bashi hak'uri."
Abincinsa ya jawo ya fara ci, yana kammalawa ya haye katifarshi yajawo jarida ya Shiga karantawa, ganin ta wahala sosai ya dubeta yace "tashi kiwuce kiba mutane wuri."
Tayi kuka idanunta sunyi jajir har sunfara kumbura, ya dubeta yace "ko gobe idan wata ta kuma aikoki da takarda da sunan kikawo min kika karb'a abunda zanyi mki sai yafi wannan, sannan idan kika kuma yimun Allah ya isa saina karye mki k'afa d'aya da hannu d'aya."
Wuce kibani wuri kinyi tsaye kin kafeni da ido kina kallona saikace Aljanah."
Sum sum tafita tana kuka, a bakin k'ofar d'akinshi ta tsaya tace anfad'a d'in "Allah ya isa ban yafeba,
Lokacin da kake zuwa k'ofar gidansu zance na sani ne?" Dan kawai ta aikoni da takarda saika sanyani kamun kunne saboda mugunta,
to banyafeba wuta balbal kuma sai dai idan Kaine Aljanin baniba."
Ganinshi tayi ya nufota ta zuba a guje tayi cikin gida, karo taci da Kaka zaune a tsakar gida, yanajinta a zaure tana Allah ya isa, dama yana da takaicinta ya sanya sandar hannunshi yashiga zungurarta da ita, yana fad'in mamuda kikeyiwa Allah ya isa marar kunya.'
Kuka takeyi sosai Wanda yasa tsohuwa tayi saurin fitowa daga d'aki ta ceceta
Tana fad'in yanzun malam saboda Allah akan mamuda kake zungurar dijama da sanda, ai dole jidama tayi masa Allah ya isa saboda baya raga mata, baya tausayinta ko kad'an."
Ta rik'a hannun dijama tace tashi mutafi ko gobe mamuda ya kuma zaluntarki kice masa baki yafeba."
[28/04, 20:50] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_😅)
Writing
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)
*3*
Shiri takeyi zataje makarantar boko. Kasan cewar Wannan shine zangonta na k'arshe da zata k'are pramary school."
Ta kammala shirinta cikin riga da wando blue
ta sanya hijabinta fari, ta d'auko jakarta ta goya a bayanta,
ta dubi tsohuwa dake zaune gefe d'aya tana kallonta."
tace "ni dai tsohuwa nagama shiryawa zantafi."
Tsohuwa tace "to "dijamar tsohuwa Allah ya tsaremin ke kidawo lafiya,
Karki tsaya ko ina, kuma karki kula kowa a kan hanya kiyi tafiyarki dan karkiyi latti."
Tace "to tsohuwa, had'ida fitowa tasanya takalminta ta fita."
Saida ta kai k'ofar gida,
Sannan kuma ta juyo ta dawo a guje saka makon fitsarin da ya matseta,
Da sauri ta sunkuya ta d'auki buta a guje ta fad'a ban d'aki."
Wa zata gani yaya Mahmud ne,
ya juya bayansa yana wanka,
ihu ta kurma. Tana fad'in wayyo Allah k'ato ba wando,
Tafito a guje cikin tashin hankali da tsoro, had'ida sakin butar hannunta tazuba aguje."
Mahmud dajin ihunta yasanyashi Sanin shigowarta band'akin,
ransa yayi matuk'ar b'aci
Yashiga tunanin lallai wannan yarinyar bakad'an ta rainashiba tunda har take iya iskoshi band'aki." Tana kiranshi da k'ato ba wando."
Gudu take falfalawa kamar filfilwa,
bata zame a ko inaba sai makarantarsu,
Da shigarta makarantar ta cikin,
Taci karo da yara yan mkrtar tsugunne alamar latti sukayi,
Da gudu ta wucesu Batabi ta kansuba tayi shigewarta Aji."
Malam sani, mai hukunci yana ganinta ya rufa mata baya yana masifa,
kai tsaye ajinsu ya nufa,
ya tarar da ita zaune a kan kujerarta,
Kujerar da ba Wanda ya isa ya zauna akanta sai ita,
koda kuwa ranar da bataxo makaranta bane,
idan taji lbrin wani Wanda tsotsayi yasa shi ya zauna a kanta to sai tayi mashi shegen dukan tsiya."
Malam sani yashigo ajin a hasale, yadubeta
yace "ke dijama fito nan waje,
Wato kinyi latti saboda rashin kunya irin taki kika wani wuce mutane kika wuto aji,
Sai kace kinfi kowa to kisani hukuncinki ya k'aru dana sauran d'alibai."
Bata kulashiba sai ma tayi kamar bada ita yakeyiba,
Tsawa ya doka mata "ke dijama wai bada ke nake maganaba,?"
sai a lokacin ta dubeshi had'ida turo baki tana gunguni."
Cike da jin haushinta ya nufeta da bulala a hannunshi, bai tsaya b'ata lokaciba yashiga zuga mata bulalar."
Ihu ta kurma ta doka wani irin tsalle tashige mashi a babban Riga,
kasan Cewar malam sani ma'abucin sanya babban rigane.
Kokawa yashiga yi da ita yana k'ok'arin ya yakwace kansa daga gareta,
amma ina, idan yayi nan gefen ta dawo masa nan gefen, sai ihu takeyi kamar Wanda ake cirewa ido."
Malam sani ya jigata sosai zufa sai karye masa take, duk zufa ta wanke masa fuska,
ga dijama cikin babban rigarshi yakasa cireta, sai jujuwashi takeyi kamar zai fad'i k'asa."
Yashiga fad'in 'fito dijama nafasa dukan naki, kije kiyi zamanki,
amma ina ta cimuimuyeshi tana ihu tana fad'in
"wlh bazan fitoba."
Suna ganinta tayo kansu suka zuba a guje suna dariya harda rik'e ciki, suna fad'in wasa mukeyi
macijin roba ne."
Yahaya gaye da saida yayi nisa sosai da wurin sannan ya tsaya yana zarar ido yana maida numfashi sama sama, a can yajiyo sautin dariyarsu dijama suna fad'in wasa mukeyi macijin roba ne."
A hasale shima ya nufesu, cike dajin haushin muzantashi da sukayi a gaban budurwanshi, bugu da k'ari ga gudun da yayi harda tusa yasaki."
Aikuwa ya tunkarosu gadan gadan, dijama na ganin haka ta d'aga murya da k'arfi tace "kowa yayi ta kansa."
Suka zuba da gudu ko wannensu yanemi hanyar tsira."
Juyawar da zatayi ta gudu, taji tayi karo da mutum a dai dai lokacin da yahaya gaye yanufota, aikuwa ta mak'alk'ale mutumin wanda batasan kowaye shiba,
D'aga idon da zatayi sai taga Ashe yaya Mahmud ne."
Mari ya kwad'a mata, ya rik'a hannunta ya mik'awa yahaya gaye yace "gata kaci ubanta,
Domin ko mu kanmu mungaji da ita, mungaji da hali irin nata, kayi mata dukan tsiya ninace."
Yahaya gaye babu abunda yakeyi sai ruwan masifa,
Ladiyo ta matso kusa da ita ta xungure mata kai tace "kinci darajar yayanki da yau sai na lahira yafiki jin dad'i,
Dijama da sai zarar ido takeyi tana kallon fuskar yahaya gaye tanaso tayi dariya amma ba hali."
Mahmud yaja hannunta yana rankwashinta a kai yana mata fad'a, sai da sukazo k'ofar gida ta kwace hannunta da k'arfi tashige gida tana fad'in Allah ya isa mugu kawai."
Da Sauri yabita cikin gidan yana Neman ya rik'ata, aikuwa ta fad'a d'akin tsohuwa da gudu,
tsohuwa na ganinta tayi saurin tashi zaune tace "babu Wanda zaibiyoki sai mamuda domin nasan shi kad'ai ke k'ok'arin yaganki bakya motsi, hakan yayi dai dai da zuwanshi k'ofar d'akin yana huci, tsohuwa tace "karka kuskura ka shigo min d'aki
kaji na fad'a maka."
Yaja yayi tsaye a k'ofar d'aki yana huci,
Saida dijama ta kalli fuskarshi ta tuntsire da dariya harda rik'e ciki, dariya takeyi sosai, sai ta kuma kallonshi ta kuma tuntsirewa da dariya,
Ya kuma hasala, tana ganin ya hasala sosai tace "yaya kasan ko menakeyiwa dariya?"
Ya wurga mata harara had'ida girgiza kai."
Tace "ba komai yake bani dariya ba sai yahaya gaye, yanda yasaki tusa ya zuba a guje."
Shima kanshi gudun da yaga yahaya gaye nayi sai da yabashi dariya kasan Cewar duk abunda sukeyi a kan idonshi,
Dariya taso sub'uce mashi yayi saurin barin wurin, yanufi d'akinshi, yana fad'in idan kingama dariyar saiki kawo min abincina ina jiranki."
Yitayi kamar bata jishiba, tashiga bawa tsohuwa labari suna dariya."
Tsohuwa tace "tashi kije ki d'auki abincin yayanki ki kaimasa yana can yana jiranki."
Ta turo baki tace "ni tsohuwa bazanjeba saboda duka na zaiyi."
Tsohuwa tace "baxai dokeki ba aina riga nayi mashi magana, nace karya dakeki kuma kinsan mamuda yanada jin maganar mutane, Wurin nan yana burgeni."
Sannan ta tashi tana turo bki tanufi kicin ta d'auki abincin shi tanufi d'akinshi,
Kai tsaye tashiga d'akin batare da tayi sallama ba,
ta tarar dashi zaune a kan katifarshi dagashi sai best da gajeran wando, jikinshi ko ta ina gashi gashine yayi kwance akan kyakkyawar fatar jikinkinshi fara fes.
hankalinta ya tashi jikinta yasoma rawa aduniya bata tab'a ganin namiji a hakanba,
Tsawa ya doka mata wadda tasanyata tadawo natsuwarta yace "ubnwaye yabaki izinin kishigo min d'aki batare da kinyi sallama ba?"
Maxa kikoma kiyi sallama sannan ki kuma shigowa."
Da Sauri ta juya ta koma jikinta na rawa."
Yana ganin fitarta yayi saurin mik'ewa tsaye ya d'auko jallabiyarshi ya sanya."
Sallama tayi sannan ya amsa mata had'ida bata umurnin shigowa, sannan ta shigo,
Kallon yabita dashi yana harararta domin cike yake da jin haushinta, yanuna mata wni tebur yace "wuce ki ajiye a can."
Kizo inaso zanyi magana dake, kuma kika kuskura kika gudu ko kika yimin ihu saina k'arye maki hannu d'aya idan na rik'aki."
Sum sum ta wuce ta ajiye harda wani sunkuyar dakai kamar ta Allah, tazo kusa dashi ta durk'usa had'ida sunkuyar da kanta k'asa."
Ya Matso daf da ita ya kama kunnenta ya murd'a sosai saida tasaki fitsari saboda azaba,
Yace "maimaita abunda kikace d'azun.
Ni kikeyiwa Allah ya isa baki yafeba?"
Rantse rantse tashigayi ita batayi Allah ya isaba"don Allah kayi hakuri karka ciremin kunne, banyi maka Allah ya isaba."
"Idan kika kuskura aka kuma sake kawo k'ararki a gidan nan saina farfasa maki baki kinyarda."
Tayi saurin d'aga kanta alamar "eh." Idanta na zubar da hawaye."
Ganin fitsarin dake d'iga a zanenta yasa yayi saurin sakinta yaja da baya da sauri ya d'auko bulala yanufota yace "koki goge fitsarin nan ko yanzun na lahira yafiki jin dad'i."
Da Sauri ta mik'e tsaye, saiga takarda ta fad'o a zanenta, ya doka mata tsawa yace "ke zonan takardar meye?"
zaro ido tayi waje takai durk'ushe tana matsar hawaye tana fad'in dan Allah yaya kayi hak"uri bazan sakeba."
Tsawa ya Doka mata yace "ba kuka nace kiyi ba tambayarki nayi."
Cikin rawar murya tace "Anty bushira ce antyn suwaiba k'awata tace nakawo maka."
Ya wurga mata harara yace "bud'e karanta abunda ke ciki,
Da sauri ta bud'e takardar tashiga karanta masa, jin kalaman soyayya ne alamar tana sonshi, yayi saurin doka mata tsawa yace "rufe min bakinki kiyi min shuru,
Bari nafaracin k'aniyarki ke 'yar aiken kamun naje ga Wanda ta aikoki."
Ke fitsararriya marar kunya ke ake aikowa da takarda kikawo min?"
Tashi ki kama kunnanki."
Tana hawaye tana fad'in "Dan Allah yaya kayi hak'uri bazan sakeba."
Yasin sai kin kama kunnenki, yayo kanta da bulala a hannunshi,
Tana ganin hakan tayi saurin mik'ewa tsaye takama kunnenta sai kuka takeyi tana bashi hak'uri."
Abincinsa ya jawo ya fara ci, yana kammalawa ya haye katifarshi yajawo jarida ya Shiga karantawa, ganin ta wahala sosai ya dubeta yace "tashi kiwuce kiba mutane wuri."
Tayi kuka idanunta sunyi jajir har sunfara kumbura, ya dubeta yace "ko gobe idan wata ta kuma aikoki da takarda da sunan kikawo min kika karb'a abunda zanyi mki sai yafi wannan, sannan idan kika kuma yimun Allah ya isa saina karye mki k'afa d'aya da hannu d'aya."
Wuce kibani wuri kinyi tsaye kin kafeni da ido kina kallona saikace Aljanah."
Sum sum tafita tana kuka, a bakin k'ofar d'akinshi ta tsaya tace anfad'a d'in "Allah ya isa ban yafeba,
Lokacin da kake zuwa k'ofar gidansu zance na sani ne?" Dan kawai ta aikoni da takarda saika sanyani kamun kunne saboda mugunta,
to banyafeba wuta balbal kuma sai dai idan Kaine Aljanin baniba."
Ganinshi tayi ya nufota ta zuba a guje tayi cikin gida, karo taci da Kaka zaune a tsakar gida, yanajinta a zaure tana Allah ya isa, dama yana da takaicinta ya sanya sandar hannunshi yashiga zungurarta da ita, yana fad'in mamuda kikeyiwa Allah ya isa marar kunya.'
Kuka takeyi sosai Wanda yasa tsohuwa tayi saurin fitowa daga d'aki ta ceceta
Tana fad'in yanzun malam saboda Allah akan mamuda kake zungurar dijama da sanda, ai dole jidama tayi masa Allah ya isa saboda baya raga mata, baya tausayinta ko kad'an."
Ta rik'a hannun dijama tace tashi mutafi ko gobe mamuda ya kuma zaluntarki kice masa baki yafeba."
[28/04, 20:50] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹
( _'Yar gidan tsohuwa_😅)
Writing
By
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)
*3*
Shiri takeyi zataje makarantar boko. Kasan cewar Wannan shine zangonta na k'arshe da zata k'are pramary school."
Ta kammala shirinta cikin riga da wando blue
ta sanya hijabinta fari, ta d'auko jakarta ta goya a bayanta,
ta dubi tsohuwa dake zaune gefe d'aya tana kallonta."
tace "ni dai tsohuwa nagama shiryawa zantafi."
Tsohuwa tace "to "dijamar tsohuwa Allah ya tsaremin ke kidawo lafiya,
Karki tsaya ko ina, kuma karki kula kowa a kan hanya kiyi tafiyarki dan karkiyi latti."
Tace "to tsohuwa, had'ida fitowa tasanya takalminta ta fita."
Saida ta kai k'ofar gida,
Sannan kuma ta juyo ta dawo a guje saka makon fitsarin da ya matseta,
Da sauri ta sunkuya ta d'auki buta a guje ta fad'a ban d'aki."
Wa zata gani yaya Mahmud ne,
ya juya bayansa yana wanka,
ihu ta kurma. Tana fad'in wayyo Allah k'ato ba wando,
Tafito a guje cikin tashin hankali da tsoro, had'ida sakin butar hannunta tazuba aguje."
Mahmud dajin ihunta yasanyashi Sanin shigowarta band'akin,
ransa yayi matuk'ar b'aci
Yashiga tunanin lallai wannan yarinyar bakad'an ta rainashiba tunda har take iya iskoshi band'aki." Tana kiranshi da k'ato ba wando."
Gudu take falfalawa kamar filfilwa,
bata zame a ko inaba sai makarantarsu,
Da shigarta makarantar ta cikin,
Taci karo da yara yan mkrtar tsugunne alamar latti sukayi,
Da gudu ta wucesu Batabi ta kansuba tayi shigewarta Aji."
Malam sani, mai hukunci yana ganinta ya rufa mata baya yana masifa,
kai tsaye ajinsu ya nufa,
ya tarar da ita zaune a kan kujerarta,
Kujerar da ba Wanda ya isa ya zauna akanta sai ita,
koda kuwa ranar da bataxo makaranta bane,
idan taji lbrin wani Wanda tsotsayi yasa shi ya zauna a kanta to sai tayi mashi shegen dukan tsiya."
Malam sani yashigo ajin a hasale, yadubeta
yace "ke dijama fito nan waje,
Wato kinyi latti saboda rashin kunya irin taki kika wani wuce mutane kika wuto aji,
Sai kace kinfi kowa to kisani hukuncinki ya k'aru dana sauran d'alibai."
Bata kulashiba sai ma tayi kamar bada ita yakeyiba,
Tsawa ya doka mata "ke dijama wai bada ke nake maganaba,?"
sai a lokacin ta dubeshi had'ida turo baki tana gunguni."
Cike da jin haushinta ya nufeta da bulala a hannunshi, bai tsaya b'ata lokaciba yashiga zuga mata bulalar."
Ihu ta kurma ta doka wani irin tsalle tashige mashi a babban Riga,
kasan Cewar malam sani ma'abucin sanya babban rigane.
Kokawa yashiga yi da ita yana k'ok'arin ya yakwace kansa daga gareta,
amma ina, idan yayi nan gefen ta dawo masa nan gefen, sai ihu takeyi kamar Wanda ake cirewa ido."
Malam sani ya jigata sosai zufa sai karye masa take, duk zufa ta wanke masa fuska,
ga dijama cikin babban rigarshi yakasa cireta, sai jujuwashi takeyi kamar zai fad'i k'asa."
Yashiga fad'in 'fito dijama nafasa dukan naki, kije kiyi zamanki,
amma ina ta cimuimuyeshi tana ihu tana fad'in
"wlh bazan fitoba."