← Book details Nahuce Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 5 OF 14

Sashe 5

Nahuce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da gaske yasa kaimi ya aureta ne don biyan bukatar ruhin sa da gangar jikin sa, bai taba fadawa a wani abu wai soyayya ba, kallon ta yake da jin ta as waste of time, burin sa da lokutansa na tunanin maida kobo ya koma dari ne, yana da manyan burika da suka zarce soyayya.

In fact, bai dauki mace a bakin komai ba banda abar hutawar gangar jikin mijin auren ta.

Amma ita wannan inda bata bullo masa ta haka ba, da bata nuna ta san ba son ta yake ba, bayan target dinsa na auren ta yanada burin tallafar rayuwar ta da maraicin ta, tare da cigaba da zama da ita har karshen rayuwar sa.

Amma tunda ta nan ta bullo, ya san ta yadda zai yi maganin ta.

Daga sanda ya mike ya durfafe ta, da sanda ta soma ja da baya cikin tsoro, cikin abinda bai gaza sakan bane idanuwan su suka hadu, ta hango wani boyayyen al'amari cikin brown kwayan idanun sa, al'amarin da har gobe ta kasa mantawa, shekaru bakwai kenan; Babu soyayya a cikin a cikin kwayar idon Habibu ko kankani face lustfuldesire wanda ya kara darsa mata tsanar sa.

Ta kuma kara yarda da cewa manufarsa kenan ta auren ta.

Da farko yayi kokarin lallashin ta, amma sai ya gane zai bata lokacin sa ne kawai, ga rashin kunya da tsiwa kala-kala na fita nau'i-nau'i daga bakin ta, sai ya ce "Raheenah bari in yi maganin ki.....".

Duk wani kokari na kwatar kai da neman ceto Raheenah Omar ta yi, kafin ta gane all her effort was futile (kokarin ta na banza ne), tamkar Habib Nahuche ya jima yana jiran wannan ranar, ya gama shirya mata.

Abubuwanda suka wakana a tsayin daren bakidayan sa ba masu dadin fada bane.

Saboda al'amarin baida maraba da rape banda igiyar aure data suturta shi.

Kuma wannan ne abinda ya gina matsanancin tsoro da kiyayyar sa a zuciyar ta.

She hates him with passion from their first night.

Ta alkawartawa ranta koda jan ciki sai ta bar Jamus, gara ta dawo Adamawa ko bara ce ta yi ta ci da kanta, da dai ta zauna da wannan mugun mutumin mai halin dabbobi.

Tamkar ya san tunanin ta, washegari da zai fita makaranta saida ya kulle ta ta waje.
*****
Ba shi ya dawo ba sai yamma lis, tunda ya san ya bar mata komai da zata bukata.

Amma ga mamakin sa a inda ya fita ya barta anan ya dawo ya sameta, a kwance akan marbles kamar kayan wanki, baya tunanin ko sallah ta tashi ta yi, balle akai ga wanka.

"And your name is bride?"
Ya tambayeta cikin zolaya.

Hararar data ke masa tamkar idanunta zasu fado, wadanda suka kada suka yi jajazur kamar an gumbuda musu barkono.

Da za'a bata dama zata iya kashe shi ta hanyar rataya, sabida tsanar data yi masa.

Ya tsugunna a gabanta ya ajiye mata ledar abincin McDonalds da lemun power horse mai sanyi, yana wani makalallen murmushi na tura haushi yace "ki ci ki sha, ko kya wartsake kinji amarya ta!

We're going for the second phase.,.... what is the marriage meant for?

I don't believe in what is called love.

Ban sani ba ko in kika haifa min 'ya'ya.....

""ta Allah ba taka ba..kada Allah ya nuna min wannan ranar""ko?" Ya tambaya yana kara hade filin dake tsakanin su...... kuma wannan karon ma kokarin ta da bijirewar ta, bai kwace ta da komai ba.

"You goddam lunatic!

I hate you.....kuma insha Allahu sai Allah ya saka mini, ta hanyar da baka taba zato ba.

Abinda kayimin sai an wa 'yar ka, in baka haifa ba kanwar ka, in baka da ita UWARKA!"
Bai san sanda ya daga hannu ya zabga mata mari ba, marin da Raheenah ta tabbatar taga wuta a cikin sa.

Kafin ya kama hannun ya rike cikin nadama!

Wai shine da dukan mace.....macen ma mai amsa sunan matar sa.

Amma abu na karshe da bazai iya dauka ba shine raini, don abinda take gani a matsayin babban laifi daga gare shi shi ko kusa bai kalle shi hakan ba.

A tunanin sa ana aure ne for sex only, kamar yadda ake cin abinci kullum.

Baya jin a duniya zai so wata mace bayan mahaifiyar sa.

Kuma baya comparing din ta da sauran mata.

Talkless of Rahinah ta ambace ta ta zaga.

"Duk rainin ki ya tsaya a tsakanin ni da ke, kada ki sake ki hada da uwata".

Ya fada yana sake rugumota jikin sa ba tareda tausayi ba ya sake maimaita laifinsa, har da cewa "ai sadaki na biya, ki jawomin ayar da tayi umarni da soyayya, aure Ubangiji yayi umarni mu yi ba soyayya ba".

This man is unbelievable ga tunanin Raheenah bata san a rukunin mutanen da zata sanya shi ba, gashi dan boko mai matakin master, amma jakancin sa akan diya mace ko gardin kauye bazai yi ba.

She hates him again and again for his wickedness.

Tunanin ta gabadaya ya koma kan how to escape from this abusive marriage.

Amma har kwanaki suka nausa zuwa biyar, bata samu wannan damar ba.

Yayin da Habib ya dukufa ga morar sadakin sa, don bai taba tunanin abinda yake yi din ba daidai bane, ko zata iya tafiya ta barshi tunda bata da kowa.
(Akwai maza da yawa irin Habibu Nahuche, wadanda baza'a ce rashin ilmi ya hana su son matan su ba, ko kasancewa masu nuna soyayya da tarairaya koda fake ce.

Suna aure ne for their own pleasure.

Ita mace kuwa 'yar son lallashi ce da soyayya kuma har abada in baka iya tafiyar da ita ba, hankalin ta bazai taba nutsuwa da kai ba.

Ita Rahinatu ma kallon Habibu take as rapist don bata yarda miji zai iya yiwa matar sa izayar da yake yi mata ba).

A duka kwanakin nan bata ci bata sha, sai taji hanjin cikin ta na neman tsinkewa ne take shan ruwan bunu ko ta sha madarar kwali, wanka kuwa rabon ta dashi har ta manta, watakila in yaji tana tsami, a yadda yake dan gayun nan mai son wanka da kamshi zai daina rabar ta.

Amma gogan nata ko a jikin sa, wani sabon abu ma ya tsiro da shi; fesa mata turaren sa 'Carolina Herrera' a duk sanda zai kusance ta, tana kuka tana tsine masa, amman kaman tana kara zuga shi.

Tsahon kwanaki shida ya tabbatar shi kansa ya samu lafiya daga masifar dake damun shi akan Raheenah, zamu iya cewa kanwa ce ta kar tsami kwannafi ya kwanta.

Ya soma jin tausayin ta, kuma ya rage takura mata.
*****
RANAR KWANA BAKWAI
anar da auren su ya cika kwana bakwai ne komai ya faru, haduwar da rabuwar masu kama da blink of an eye (kiftawar ido).

Gabadaya haduwar sa da saninsa da Raheenah Omar, zuwa auren su da zaman auren watanni uku ne cif har kwanaki bakwai na aure data yi a gidan sa.

A safiyar ranar tun asubah ta faki idon sa ta dauke masa mukullai, neman duniya yayi musu bai gan su ba, kuma baya so ta gane abinda yake nema kenan, don haka yaja bakin sa yayi shiru, kada ta gane bai rufeta ba tayi tunanin guduwa, shi kuma daga ranar ya fara nadama, ya kuma alkawartawa ransa bazai kara kusantar ta ba sai bisa amincewar ta.

Sannan zai yi kokari ya koma yadda duk take son sa, wato namiji dan soyayya, mara gaggawa, loving, caring, romantic.

Mai bin komai a sannu.

Sex will be his last priority a rayuwar auren su.

In ta kama zai je makaranta ya shiga aji ya zauna a koya masa yadda zai koyi zama da mata ne zai yi hakan, sakamakon wani irin pleasant feeling (so na hakika) tamkar maganadisu mai jan zuciya da ruhi da ya ji yana shigarsa a hankali akan RAHINAH OMAR daga daren jiya zuwa wayewar garin yau.

Wayewar garin data cika kwanaki bakwai da auren su.

Bata taba yarda sun kwana gado daya ba, in suka gama damben su yayi galaba akanta anan kasan marbles da ya barta bata canza matsugunni, sai in ya fita ne taji yunwa zata kasheta take yunkurawa ta isa ga firji ta sha madara ta koma ta kwanta.

Haka zata wuni kuka idan ta tuno karatun ta, da abokan karatun ta da Dadar ta.

Yau ta dauke masa mukullai ne da niyyar zata gudu, kuma zata bar Jamus gabadaya.

Bai nuna mata bai ga mukulli ba, tana daga kwance inda take ya sunkuya ya ajiye mata kofin tea.

Sai tiriri yake.

Ta runtse ido hawaye na bulbula domin ko fuskarsa bata son gani.

Kamshin turarensa duk ya mamaye ta.

"Kiyi hakuri sweetie, i promised to become a changed person, if you give me another chance (nayi alkawarin canzawa, in har zaki bani dama).

Yanzu dai na makara, inna dawo zamu tattauna sosai".

"Allah yasa kafin ka dawo ka tadda gawata!"
Ta fada cikin rishin kuka.

Tana mai addu'ar Allah ya dauki ranta ta huta kafin Habibu ya dawo
Murmushi Habib yayi, sannan ya sunkuya ya sumbaci bakin ta lightly.

Wani abu da bai taba wanzuwa tsakanin su ba (sumba).

Ta tattaro miyau ta tofa masa a fuska.

Maimakon ta ga ransa ya baci ko ya falleta da mari kamar yadda ya saba, sai taga yasa dan yatsa ya lakato miyan ya kai bakin sa ya lashe.

Ya kuma kasheta da murmushi yace "i know that i offend you, and it's intentional as you expect, but i promised to become new HABEEB (masoyi) har sai kin koreni sabida soyayya.

Ki bani thirty minutes yanzu zan dawo we will discuss everything, in nace EVERYTHING ina nufin har ASALI NA da naki".

Maimakon maganganun sa su farantawa Raheena, sai ma suka kara shafa masa shuni a idanun ta.

Ba abinda zai ce ta yarda yana kaunar ta.

Ya baro gini tun ran zane....zuciyar ta ta riga ta mace a tsanar sa.

Abinda kuma zai farfado da matacciyar zuciyar nan ba kankani bane.

Ya riga ya raunata zuciyar ya yi mata illah.

Tsanar data yi masa ba 'yar kadan bace.

Kuma zata nuna masa ita ba yar tsana bace duk rashin gatanta ta san 'yancin kanta.
Chapter 5 · 0% Book details