Sashe 15
Me Ya Jamin New Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Zama sukayi da kansa ya rinƙa bata abincin a baki tun daga wannan rana ya zame mata al'ada duk dare basa bacci kwana yakeyi akanta sai safiya tayi suke samun nutsuwa tsayin wata guda sai kuma laulayi ya sawo kai kullum tana kwance kamar ruwa tun ga amai da take fama dashi babban abinda ya fara bata mamaki da tsoratata a yanayin zaman gdan nasu idan yana gda Salma zata nuna mata tafi kowa kulawa da ita idan bayanan kuwa ko leƙota batayi haka suke rayuwa sannu a hankali lkc ya rinƙa tafiya cikin yanada watanni hudu cikin wani dare da bata mantawa dashi ranar ba ita keda girki ba Salma ce tun yamma takejin yanayin zazzaɓi ajikinta haka ta gama abinda takeyi a daddafe ta kwanta bacci ya ɗauketa cikin baccin taji wani mugun huci yana tunkarota ta buɗe idonta da sauri tare da dirowa a gadon daidai lkcn da wata doguwar halitta ta ƙaraso gabanta batayi aune ba taji an feso mata wani abu me azabar raɗaɗi a jikinta azabar data ratsa ta itace tasata sakin wata gigitacciyar ƙara ta zube a gurin kasancewar dakin a kulle yake Tsakanin ɗakinta dana Aliyu akwai tazara baijita ba amma Salma taji ta basar hakanan tayita juyi tana murƙususun azaba ta daɗe sannan ta samu raɗaɗin ya ragu tana addu'a sannan ta buɗe idanunta taga wannan mutumin ya ɓace taja ajiyar zuciya tanabin jikinta da kallo.
Me zata gani wasu irin ƙananun ƙuraje ne gabaɗaya jikinta sai zubar da ruwa sukeyi aikuwa ta mike a razani tana ƙara bin jikin da kallo tana faɗin “Innanillahi wa Innah Ilaihirraji'un" tsoro ya sake kamata ta tsigar jikinta tana tashi wasu zafafan hawaye suka zubo mata cikin tashin hankalin da bata taɓa shigaba tace “Na shiga uku Ni Kharimatu wannan wacce irin masifa ce?" Ashe wasa farin girki ne cikin lkc ƙanƙani taji kanta da jijiyoyin jikinta sun ɗaure ɗam ta kasa ko matsa komanta kafin kace meye wannan ta yanke jiki ta faɗi.
Bata farka ba sai a gadon asibiti tana buɗe idonta jikinta ta fara kallo ta rintse idonta cikin ƙyanƙyami da tashin hankali ta rushe da wani kuka me gunji tace Innanillahi Granny meye wannan a jikina" Granny da Mom da suke zaune a gefe suka nufota da sauri cikin tsananin tausayi Granny tace “Sannu Kharimatu ke kuma taki ƙaddarar kenan daga wannan sai wannan Ni waɗannan ƙuraje don dai sun dage akan ayi maganin asibiti ne nikam nafi tunanin sihiri ne" Mom ce ta cafe da cewa ashe muna ɗaya dake lamarin yarinyar nan akwai alamun bincike Hajiya iyakar zamanmu da ita batada jinnu kina gani fah dagayin aurennnan abu yaƙi daɗi kullum ita kenan ta yanke jiki ta faɗi yanzu kuma ga wata sabuwar masifar ta sako kai kiga fa jikinta yanda ƙurajen nan suka girma fata me kyau ta zama kamar bayan bishiya sai daddarewa takeyi"
Jinjina kai Granny tayi tace “Ma'aruf ne yake biyewa yaron nan Ni dama Muniba tun farko banso zaman Kharimatu da Salma guri ɗaya ba nasan sai an cutar da yarinyar nan" karɓa Mom tayi da cewa “ai gashinan sun fara gani Hajiya dole idan yarinyar nan ta samu sauƙi ya raba musu gda ko kuma ya sawwaƙe mata tunda zamansu taren ba dole bane" akan wannan shawarar suka tsaya.
Tun ranar data farka a asibitin take sanya idon ganin Aliyu shiru babu shi babu labarinsa har yau gashi kwana uku da farkawarta abinda yake bata mamaki ko a waya bataji yana kiran Granny ba yau tun safe ta tashi jikinta sai ruwan mugunya yake zubarwa abinda ya tashi hankalin kowa babu shiri Granny ta Kira Aliyu ta sanar dashi abin mamaki sai cewa yayi da ita shifa ayi duk abinda ya dace Bama ya gari yana Lagos zai turo musu da kuɗi" jinjina kai Granny tayi tace “Anya Aliyu yau yarinyar nan watanta guda a asibitin nan tun washegarin ranar da aka kawota baka ƙara dawowa ba matarka ma batazo ba meye yake faruwa ne haka?"
A kausashe yace “Itama batanan muna tare anan yaran suna gdansu Salma daganan Dubai ma zamu wucce Salma keda ciki zataje ta huta acan maybe sai yakai 6 months zamu dawo" murmushi Granny tayi tace “Lallai ne Gadanga kabar yarinya marainiyar Allah cikin lalura ka ɗauki matarka kunbar gari kuma har kana sanar da cewa zaku wucce Dubai to ita ame kabarta da nata cikin?"
Tsaki yayi yace “Ke wlh Granny da son takurawa kike naga gashinan kuna kula da ita" bazata iya jure lamarin ba wannan tasa ta kashe wayarta takai dubanta ga Kharimatu da takejin duk abinda yake faruwa tace “Inason ganinsa Granny kice yazo don Allah" hawayen tausayinta Granny ta share tace “zaizo Kharimatu wani aikine na gaggawa ya taso masa ya tafi Lagos amma kina ransa kiyi hƙr kinji kiyi fatan Allah ya baki lfyrki kawai"
Komawa tayi ta kwanta tana share hawaye kewar mahaifiyarta tana sake bijirowa zuciyarta sosai tayi kuka Granny nata aikin rarrashinta cikin kukan tace “Ba damuwata yazo ba Granny damuwata shine son sanin yanda ya karɓi amanar da Mahaifiyata ta bar masa, meyesa ta amince na zauna da Aliyu tun kafin na amince dashi? Meyesa ta zaɓamin shi tace naje na zauna dashi harma take bani wasiyyar na zauna dashi iyakar wuya bayan shi tun yanzu ya fara juyamin baya Granny tunda na farka kwana uku kenan banga Daddyn Farooq ba kuma yanzu naji kina faɗa cewar tunda aka kawoni asibitin nan washegari bai ƙara zuwa ba"
Sharce gumi Granny tayi ta kamo hannun Kharimatu da taketa zubar da hawaye tace “kinga Kharimatu inason ki cire komai a ranki don Allah ki manta da komai kinga cikinki ya tsufa watanni bakwai bakya buƙatar hayaniya ga kuma lalurar nan da take damunki don Allah ki daina sa Aliyu a ranki Kharimatu ba haka akabar Aliyu ba kinsani wannan lamari yana buƙatar addu'a me tsanani"
Jan zuciya tayi tace “Yanzu a haka zanta zama kenan?" Murmushi Granny tayi tace “Aa bazakiyita zama a haka ba yanzu abinma dake akwai zaki koma gabanmu ne aci aci gaba da magani har Allah ya baki lfyrki"
Zuciyarta na suya haka ta hƙr tabar mgnr ta koma ta kwanta kwana takwas ta ƙara a asibitin suka sallameta domin suma sun fahimci ciwon nata bana asibiti bane dole tasa aka nemi maganin Hausa tare da yin waya Guru aka sanar dasu halin da ake ciki Baba Na'ibi wane a gurin babanta shine ya niƙo gari ya taho Kano ya kawo mata magani cikin ikon Allah Suna fara amfani da maganin sauƙi yayita samuwa sati guda bata rufa ba wannan ƙanzo²n da fatarta tayi duk ya ɓare asalin fatarta ta dawo Baba Na'ibi yana kallonta yayi murmushi yace “komai zai wucce da yardar Allah"
*Oum Hairan*
[11/10, 8:59 PM] Oum Hairan&Affan: *MYJ39-40 Oum Hairan* Littafina na kuɗi kada ki karanta min baki biya ba don Allah idan kinaso ki biya ta 0255526235 Gtbank ko ki turo hoton katin 300 ta wannan number 09013718241 saiki tura evidance of payment ta number dai ko VTU ta 0931307566
Kwanaki har watanni sukayita wuccewa babu Aliyu babu Salma Kharimatu tanata rainon cikinta har ya isa haihuwa ranar wata asabar da yamma ta shiga bayi tana tsugunnawa taga wani jini me yauƙi ya zubo mata ta miƙe da sauri ta fita ta kira Granny dake a sashinta take zaune. Tana gani ta gane meye ke faruwa tayi murmushi tace “Abin yazo Kharimatu haihuwa ce" gabanta ya faɗi tace “Granny tun jiya marata take ciwo fah" kama hannunta tayi tace “kije ki zauna bari nayiwa Mal Hassan mgn yayi miki rubutu idan haihuwar ce ciwon zai tashi ayi a wucce gurin idan ba ita bace kuma zaiyi sauƙi"
Zaunar da ita tayi ta shiga ɗaki bata jima ba ta fito ta tarar da ita ta riƙe ciki ta cije leɓe tana ƙoƙarin zamewa daga kujerar kamota tayi ta saukar da ita ƙasa tanayi mata sannu itadai kallonta kawai takeyi tana karɓar azaba babu jimawa Mal Hassan ya aiko da rubutun Granny ta bata tasha tace ta kwanta, kwanciya tayi bacci ya ɗauketa cikin baccin taji azabar ciwon ta ƙaru ta zabura ta miƙe da sauri tana faɗin Innanillahi wa Innah Ilaihirraji'un Granny bayana marata ƙirjina wayyoh wayyoh Granny shikenan na mutu na ƙare...." Rufe mata baki tayi tace “ke ar sakarya ki rinƙa salati" fita Granny tayi tayima driven gdan mgn tazo ta ɗauko mata hijjab ɗinta tasa mata daidai lkcn Mom ta fito itama suka nufi asibiti suna zuwa aka shiga da ita labour room.
Bata wani ɓata lkc ba Ubangiji ya yassare mata ta haifo sankacecen ɗanta namiji kyakkyawa kamannin sa na mahaifinsa ne sak sumarsa da bakinsa sune kawai nata, ana gyara yaron aka sallamesu suka tafi gda sunata murna kamar ba'a taɓayi musu haihuwa ba.
Waya sukayi Guru ƙanwar Mama Yabi tazo ita da Granny suka rinƙa kula da ita abinda ya dami zuciyarta tun ranar data haihu take kiran wayar Aliyu bata shiga shikuma bai kirata ba zuciyarta na faɗa mata to ko baisan ta haihu bane?" Wannan abu sosai ya damu ranta ranar da ɗanta ya kwana biyar suna zaune take tambayar Granny Daddyn Farooq kuwa yasan ta haihu?"
Me zata gani wasu irin ƙananun ƙuraje ne gabaɗaya jikinta sai zubar da ruwa sukeyi aikuwa ta mike a razani tana ƙara bin jikin da kallo tana faɗin “Innanillahi wa Innah Ilaihirraji'un" tsoro ya sake kamata ta tsigar jikinta tana tashi wasu zafafan hawaye suka zubo mata cikin tashin hankalin da bata taɓa shigaba tace “Na shiga uku Ni Kharimatu wannan wacce irin masifa ce?" Ashe wasa farin girki ne cikin lkc ƙanƙani taji kanta da jijiyoyin jikinta sun ɗaure ɗam ta kasa ko matsa komanta kafin kace meye wannan ta yanke jiki ta faɗi.
Bata farka ba sai a gadon asibiti tana buɗe idonta jikinta ta fara kallo ta rintse idonta cikin ƙyanƙyami da tashin hankali ta rushe da wani kuka me gunji tace Innanillahi Granny meye wannan a jikina" Granny da Mom da suke zaune a gefe suka nufota da sauri cikin tsananin tausayi Granny tace “Sannu Kharimatu ke kuma taki ƙaddarar kenan daga wannan sai wannan Ni waɗannan ƙuraje don dai sun dage akan ayi maganin asibiti ne nikam nafi tunanin sihiri ne" Mom ce ta cafe da cewa ashe muna ɗaya dake lamarin yarinyar nan akwai alamun bincike Hajiya iyakar zamanmu da ita batada jinnu kina gani fah dagayin aurennnan abu yaƙi daɗi kullum ita kenan ta yanke jiki ta faɗi yanzu kuma ga wata sabuwar masifar ta sako kai kiga fa jikinta yanda ƙurajen nan suka girma fata me kyau ta zama kamar bayan bishiya sai daddarewa takeyi"
Jinjina kai Granny tayi tace “Ma'aruf ne yake biyewa yaron nan Ni dama Muniba tun farko banso zaman Kharimatu da Salma guri ɗaya ba nasan sai an cutar da yarinyar nan" karɓa Mom tayi da cewa “ai gashinan sun fara gani Hajiya dole idan yarinyar nan ta samu sauƙi ya raba musu gda ko kuma ya sawwaƙe mata tunda zamansu taren ba dole bane" akan wannan shawarar suka tsaya.
Tun ranar data farka a asibitin take sanya idon ganin Aliyu shiru babu shi babu labarinsa har yau gashi kwana uku da farkawarta abinda yake bata mamaki ko a waya bataji yana kiran Granny ba yau tun safe ta tashi jikinta sai ruwan mugunya yake zubarwa abinda ya tashi hankalin kowa babu shiri Granny ta Kira Aliyu ta sanar dashi abin mamaki sai cewa yayi da ita shifa ayi duk abinda ya dace Bama ya gari yana Lagos zai turo musu da kuɗi" jinjina kai Granny tayi tace “Anya Aliyu yau yarinyar nan watanta guda a asibitin nan tun washegarin ranar da aka kawota baka ƙara dawowa ba matarka ma batazo ba meye yake faruwa ne haka?"
A kausashe yace “Itama batanan muna tare anan yaran suna gdansu Salma daganan Dubai ma zamu wucce Salma keda ciki zataje ta huta acan maybe sai yakai 6 months zamu dawo" murmushi Granny tayi tace “Lallai ne Gadanga kabar yarinya marainiyar Allah cikin lalura ka ɗauki matarka kunbar gari kuma har kana sanar da cewa zaku wucce Dubai to ita ame kabarta da nata cikin?"
Tsaki yayi yace “Ke wlh Granny da son takurawa kike naga gashinan kuna kula da ita" bazata iya jure lamarin ba wannan tasa ta kashe wayarta takai dubanta ga Kharimatu da takejin duk abinda yake faruwa tace “Inason ganinsa Granny kice yazo don Allah" hawayen tausayinta Granny ta share tace “zaizo Kharimatu wani aikine na gaggawa ya taso masa ya tafi Lagos amma kina ransa kiyi hƙr kinji kiyi fatan Allah ya baki lfyrki kawai"
Komawa tayi ta kwanta tana share hawaye kewar mahaifiyarta tana sake bijirowa zuciyarta sosai tayi kuka Granny nata aikin rarrashinta cikin kukan tace “Ba damuwata yazo ba Granny damuwata shine son sanin yanda ya karɓi amanar da Mahaifiyata ta bar masa, meyesa ta amince na zauna da Aliyu tun kafin na amince dashi? Meyesa ta zaɓamin shi tace naje na zauna dashi harma take bani wasiyyar na zauna dashi iyakar wuya bayan shi tun yanzu ya fara juyamin baya Granny tunda na farka kwana uku kenan banga Daddyn Farooq ba kuma yanzu naji kina faɗa cewar tunda aka kawoni asibitin nan washegari bai ƙara zuwa ba"
Sharce gumi Granny tayi ta kamo hannun Kharimatu da taketa zubar da hawaye tace “kinga Kharimatu inason ki cire komai a ranki don Allah ki manta da komai kinga cikinki ya tsufa watanni bakwai bakya buƙatar hayaniya ga kuma lalurar nan da take damunki don Allah ki daina sa Aliyu a ranki Kharimatu ba haka akabar Aliyu ba kinsani wannan lamari yana buƙatar addu'a me tsanani"
Jan zuciya tayi tace “Yanzu a haka zanta zama kenan?" Murmushi Granny tayi tace “Aa bazakiyita zama a haka ba yanzu abinma dake akwai zaki koma gabanmu ne aci aci gaba da magani har Allah ya baki lfyrki"
Zuciyarta na suya haka ta hƙr tabar mgnr ta koma ta kwanta kwana takwas ta ƙara a asibitin suka sallameta domin suma sun fahimci ciwon nata bana asibiti bane dole tasa aka nemi maganin Hausa tare da yin waya Guru aka sanar dasu halin da ake ciki Baba Na'ibi wane a gurin babanta shine ya niƙo gari ya taho Kano ya kawo mata magani cikin ikon Allah Suna fara amfani da maganin sauƙi yayita samuwa sati guda bata rufa ba wannan ƙanzo²n da fatarta tayi duk ya ɓare asalin fatarta ta dawo Baba Na'ibi yana kallonta yayi murmushi yace “komai zai wucce da yardar Allah"
*Oum Hairan*
[11/10, 8:59 PM] Oum Hairan&Affan: *MYJ39-40 Oum Hairan* Littafina na kuɗi kada ki karanta min baki biya ba don Allah idan kinaso ki biya ta 0255526235 Gtbank ko ki turo hoton katin 300 ta wannan number 09013718241 saiki tura evidance of payment ta number dai ko VTU ta 0931307566
Kwanaki har watanni sukayita wuccewa babu Aliyu babu Salma Kharimatu tanata rainon cikinta har ya isa haihuwa ranar wata asabar da yamma ta shiga bayi tana tsugunnawa taga wani jini me yauƙi ya zubo mata ta miƙe da sauri ta fita ta kira Granny dake a sashinta take zaune. Tana gani ta gane meye ke faruwa tayi murmushi tace “Abin yazo Kharimatu haihuwa ce" gabanta ya faɗi tace “Granny tun jiya marata take ciwo fah" kama hannunta tayi tace “kije ki zauna bari nayiwa Mal Hassan mgn yayi miki rubutu idan haihuwar ce ciwon zai tashi ayi a wucce gurin idan ba ita bace kuma zaiyi sauƙi"
Zaunar da ita tayi ta shiga ɗaki bata jima ba ta fito ta tarar da ita ta riƙe ciki ta cije leɓe tana ƙoƙarin zamewa daga kujerar kamota tayi ta saukar da ita ƙasa tanayi mata sannu itadai kallonta kawai takeyi tana karɓar azaba babu jimawa Mal Hassan ya aiko da rubutun Granny ta bata tasha tace ta kwanta, kwanciya tayi bacci ya ɗauketa cikin baccin taji azabar ciwon ta ƙaru ta zabura ta miƙe da sauri tana faɗin Innanillahi wa Innah Ilaihirraji'un Granny bayana marata ƙirjina wayyoh wayyoh Granny shikenan na mutu na ƙare...." Rufe mata baki tayi tace “ke ar sakarya ki rinƙa salati" fita Granny tayi tayima driven gdan mgn tazo ta ɗauko mata hijjab ɗinta tasa mata daidai lkcn Mom ta fito itama suka nufi asibiti suna zuwa aka shiga da ita labour room.
Bata wani ɓata lkc ba Ubangiji ya yassare mata ta haifo sankacecen ɗanta namiji kyakkyawa kamannin sa na mahaifinsa ne sak sumarsa da bakinsa sune kawai nata, ana gyara yaron aka sallamesu suka tafi gda sunata murna kamar ba'a taɓayi musu haihuwa ba.
Waya sukayi Guru ƙanwar Mama Yabi tazo ita da Granny suka rinƙa kula da ita abinda ya dami zuciyarta tun ranar data haihu take kiran wayar Aliyu bata shiga shikuma bai kirata ba zuciyarta na faɗa mata to ko baisan ta haihu bane?" Wannan abu sosai ya damu ranta ranar da ɗanta ya kwana biyar suna zaune take tambayar Granny Daddyn Farooq kuwa yasan ta haihu?"