← Book details Me Ya Jamin New Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 19

Sashe 14

Me Ya Jamin New Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Da asuba ita ta tasheshi yajasu sallah suka sake kwanciya ya maƙaleta batason yanda yake nuna mata nacinsa saidai bazata iya hanashi haƙƙinsa ba haka suka bawa juna aikin safe suka sake sabon bacci sai goma sukaji ana taɓa ƙofar ta miƙe da sauri ta faɗa bathroom shine ya tashi ya buɗe ƙofar yana miƙa Salma ta leƙo ɗakin tans cewa “Ina sister na kaida baka gajiya da bacci ka makarar da ita koda yake yau Sartuday ku huta abinku"
Lumshe idanunsa yayi yace “Tana bayi yanzun zata fito" yana mata bayani idanunta nakan gadon da suka turmushe da kuma bra ɗin da take ƙasa wani mashi ya caki ƙirjinta ta haɗiye wani yawu me ɗaci ta dubeshi tace “ok idan kun shirya ga breakfast can a dinning" jinjina kai yayi ta juya ta fice ya koma ya ɗebe kayan daidai lkcn data fito a wankan tana goge sumarta ya zagaya ya rungumeta ta baya yayi kissing wuyanta yace “Morning My Chocolate" murmushi Kalmar tasata.

Ta janye a jikinsa tace “kayi wanka tukunnan" nufar bathroom ɗin yayi yana cewa “kamata yayi kiyimin wankan nan ba kibani umarnin yin wankan ba" shiru tayi masa ta buɗe wardrobe ta ɗauki kayanta wasu sabbin riga da zani na atamfa tasa ta ɗaura ɗankwalin tana sanya ɗan kunne ya fito ya karɓa ya saka mata ya miƙa mata mai ya kashe mata idanu tare da nuna mata jikinsa inda sabo ta fara sabawa da sangartarsa ko lkcn da yake ɗaukar ta yakaita hotel idan yayi wanka miƙe mata yake yace ta shafa masa hakan yasa ta saba ta shafesa tsaf ta ɗauko masa kayansa data gani a gurin ta taimaka masa yasa ya kamo hannunta suka fito.

Salma na zaune ta zuba uban tagumi a parlourn taji saukowarsu tayi saurin kawar da damuwarta tana mamakin yanda taga Kharimatun lfy ƙlau nandanan taji wani baƙin ciki ya cushe mata zuciya wannan wacce irin yarinya ce duk abinda aka shirya mata yake neman watsawa a banza, ƙwafa tayi a zuciyarta tace “in kinsan wata ai bakisan wata ba zanyi maganinki bari muga kamun ludayin wannan da akace nasa miki a abincin tukunna" zama sukayi a dinning ɗin ta gaisheta cikin ladabi ta amsa da murmushin da baikai zuci ba da kanta ta haɗawa kowa break ɗin Kharimatu ta ɗauki nata a kunyace tayi bismilla takai bakinta nandanan annurin fuskar Salma ya ɗauke jin tayi bismilla abincin da bata iya ci ba kenan komanta ya rushe duk kuɗin data kashe sun tashi a banza wannan shegiyar yarinyar dole a canza taku ƙaramin asiri bazai kaita ƙasa ba saidai tsafi.
Daƙyar Salma ta rinƙa tura abincin bayan sun gama ta tashi ta kwashe kayan Kharimatu ta miƙe domin ta tayata tace “aa yi zamanki ki huta amarya bata wahala kedai ki kula mana da mijinmu shine kawai aikinki" kunya ce tasa Kharimatu ƙasa da kanta ya riƙo hannunta yace “kinji abinda akace miki ko ki kula dani" yanda yayi mgnr yabasu dariya sukayi dariya ya miƙe yace “Zanje na gaida su Hajiya ku kulamin da kanku" fatan alkhairi sukayi masa Kharimatu ta miƙe ta sake gyara parlourn suka zauna suna hirarsu sama sama Salma ke janta da hirar nandanan ta saki jikinta sukayita harkokinsu tare ranar har girki tare sukayi abinsu can yamma aka dawo musu da yaran gdan da suka tafi hutu gdan kakanninsu yaran suna ganinta suka fara murna ta jasu jikinta sukayita shirmensu a haka Aliyu ya dawo ya tarar dasu yaransa sai nishaɗi sukeyi da ganin Uwar goyonsu shima sai yajishi cikin farin ciki ya zauna a cikinsu yana tayasu Salma sai tsiya takeyi masa wai yamai da kansa yaro.

Basu suka bar parlourn ba sai goma saura na dare Muwaddat tace “Aunty yau ɗakinki zan kwana" Farooq ma yace “nima acan zan kwana" Aliyu dake zaune ya miƙe yace “Nima Aunty yau a ɗakinki zan kwana" dariya sukayi Salma tace “aikuwa saidai kai ka hƙr kabarwa yara Auntynsu" murmushi yayi yace “dake don yara aka halicce ta ba to aikuwa saidai su su hƙr subarmin so nake na samo musu ƙani da wuri" haɗiye takaicinta tayi ta nufi saman tana cewa Allah ya taimaka zanyi murna da hakan mukam munyi adabo da haihuwa" ɗaukar Jannat tayi tace “muje mu kwanta saida safe ko" miƙewa dukansu sukayi suka bita suna murna yau zasu kwana da Auntynsu. Muryar Aliyu taji a bayanta yace “My Kharry!" Tsayawa tayi ya tako ya dafata yace “ina jiranki a ɗakina" saida ƙirjinta ya buga tayi ƙarfin halin cewa ok bari na kwantar dasu"

Jinjina mata kai yayi ta nufi saman yana biye da ita ta buɗe ɗakin yaran ta kwantar dasu tare dayi musu addu'a bayan tasa musu kayan baccinsu kwanciya tayi a gefen su sunata yi mata surutu har bacci ya ɗauke su Dukansu.
Shirun Aliyu yaji tayi yawa ya miƙe ya buɗe ƙofar ya nufi ɗakin yaran ya isheta tana bacci rungume da Jannat ya zubanta ido shauƙin ƙaunarta da sha'awarta suna ɗibansa ya matsa ya zare Jannat ɗin ya kwantar da ita ya ɗagota gabadayanta ya nufi ɗakinsa da ita ya kwantarta kamar wata baby yana ƙare mata kallo yaja numfashi ya ɗora bakinsa saman lips ɗinta ta buɗe idanunta akansa shima ita yake kallo tace “ina yaran?" Dariya tambayar tabashi ya janye yace “da kina tunanin kinci bulus ne zaki tafi gurin yara kibarni shanye kamar mayafi" miƙa tayi ta tashi zanne ya zauna a gefenta yace “meye na miƙewar?" Murza idanunta tayi tace “kayan nan zan cire" janyota jikinsa yayi yace “ki kwanta abinki zan cire miki" hannu yakai bayanta ya zuge zip ɗin ya zuge na sikelt ɗin ya zare mata ya ɗora bakinsa saman wuyanta yana lasa ta lumshe idonta tanajin wata muguwar faɗuwar gaba da batasan meye ya sabbabata ba cikin lkc ƙanƙani kanta yayi wata muguwar sarawa ta sanya hannunta biyu ta riƙe kanta ta saki wata razannanniyar ƙara data sanya kowa na gdan fitowa...........

Oum Hairan
[11/6, 7:22 PM] Oum Hairan&Affan: *MYJ37-38 Oum Hairan* Littafina na kuɗi kada ki karanta min baki biya ba don Allah idan kinaso ki biya ta 0255526235 Gtbank ko ki turo hoton katin 300 ta wannan number 09013718241 saiki tura evidance of payment ta number dai ko VTU ta 0931307566

Ƙoƙarin riƙeta Aliyu yakeyi saidai tafi ƙarfinsa watsoshi tayi ƙasa itama ta zube tana wani irin abu daya tashi hankalinsa ya matsa ya riƙe ta daidai lkcn da Salmah ta turo ƙofar ta shigo tayi kansu da sauri tana faɗin subhanallah meye ya sameta?" Kallonta kawai Aliyu yayi yaci gaba da yima Kharimatu addu'a amma kamar Bama yi yakeyi ba ganin abin bana wasa bane ya tashi ya fita yana kiran wayar Alh Ma'aru dake dare baiyi nisa ba ya sameshi nan yake faɗa masa abinda yake faruwa hankalinsa ya tashi matuƙa da kansa ya fita ya ɗauko limamin unguwarsu suka nufo gdan nasu bayan ya ɗauki Granny yanayin da suka tarar da ita ya basu tsoro liman ɗin ne ya soma yi mata addu'a ta rinƙa miƙewa tana son ƙwacewa daƙyar Suka samu ta fara mgn cikin wata irin murya data tsorata kowa dake gurin sukaji ta fashe da kuka tana cewa “mu ku ƙyalemu bamu muka kawo kanmu ba ita ta taɓomu mu haukatata ko mu sanya mata ciwo mun kasa yin ko ɗaya sharaɗin zuwanmu bazamu barta ta samu ciki ba amma abin takaicin saida ciki ya shigeta" wata dariya ta ƙara fashewa da ita data sanya Salma matsawa taci gaba da soki burutsun surutunta liman nata kwarara mata karatu.

Basu suka samu ta jirge ba sai wajen asuba sannan ta kama bacci liman ya sharce gumi ya dubi Aliyu yace “ka biyoni gda ka karɓo mata rubutu gdy yayi suka fita suka barta kwance tanata baccinta suna fita Salma ta sheƙe da dariya ta matsa kusa da gadon tace “yaro man kaza kin tabka kuskure da kika bari kika shigo gonata zaki gane kurenki mijina gdana sunfi ƙarfinki sai na mayar dake abar tausayi kuma abar kwatance a duniyar maciya amana" tsaki taja ta juya ta fice daga ɗakin bai jima sosai ba ya dawo kamar yanda Mal Kabir ya faɗa masa.
Haka ya rinƙa shafa mata rubutun a ƙasan mararta zuwa ƙirjinta ta rinƙa sakin ajiyar zuciya bai jima da gama shafa mata ba ta buɗe idonta ta saukeshi a saman agogo takwas da rabi ta yunƙura zata miƙe ya ɗagata taja numfashi tare da sauke idanunta akansa yayi mata murmushi yace “Ya jikin" lumshe idonta tayi kanta har yanzu sarawa yakeyi ta buɗe idonta akansa tace “Meyesa baka tasheni da asuba ba?" Kawar dakai yayi yace “bakida lfy ne shiyasa" da wannan ta miƙe ta shiga bathroom tayi wanka ta ɗauro alwala tayi sallah ta shirya cikin wasu riga da sikert na jeans tayi kyau sosai sauka yayi ƙasa ya ɗauko mata break ya dawo.
Chapter 14 · 0% Book details