Sashe 13
Me Ya Jamin New Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haɗiye abinda ke damun zuciyarta tayi ta harari gefe tace “Uhm madalla ka gaisheta aje wayar tayi shima ya aje suna kallon juna yace “ki daina zama da yunwa banason zama da yunwa Khary" lumshe idonta tayi ta buɗe yace “Ok bazaki daina ɗinba kenan" ƙasa tayi da kanta tana wasa da hannunta ya riƙo zara²n yatsunta da sukasha lalle ya lumshe idonsa yace “lallai nan yayimin kyau" ɗagowa sukayi tare ya zuba idanunsa cikin nata yace “likita yace gobe zai sallameki kinji sauƙi am idan an sallameki gdanki zan kaiki" da sauri ta dubeshi ya ɗaga mata gira yace “hakan ya kamata zaman nan naki a gda bazai yiwu ba gara kije gdanki kema ki samu ladan aure kamar kowacce mace"
Girgiza masa kai tayi ya sanya hannu ya ɗago fuskarta yace “idan kika koma gdanki zakifi samun nutsuwa" bata iya jayayya ba hakan yasata yi masa shiru yayi murmushi yace “shiyasa nakesonki" ya ɓata lkc a asibitin kafin sukayi sallama da Granny ya tafi tunda yaje gda Salma ta kawo masa abinci ta zauna kusa dashi tana wasa da yatsunsa yana cin abincin suna hirarsu tana dariyar yaƙe saida taja hankalinsa sosai sannan ta ɗago ta dubeshi tace “My Haidar!" Dubanta yayi tare da tattara hankalinsa waje guda yace “yadai My Salmah
Sunkuyar da kanta ƙasa tayi tace “Da zakayimin wannan alfarmar da zanji daɗi sosai Aliyu nayi alƙawarin duk wani abu da kake tsoro bazai faru ba don Allah ka amince dani" aje cokalin yayi ya zubanta ido tare da cewa “Wanne Alfarma kenan?" Sosa kanta tayi tace “Kada ka raba mana gda da Kharimatu saboda yarannan kaga Ni ina zuwa aiki kuma ina yawan tafiye² idan tana gdan zasu zauna tare tunda dama sun saba rainonta ne kuma kaga nan yafi kusa da makarantarsu fiye da can inda kake gini bayan haka kaima sauƙin ka ne komai katashi siye ɗaya zaka siya na amfanin gda memakon idan ka rabamu da komai saika nemi biyu sannan inason mu samu kusanci kamar yanda Hajiyata da Hajiya ƙarama suke inason mu zama abu ɗaya ta yanda zakayi alfahari damu, Amma fah kada ka canza min fassara iyakar gskyta kenan"
Tana mgnr tana cigaba da wasa da yatsunsa.
Zubanta idanu yayi a hankali yakai hannu ya ɗago fuskarta ta lumshe idanunta tare da shigewa jikinsa shikuma ya matseta cike da so yace “Meye ya canzamin ke kikayi laushi haka ne My Salmah naga a farko kin ɗauki abin da zafi yanzun kuma kin sauka da wuri" murmushin bakada wayo tayi masa tace “tausayin Kharimatu ne ya fara canzamin tunani sai kuma nasihar Hajiyata Aliyu na gane abinda kake nufi kaine ka cancanci riƙe maraicin Kharimatu shiyasa naji a raina zan taimaka maka na tayaka riƙon amanar nan musamman da akace Mahaifiyarta kafin ta rasu ta damƙa maka ita amana"
Sosai Aliyu yaji daɗin kalaman matarsa nan take yayi mata alƙawarin haɗa su gda ɗaya da Kharimatu suka tashi sukaje suka kwanta washegari tun safe yasa aka gyara masa daya bangaren na gdan dake dama gdan nasa yanada girma akwai ɓangare ɗaki biyu manya da parlour da toilet a kowanne ɗaki sai kitchen ƙarami batare da ya sanar da kowa abinda suka shirya ba yasa aka ɗebo kayanta da aka shirya a sabon gdan aka dawo dasu nan masu shirya gidaje suka baje fasahar su wajen tsara mata sashin duk da cewar kayan sun yima ɓangaren yawa haka aka shiryasu aka zuba mata wasu a store da yake Alh Ma'aru ya narka mata kuɗi sosai a wancan gdan.
Kwana uku ta ƙara aka sallameta a asibiti da farko sunso tafiya da ita gda suci gaba da kula da ita saidai basu samu wannan damar daga mijinta ba yayi kicin²n ya matse lamba kan saidai abashi matarsa shi ya gaji da wannan galantoyin hakanan da Granny ta fusata tace “ga matarka nan idan ka tafi da ita kasa mata mai da yaji ka cinye ƙarewar so sakarai kawai"
Baiji haushi ba ta fice driver ya ɗauketa shima ya haɗa musu kayansu sai gda tunda suka taho take hawaye har sukazo ƙofar get na gdan yayi horn ta ɗago gabanta yayi muguwar faɗuwa ganin gdan da ya kawota ta dubeshi cikin kaɗuwa tace “Daddyn Farooq gdan Aunty Salma ka kawoni fah" shafa sumarsa yayi ya ɗaga mata gira yace “Gdan Aliyu dai ko Kharimatu tunda Salma batazo dashi a gara ba" numfashi ta sauke yana matsowa jikinta tace “Amma ai ba anan zan zauna ba kace dasu Granny" murmushi ya sake yi mata ya tallafi kuncinta ya ɗora bakinsa saman nata ya lashi lips ɗin ta da harshensa ya ɗago yace “Zanfi samun nutsuwa idan kuna a guri ɗaya kada ki tashi hankalinki bazaki samu matsala da Salma ba ta sauko sosai kinji My Khary"
Ƙasa tayi da kanta cikin zullumi zuciyarta na bugawa da ƙarfi taji ya buɗe motar ya fito ya buɗe mata ta zuro ƙafafunta cikin fargaba yayi gaba tana binsa a baya kamar mara gaskiya ya buɗe falon suka shiga da sallamarsa Salma dake zaune ta miƙe Kharimatu tayi saurin raɓewa a jikinsa domin mugun tsoron Salma takeji abinda yaja sukayi dariya su biyun Aliyu ya shafa bayan Kharimatu yace “My Salma kin tsoratamin mata da yawa" dariya tayi tace “Double sorry Ƙanwata ki daina jin tsorona babu abinda zanyi miki kinji" hannu tasa ta janyeta a jikinsa ta kama hannunta tana mata murmushi suka haura saman.
Ta buɗe mata ƙofar shiga sashin ta yana biye dasu a baya saida ta shigar da ita har cikin bedroom ɗinta ta zaunar da ita a gefen gado tace “amarya kike sak yau gaki a angonki ina fatan hannun bazai hana ku sakewa ba?" A mugun kunyace da al'ajabin canjin na Salma tayi ƙasa da kanta Aliyu dake tsaye yana mamakin yanda matar tasa ta sauko cikin ƙanƙanin lkc yace “sai abishi a hankali ai kinsanni da tausayi" juyowa tayi ta sakar masa murmushi tace nasan wannan yanzu meye zakuci a sama muku?"
Agogo ya duba takwas da minti biyar na dare ya ɗago yace “na hutassheki kema kije ki kwanta ki kulamin da kanki zan fita na samo abinda zamu tari baƙuwar tamu" lumshe idonta tayi tace “Idan kayi hakan zanji daɗi kaje ka dawo zan tayata hira har ka dawo" jinjina kai yayi ya juya ya fice ta zauna kusa da Anam tana kallonta tana saƙa abubuwa da yawa a ranta tana murmushin da ita kaɗai tasan ma'anarsa haka suka zauna jefi² tana yima Anam hira itadai saidai tayi ajiyar zuciya domin kuwa zuciyar Tata a karye take kukan ne kawai batason tabashi damar zuwa.
Sun jima a zaune Kharimatu har ta farajin bacci sukaji shigowarsa ya buɗe ƙofar ya shigo da sallamarsa ya aje ledojin ya fara ƙoƙarin cire rigarsa yace “Am My Salmah ki ɗauki leda biyu ki tafi dashi na gde da kulawa Allah yabarni daku a haka" miƙewa tayi ta ɗauka tayi musu sallama daƙyar ta haɗiye abinda yake cakar zuciyarta ta shiga ɗakinta ta kulle tayi jifa da ledar hannun nata ta zube a jikin ƙofar ta ɗora hannunta akanta zata kurma ihu tayi saurin toshe bakinta taja ɗuwawu ta isa jikin gadon ta haɗe kanta da gadon ta saki kuka.
Zama yayi kusa da Kharimatu ya kamo hannunta da hannunsa yakai bakinsa yayi kissing nata yaja fasali yace “ya kikeji a zuciyarki game da wannan sauyin da aka samu a gurin Auntynki?" Ɗago manyan idanunta tayi ta saukesu akansa baisan meye yasa ba baya jure su haɗa ido da yarinyar mugun kwarjinin takeyi masa hakan yasa ya sauke idonsa yace “kiyi mgn" ajiyar zuciya tayi ta yunƙura zata miƙe ya janyota ta faɗo jikinsa yakai hannu ya riƙe hannunta me ciwon ya saita fuskarsa a tata tare da haɗe bakinsu guri ɗaya suka lumshe ido a tare duk da a mugun tsorace take dashi haka ya rinƙa sarrafata bai ƙyaleta ba saida ya samu nutsuwa da ita sosai ya shafa saman goshinta yace “kina da baiwa My Kharry Allah yayi miki albarka" itadai kunyarsa takeji sosai duk da ba wannan ne karo na farko da hakan take faruwa tsakaninsu ba inda sabo ma kusan ta saba dashi a cikin watannin auren nasu baya bata da sauƙi.
Bayan komai ya nutsa ne sunyi wanka ya buɗe musu abinda ya siyo sukaci dakansa ya rinƙa bata a baki sukaci sukayi hani'an sannan sukayi brush Suka sake kwanciya, saime cikin dare kamar wacce aka tsikarawa allura ta zabura ta miƙe cikin wani irin tashin hankali tana furta “A'uzubillahi minasshaiɗanur rajim Innanillahi wa Innah Ilaihirraji'un" shima tashi yayi a firgice ya riƙeta da ƙarfi yana kiran sunanta ta ƙanƙameshi jikinta yana wata muguwar tsuma ƙirjinta sai bugawa yakeyi da ƙarfi.
[11/6, 7:22 PM] Oum Hairan&Affan: *MYJ35-36 Oum Hairan* Littafina na kuɗi kada ki karanta min baki biya ba don Allah idan kinaso ki biya ta 0255526235 Gtbank ko ki turo hoton katin 300 ta wannan number 09013718241 saiki tura evidance of payment ta number dai ko VTU ta 0931307566
Kiran sunanta yayi da ƙarfi yana cewa “Me... Meye ya firgitaki haka meye damuwarki" sake shigewa tayi jikinsa tanajan ajiyar zuciya ganin yanda ta fice a hayyaci lkc guda yasashi fara tofa mata ayatul kursiyyu a tsakiyar kanta da addu'o'in neman tsari a hankali yaji zufa yana keto mata zuwa anjima kuma yaji taja fasali ya nitsa hannunsa cikin sumarta yace “Meye ya tsorataki haka My Khary?" Numfashi ta sauke ta ɗago ƙwayar idanunta da suke cike da bacci ta sauke akan fuskarsa ta sake jan fasali ta kwantar da kanta a ƙirjinsa tace “Wasu irin halittu ne masu kama da gizo² suka biyoni suka ɗafemin jikina suna cizona kuma duk inda suka cijeni rami yakeyi shine inata neman taimakonka kawai kayi tafiyarka ka ƙyaleni a tsakiyarsu inata kiranka kaƙi juyowa"
Shafa bayanta yayi yace sharrin mafarki ne kawai shine kika tashi kina ihu salon ki tashi mutanen gidan oya koma mu kwanta saida safe" komawa sukayi suka kwanta ta sake sabuwar addu'a bacci ya ɗauke ta tana maƙale a ƙirjinsa shikam hakanan yaji zuciyarsa taƙi kwanciya da labarin mafarkinta data bashi koda yaga tayi bacci saida ya sake tofeta da addu'a sannan shima yayi baccin.
Girgiza masa kai tayi ya sanya hannu ya ɗago fuskarta yace “idan kika koma gdanki zakifi samun nutsuwa" bata iya jayayya ba hakan yasata yi masa shiru yayi murmushi yace “shiyasa nakesonki" ya ɓata lkc a asibitin kafin sukayi sallama da Granny ya tafi tunda yaje gda Salma ta kawo masa abinci ta zauna kusa dashi tana wasa da yatsunsa yana cin abincin suna hirarsu tana dariyar yaƙe saida taja hankalinsa sosai sannan ta ɗago ta dubeshi tace “My Haidar!" Dubanta yayi tare da tattara hankalinsa waje guda yace “yadai My Salmah
Sunkuyar da kanta ƙasa tayi tace “Da zakayimin wannan alfarmar da zanji daɗi sosai Aliyu nayi alƙawarin duk wani abu da kake tsoro bazai faru ba don Allah ka amince dani" aje cokalin yayi ya zubanta ido tare da cewa “Wanne Alfarma kenan?" Sosa kanta tayi tace “Kada ka raba mana gda da Kharimatu saboda yarannan kaga Ni ina zuwa aiki kuma ina yawan tafiye² idan tana gdan zasu zauna tare tunda dama sun saba rainonta ne kuma kaga nan yafi kusa da makarantarsu fiye da can inda kake gini bayan haka kaima sauƙin ka ne komai katashi siye ɗaya zaka siya na amfanin gda memakon idan ka rabamu da komai saika nemi biyu sannan inason mu samu kusanci kamar yanda Hajiyata da Hajiya ƙarama suke inason mu zama abu ɗaya ta yanda zakayi alfahari damu, Amma fah kada ka canza min fassara iyakar gskyta kenan"
Tana mgnr tana cigaba da wasa da yatsunsa.
Zubanta idanu yayi a hankali yakai hannu ya ɗago fuskarta ta lumshe idanunta tare da shigewa jikinsa shikuma ya matseta cike da so yace “Meye ya canzamin ke kikayi laushi haka ne My Salmah naga a farko kin ɗauki abin da zafi yanzun kuma kin sauka da wuri" murmushin bakada wayo tayi masa tace “tausayin Kharimatu ne ya fara canzamin tunani sai kuma nasihar Hajiyata Aliyu na gane abinda kake nufi kaine ka cancanci riƙe maraicin Kharimatu shiyasa naji a raina zan taimaka maka na tayaka riƙon amanar nan musamman da akace Mahaifiyarta kafin ta rasu ta damƙa maka ita amana"
Sosai Aliyu yaji daɗin kalaman matarsa nan take yayi mata alƙawarin haɗa su gda ɗaya da Kharimatu suka tashi sukaje suka kwanta washegari tun safe yasa aka gyara masa daya bangaren na gdan dake dama gdan nasa yanada girma akwai ɓangare ɗaki biyu manya da parlour da toilet a kowanne ɗaki sai kitchen ƙarami batare da ya sanar da kowa abinda suka shirya ba yasa aka ɗebo kayanta da aka shirya a sabon gdan aka dawo dasu nan masu shirya gidaje suka baje fasahar su wajen tsara mata sashin duk da cewar kayan sun yima ɓangaren yawa haka aka shiryasu aka zuba mata wasu a store da yake Alh Ma'aru ya narka mata kuɗi sosai a wancan gdan.
Kwana uku ta ƙara aka sallameta a asibiti da farko sunso tafiya da ita gda suci gaba da kula da ita saidai basu samu wannan damar daga mijinta ba yayi kicin²n ya matse lamba kan saidai abashi matarsa shi ya gaji da wannan galantoyin hakanan da Granny ta fusata tace “ga matarka nan idan ka tafi da ita kasa mata mai da yaji ka cinye ƙarewar so sakarai kawai"
Baiji haushi ba ta fice driver ya ɗauketa shima ya haɗa musu kayansu sai gda tunda suka taho take hawaye har sukazo ƙofar get na gdan yayi horn ta ɗago gabanta yayi muguwar faɗuwa ganin gdan da ya kawota ta dubeshi cikin kaɗuwa tace “Daddyn Farooq gdan Aunty Salma ka kawoni fah" shafa sumarsa yayi ya ɗaga mata gira yace “Gdan Aliyu dai ko Kharimatu tunda Salma batazo dashi a gara ba" numfashi ta sauke yana matsowa jikinta tace “Amma ai ba anan zan zauna ba kace dasu Granny" murmushi ya sake yi mata ya tallafi kuncinta ya ɗora bakinsa saman nata ya lashi lips ɗin ta da harshensa ya ɗago yace “Zanfi samun nutsuwa idan kuna a guri ɗaya kada ki tashi hankalinki bazaki samu matsala da Salma ba ta sauko sosai kinji My Khary"
Ƙasa tayi da kanta cikin zullumi zuciyarta na bugawa da ƙarfi taji ya buɗe motar ya fito ya buɗe mata ta zuro ƙafafunta cikin fargaba yayi gaba tana binsa a baya kamar mara gaskiya ya buɗe falon suka shiga da sallamarsa Salma dake zaune ta miƙe Kharimatu tayi saurin raɓewa a jikinsa domin mugun tsoron Salma takeji abinda yaja sukayi dariya su biyun Aliyu ya shafa bayan Kharimatu yace “My Salma kin tsoratamin mata da yawa" dariya tayi tace “Double sorry Ƙanwata ki daina jin tsorona babu abinda zanyi miki kinji" hannu tasa ta janyeta a jikinsa ta kama hannunta tana mata murmushi suka haura saman.
Ta buɗe mata ƙofar shiga sashin ta yana biye dasu a baya saida ta shigar da ita har cikin bedroom ɗinta ta zaunar da ita a gefen gado tace “amarya kike sak yau gaki a angonki ina fatan hannun bazai hana ku sakewa ba?" A mugun kunyace da al'ajabin canjin na Salma tayi ƙasa da kanta Aliyu dake tsaye yana mamakin yanda matar tasa ta sauko cikin ƙanƙanin lkc yace “sai abishi a hankali ai kinsanni da tausayi" juyowa tayi ta sakar masa murmushi tace nasan wannan yanzu meye zakuci a sama muku?"
Agogo ya duba takwas da minti biyar na dare ya ɗago yace “na hutassheki kema kije ki kwanta ki kulamin da kanki zan fita na samo abinda zamu tari baƙuwar tamu" lumshe idonta tayi tace “Idan kayi hakan zanji daɗi kaje ka dawo zan tayata hira har ka dawo" jinjina kai yayi ya juya ya fice ta zauna kusa da Anam tana kallonta tana saƙa abubuwa da yawa a ranta tana murmushin da ita kaɗai tasan ma'anarsa haka suka zauna jefi² tana yima Anam hira itadai saidai tayi ajiyar zuciya domin kuwa zuciyar Tata a karye take kukan ne kawai batason tabashi damar zuwa.
Sun jima a zaune Kharimatu har ta farajin bacci sukaji shigowarsa ya buɗe ƙofar ya shigo da sallamarsa ya aje ledojin ya fara ƙoƙarin cire rigarsa yace “Am My Salmah ki ɗauki leda biyu ki tafi dashi na gde da kulawa Allah yabarni daku a haka" miƙewa tayi ta ɗauka tayi musu sallama daƙyar ta haɗiye abinda yake cakar zuciyarta ta shiga ɗakinta ta kulle tayi jifa da ledar hannun nata ta zube a jikin ƙofar ta ɗora hannunta akanta zata kurma ihu tayi saurin toshe bakinta taja ɗuwawu ta isa jikin gadon ta haɗe kanta da gadon ta saki kuka.
Zama yayi kusa da Kharimatu ya kamo hannunta da hannunsa yakai bakinsa yayi kissing nata yaja fasali yace “ya kikeji a zuciyarki game da wannan sauyin da aka samu a gurin Auntynki?" Ɗago manyan idanunta tayi ta saukesu akansa baisan meye yasa ba baya jure su haɗa ido da yarinyar mugun kwarjinin takeyi masa hakan yasa ya sauke idonsa yace “kiyi mgn" ajiyar zuciya tayi ta yunƙura zata miƙe ya janyota ta faɗo jikinsa yakai hannu ya riƙe hannunta me ciwon ya saita fuskarsa a tata tare da haɗe bakinsu guri ɗaya suka lumshe ido a tare duk da a mugun tsorace take dashi haka ya rinƙa sarrafata bai ƙyaleta ba saida ya samu nutsuwa da ita sosai ya shafa saman goshinta yace “kina da baiwa My Kharry Allah yayi miki albarka" itadai kunyarsa takeji sosai duk da ba wannan ne karo na farko da hakan take faruwa tsakaninsu ba inda sabo ma kusan ta saba dashi a cikin watannin auren nasu baya bata da sauƙi.
Bayan komai ya nutsa ne sunyi wanka ya buɗe musu abinda ya siyo sukaci dakansa ya rinƙa bata a baki sukaci sukayi hani'an sannan sukayi brush Suka sake kwanciya, saime cikin dare kamar wacce aka tsikarawa allura ta zabura ta miƙe cikin wani irin tashin hankali tana furta “A'uzubillahi minasshaiɗanur rajim Innanillahi wa Innah Ilaihirraji'un" shima tashi yayi a firgice ya riƙeta da ƙarfi yana kiran sunanta ta ƙanƙameshi jikinta yana wata muguwar tsuma ƙirjinta sai bugawa yakeyi da ƙarfi.
[11/6, 7:22 PM] Oum Hairan&Affan: *MYJ35-36 Oum Hairan* Littafina na kuɗi kada ki karanta min baki biya ba don Allah idan kinaso ki biya ta 0255526235 Gtbank ko ki turo hoton katin 300 ta wannan number 09013718241 saiki tura evidance of payment ta number dai ko VTU ta 0931307566
Kiran sunanta yayi da ƙarfi yana cewa “Me... Meye ya firgitaki haka meye damuwarki" sake shigewa tayi jikinsa tanajan ajiyar zuciya ganin yanda ta fice a hayyaci lkc guda yasashi fara tofa mata ayatul kursiyyu a tsakiyar kanta da addu'o'in neman tsari a hankali yaji zufa yana keto mata zuwa anjima kuma yaji taja fasali ya nitsa hannunsa cikin sumarta yace “Meye ya tsorataki haka My Khary?" Numfashi ta sauke ta ɗago ƙwayar idanunta da suke cike da bacci ta sauke akan fuskarsa ta sake jan fasali ta kwantar da kanta a ƙirjinsa tace “Wasu irin halittu ne masu kama da gizo² suka biyoni suka ɗafemin jikina suna cizona kuma duk inda suka cijeni rami yakeyi shine inata neman taimakonka kawai kayi tafiyarka ka ƙyaleni a tsakiyarsu inata kiranka kaƙi juyowa"
Shafa bayanta yayi yace sharrin mafarki ne kawai shine kika tashi kina ihu salon ki tashi mutanen gidan oya koma mu kwanta saida safe" komawa sukayi suka kwanta ta sake sabuwar addu'a bacci ya ɗauke ta tana maƙale a ƙirjinsa shikam hakanan yaji zuciyarsa taƙi kwanciya da labarin mafarkinta data bashi koda yaga tayi bacci saida ya sake tofeta da addu'a sannan shima yayi baccin.