Sashe 7
Matar Police Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jidda ta ce, "Yauwa ki saurareni in mi ki fada ehee ban da rawar kai, kuma karki Yarda ya rainaki Wallahi, kina sa shi aiki, kamar irin wanki da sharar tsakar gida, kar ki kuskura ki na washe ma sa baki kalan ya rainaki kin San haka mazan su ke fa hmm na fada mi ki nidai, sannan yadda na ga Mamana na yi dare na yi kiyi kwaskwari ma ki chanja kaya, ita dai kam wanka ta ke Amman ni kwaskwarima zannayi Dan wanka zai na kodar min da jiki, ke ma in kinga zaki iya wankan to Shikenan ki na yi,kuma zan zo ma in koya mi ki girkin yan birni, sannan fa in kin gashi karkina zama ba hijabi kin tuna abin da mallam ya ke fada mana amakaranta? Yauwa sai ma me zan ce miki? In him ki dinga irin kwalliyar nan da na koya mi ki kinji."
Ita kuwa Lantana sai bin Jidda da Ido kawai ta ke.
Indo ta ce, "Kin manta baki tuna mata maganar tafiyar nan ba."
Jidda ta ce, "Yauwa wannan tafiyar da na koya mi ki haka fa zaki na mishi kina Dan fari da ido, hhhh haka ake yasin."
Ta ce la na Dada mantawa ma kawo kunnenki kiji Lantana ta kawo kunnenta suna gama magana kawai naga sun birke da dariya.
Angwaye su ka yi sallama da sauri Jidda ta rufewa Lantana fuska da mayafi.
Suna shigo Jidda da indo su ka amsa.
Ummaru ya ce, "Ah Hajiya Jidda Ikon Allah."
Hararshi ta yi ta ce, "Kai dai kaji da shi, sai wani washe baki ka ke ko kunya."
Adamu ya ce, "To mallama Jidda amana Addu'a."
Gyara zama tayi tare da murtuke fuska kamar wa ta babbar ma ta ta ce, "To bismillah da fatiha, ta kammala da fadin Ammen kan ta cigaba, " To Allah ya sanya alkairy, Allah ya sa kar ka mata kishiya, Allah sa kana tayata aiki, Allah rabaku da dambe kamar yadda Innar lantana da babanta ke yi, Allah ba Ku 'ya'ya dozin-dozin."
Amsawa su ke da amin kawai, Jidda ta ce, "To maza asallame mu muyi gaba."
Adam ya ce, "Gashinan awajena in mun fita zan Baku."
Har sun tashi za su fita Jidda ta je dai-dai kunnen lantana ta ce, "Ni dai karki manta aragemin sauran tsire da kifi har ma da lemun kwalbar da asuba za mu zo karfa, sannan kar ki manta da abin da na fada mi ki dazu."
Har sunje bakin kofa ta kara juyowa ,"karki manta fa."
Lantana ta daga ma ta kai.
Su na fita Jidda ta fara Harar Adamu ta na murguda baki , "Ni ka sallame mu kawai mu yi gaba mu na da abin yi fa."
Har da juya mi shi baya.
Ciro dubu daya ya yi ya ce, "to gashinan."
Karba ta yi tana washe baki, "Ah lallai ka ce kai ma Alhaji ne kamar babana to mungode."
Adam ya ce, "Ah tsaya ma na kiji."
Gwalo ta mi shi ta na tafiya tare da fadin, "Sai da Safe Dan samrayi."
Ba ason ran Adam ba haka Jidda ta tafi ta bar shi tsaye awajen.
Jidda ta ce, "Indo ga kudin nan ki tafi dashi kawai da safe in zamu tafi boko kya mana chanji, yauwa karki manta da asuba za mu je cin tsiren Lantana."
Dariya Indo ta yi kan ta ce, "Shikenan ina idar da sallah zan zo yasin."
,,,,,, haka kuwa akayi Jidda na idar da sallah ta sha ruwan shayin ta na fama sai ko ga Indo.
Iya ta ce, "Ina za Ku je haka?"
Jidda ta ce, "Gidan lantana ma na cin tsiren amare kalan mu bari aje a cinye."
Iya ta daura hannu a ka , "Oh ni Ibrahim ya haifo min wadda ta fi ni iya shegeni, ni ko zamanin mu mu kan bari hantsi ya fito kan muje Amman fa Ku da duku-duku haka? Ku bari garin ya Dan washe mana."
Jidda ta murguda baki , "Mu ina ruwan mu walle sai munje in ma ba su tashi sallah ba ma tashesu kin san lantana da shegen barcin tsiya."
Iya ta ce, "Yo ai Shikenan ni dai aragomin tsiren."
Jidda ta ce, "Tab walle cinye kayanmu za mu yi naga ke ma lokacin da Kakana ya ke Raye ai kinci kuma Baki rage min ba."
Iya ta yi shewa, "Lallai ma Jiddatu yo shi kakan na ki ma da bai kawo tsire ba sai kosai."
Jidda ta galla ma ta harara , "andai ji kuma ysin ba zana ragoma ki ba."
Fita suka yi suna zuwa kuwa ko Sallah su lantana da ummaru ba su yi su na ta barci, kwankwaso kofar galan-galan din ne ya farkar da ummaru, azubure ya je ya bude kofar ganin Su Jidda kafe ne ya sa shi suman tsaye.
"Wato ma ko tashi sallar ba kuyi ba yanzu ai kwayi ni matsamin in shige." Cewar Jidda.
Abin ya matukar batawa ummaru rai Amman ba yadda ya iya haka ya nufi massallaci.
Suna shiga Jidda ta fara dukan Lantana, "Dallah ki tashi wawiya ko sallah daga ke har mijin na ki ba Ku yi ba, ni tashi ki ba mu tsiren mu da sauran lemon kwalba."
Ta shi Lanta ta yi ta na mitsika Ido ta daga filon ta ta mikawa Jidda.
Jidda ta sake baki, " kambu Dan wannan za Ku rage ma na."
Lantana ta ce, "Jidda Wallahi wannan din ma da dambe da kwatan ma Ku fa sai ci ya ke ya ma fi ni ci."
Jidda na ci ta na, "Amman lallai wannan Ummaru ya Iya shege sai mun gyara ma sa zama wa to ko kunya ma."
Indo ma naci ta na, "Amman yau za ki shirya mu je boko ko?"
Jidda ta ce, "Ai dolen ta ma Yanzu ki tashi ki yi sallah, in kin gama komai za mu biyo mi ki mutafi bokon."
Lantana ta tashi ta na, "To ni kayan boko na ma na gida."
Urs Xayyeesherth
[11/13, 1:57 PM] Xayyeesherth: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation
°°°°°° _*MATAR POLICE*_ °°°°°°
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*🤝
__________________________________________________________
_We Are Here To Educate,Motivate, And Entertain Our Readers._
__________________________________________________________
_*Matar Police kirkirarren labarine mai cike da barkwanci, fadakarwa,nishadantarwa tare da sabon salo na mussaman domin farantawa masoya littafaina*_
_*LABARI DA RUBUTAWA*_
_*AISHA MOHAMMED SANI (Xayyeesherthul-humaerath)*_
_LITTAFAN MARUBUCIYAR_
1- _BABU RUWAN SO_
2- _KUCHAKAR KISHIYA_
3- _WASA DA SO_
4- _AZZAWAJUL-MUKADDAR_
5- _JAMEEL (Nafseen)_
6- _KWADAYI 2020_
AND NOW *MATAR POLICE*
_LITTAFINA NA KUDINE INDAI KI NA SON CIGABAN ZA KI TURO KATIN 200 KACAL TA WANNAN NUMBER 08103080717 SANNAN KI YI SCREENSHOT DOMIN TUROMIN DA SHEDAR BIYA_
_*BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM*_
*_FREE PAGE 16/17_*
****************
************
******************
Jidda ta ce,"Ai sai ki tafi dana jikinki kawai."
Sannan ta tashi.
Indo ta ce, "Mu kam mun tafi muje mu shirya, Yau fa in aka tashi za mu zo nan mu yi girki."
Lantana ta ce, "To daman ni ban ma Iya girkin ba kwa koyamin."
Jidda na fita tana fadin, "Ai ko za mu koya mi ki irin na yan birni ma."
Lantana harda tsalle ta na murna za ta koyi girki,irin na yan birni ma.
Kamar yadda Jidda ta ce ko haka akayi Ummaru na shigowa ya ga Lantana na kokawar fita.
"Ah'ah Amarsu ina za kije yanzu ko kin manta cewa amare ba sa fitane bare ma in za su fita sai da izinin mai gida ko?"
Lantana ta tabe baki za ta yi kuka, "Ni Wallahi zan je, ni Wallahi in ba ka barni na je ba, ba ma ruwana da kai, kuma kai ba Angona ba ne, kuma fa in ban je ba su Jiddatu ba za su zo su koyamin girkin yan birni ba."
Ummaru ya ce, "Dan Allah ki yi hakuri kar ki sa a zata wani abin na ke mi ki, yi shiru za ki je, ai ko Dan girkin birni ma na barki ki je, kin ga yau na fadawa su Adamu da Mustapha har ma da Lawandi su zo, su kwashi girkin yan birni."
Lantana ta yi tsalle ta na, "Yauwa Angon lantana, shiyasa na ke son Ka fa."
Ummaru ya ce, "Allah ko?"
Lantana ta ce, "Eh ma na irin Son yan birni ma na ke ma, me ma suke cewa? Kamar Jidda ta koyamin Yauwa, Lilivi lovi yoh."
Ta karasa fada ta na rufe fuska.
Ummaru ya sa hannu a kirji, "Aradu har kin sa na ji kifiyar so da kaunarki ta cekeni a kirji, yanzu to fa ko wanka bakiyi ba ko sai kin dawo ne."
Ta na wani fari da Ido ta ce, "Eh mana."
Ummaru ya ce, "To ai karki tafi da yunwa bara in karbo ma na shayi da burodi mu ci ko."
Lantana ta ce, "Yauwa daman rabona da burodi tin ran Sallah da Jidda ta sammana."
Cikin Murmushi Ummaru ya ce,"yau kam zakici har ma sai ya ginsheki."
Zuwa ya yi, ya siyo ma su, kan kici me lantana har ta kusa cinye biredin.
Ummaru dai ya siyo Abu Amman ya fi karfin shi haka ya yi hakuri har su Ka kammala.
Lantana ta tashi , "To ni natafi Ka gyara gidan Ka yi wanke-wanken ko?"
Ummaru ya ce, "Angama Amarya Amman mu je in fara rakaki ko?"
Lantana ta ce,"To mu je."
Suna fita sun fara tafiya kenan sai ga su Jidda da Indo.
Indo ta ce,"Yauwa sai mu hice makarantar ai daman gidan ki mu Ka nufa."
Ummaru ya ce,"To ai hikenan mu je in Dan taka ma ku. "
Jidda ta galla mi shi harara, "To bayan ma ko rikye ma ta hannu ba kayi ba wannan ai kauyancine."
Ta yo gabansu ta daga hannun Lantana da na Ummaru ta hada ta na, "Yauwa kunga yanzu kowa ya ganku ya San amarene."
Sai da suka isa kofar skul din kan Ummaru ya jiyo da niyar komawa gida.
Da karfi lantana ke magana, "Kar Ka manta da wanke-wanke fa kaji ko."
Ummaru ya ce,"Yanzu ma kuwa Amarya."
Suna shiga ana dukan wa inda suka makara Jidda ta ce, "Lallai Yau in malamin nan ya ta ba ni zai ga masifa."
Indo ta ce, "Allah sarki ita kam lantana Yanzu ba mai dukanta kamar yadda ba a dukan su Sha'awa."
Ita kuwa Lantana sai bin Jidda da Ido kawai ta ke.
Indo ta ce, "Kin manta baki tuna mata maganar tafiyar nan ba."
Jidda ta ce, "Yauwa wannan tafiyar da na koya mi ki haka fa zaki na mishi kina Dan fari da ido, hhhh haka ake yasin."
Ta ce la na Dada mantawa ma kawo kunnenki kiji Lantana ta kawo kunnenta suna gama magana kawai naga sun birke da dariya.
Angwaye su ka yi sallama da sauri Jidda ta rufewa Lantana fuska da mayafi.
Suna shigo Jidda da indo su ka amsa.
Ummaru ya ce, "Ah Hajiya Jidda Ikon Allah."
Hararshi ta yi ta ce, "Kai dai kaji da shi, sai wani washe baki ka ke ko kunya."
Adamu ya ce, "To mallama Jidda amana Addu'a."
Gyara zama tayi tare da murtuke fuska kamar wa ta babbar ma ta ta ce, "To bismillah da fatiha, ta kammala da fadin Ammen kan ta cigaba, " To Allah ya sanya alkairy, Allah ya sa kar ka mata kishiya, Allah sa kana tayata aiki, Allah rabaku da dambe kamar yadda Innar lantana da babanta ke yi, Allah ba Ku 'ya'ya dozin-dozin."
Amsawa su ke da amin kawai, Jidda ta ce, "To maza asallame mu muyi gaba."
Adam ya ce, "Gashinan awajena in mun fita zan Baku."
Har sun tashi za su fita Jidda ta je dai-dai kunnen lantana ta ce, "Ni dai karki manta aragemin sauran tsire da kifi har ma da lemun kwalbar da asuba za mu zo karfa, sannan kar ki manta da abin da na fada mi ki dazu."
Har sunje bakin kofa ta kara juyowa ,"karki manta fa."
Lantana ta daga ma ta kai.
Su na fita Jidda ta fara Harar Adamu ta na murguda baki , "Ni ka sallame mu kawai mu yi gaba mu na da abin yi fa."
Har da juya mi shi baya.
Ciro dubu daya ya yi ya ce, "to gashinan."
Karba ta yi tana washe baki, "Ah lallai ka ce kai ma Alhaji ne kamar babana to mungode."
Adam ya ce, "Ah tsaya ma na kiji."
Gwalo ta mi shi ta na tafiya tare da fadin, "Sai da Safe Dan samrayi."
Ba ason ran Adam ba haka Jidda ta tafi ta bar shi tsaye awajen.
Jidda ta ce, "Indo ga kudin nan ki tafi dashi kawai da safe in zamu tafi boko kya mana chanji, yauwa karki manta da asuba za mu je cin tsiren Lantana."
Dariya Indo ta yi kan ta ce, "Shikenan ina idar da sallah zan zo yasin."
,,,,,, haka kuwa akayi Jidda na idar da sallah ta sha ruwan shayin ta na fama sai ko ga Indo.
Iya ta ce, "Ina za Ku je haka?"
Jidda ta ce, "Gidan lantana ma na cin tsiren amare kalan mu bari aje a cinye."
Iya ta daura hannu a ka , "Oh ni Ibrahim ya haifo min wadda ta fi ni iya shegeni, ni ko zamanin mu mu kan bari hantsi ya fito kan muje Amman fa Ku da duku-duku haka? Ku bari garin ya Dan washe mana."
Jidda ta murguda baki , "Mu ina ruwan mu walle sai munje in ma ba su tashi sallah ba ma tashesu kin san lantana da shegen barcin tsiya."
Iya ta ce, "Yo ai Shikenan ni dai aragomin tsiren."
Jidda ta ce, "Tab walle cinye kayanmu za mu yi naga ke ma lokacin da Kakana ya ke Raye ai kinci kuma Baki rage min ba."
Iya ta yi shewa, "Lallai ma Jiddatu yo shi kakan na ki ma da bai kawo tsire ba sai kosai."
Jidda ta galla ma ta harara , "andai ji kuma ysin ba zana ragoma ki ba."
Fita suka yi suna zuwa kuwa ko Sallah su lantana da ummaru ba su yi su na ta barci, kwankwaso kofar galan-galan din ne ya farkar da ummaru, azubure ya je ya bude kofar ganin Su Jidda kafe ne ya sa shi suman tsaye.
"Wato ma ko tashi sallar ba kuyi ba yanzu ai kwayi ni matsamin in shige." Cewar Jidda.
Abin ya matukar batawa ummaru rai Amman ba yadda ya iya haka ya nufi massallaci.
Suna shiga Jidda ta fara dukan Lantana, "Dallah ki tashi wawiya ko sallah daga ke har mijin na ki ba Ku yi ba, ni tashi ki ba mu tsiren mu da sauran lemon kwalba."
Ta shi Lanta ta yi ta na mitsika Ido ta daga filon ta ta mikawa Jidda.
Jidda ta sake baki, " kambu Dan wannan za Ku rage ma na."
Lantana ta ce, "Jidda Wallahi wannan din ma da dambe da kwatan ma Ku fa sai ci ya ke ya ma fi ni ci."
Jidda na ci ta na, "Amman lallai wannan Ummaru ya Iya shege sai mun gyara ma sa zama wa to ko kunya ma."
Indo ma naci ta na, "Amman yau za ki shirya mu je boko ko?"
Jidda ta ce, "Ai dolen ta ma Yanzu ki tashi ki yi sallah, in kin gama komai za mu biyo mi ki mutafi bokon."
Lantana ta tashi ta na, "To ni kayan boko na ma na gida."
Urs Xayyeesherth
[11/13, 1:57 PM] Xayyeesherth: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation
°°°°°° _*MATAR POLICE*_ °°°°°°
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*🤝
__________________________________________________________
_We Are Here To Educate,Motivate, And Entertain Our Readers._
__________________________________________________________
_*Matar Police kirkirarren labarine mai cike da barkwanci, fadakarwa,nishadantarwa tare da sabon salo na mussaman domin farantawa masoya littafaina*_
_*LABARI DA RUBUTAWA*_
_*AISHA MOHAMMED SANI (Xayyeesherthul-humaerath)*_
_LITTAFAN MARUBUCIYAR_
1- _BABU RUWAN SO_
2- _KUCHAKAR KISHIYA_
3- _WASA DA SO_
4- _AZZAWAJUL-MUKADDAR_
5- _JAMEEL (Nafseen)_
6- _KWADAYI 2020_
AND NOW *MATAR POLICE*
_LITTAFINA NA KUDINE INDAI KI NA SON CIGABAN ZA KI TURO KATIN 200 KACAL TA WANNAN NUMBER 08103080717 SANNAN KI YI SCREENSHOT DOMIN TUROMIN DA SHEDAR BIYA_
_*BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM*_
*_FREE PAGE 16/17_*
****************
************
******************
Jidda ta ce,"Ai sai ki tafi dana jikinki kawai."
Sannan ta tashi.
Indo ta ce, "Mu kam mun tafi muje mu shirya, Yau fa in aka tashi za mu zo nan mu yi girki."
Lantana ta ce, "To daman ni ban ma Iya girkin ba kwa koyamin."
Jidda na fita tana fadin, "Ai ko za mu koya mi ki irin na yan birni ma."
Lantana harda tsalle ta na murna za ta koyi girki,irin na yan birni ma.
Kamar yadda Jidda ta ce ko haka akayi Ummaru na shigowa ya ga Lantana na kokawar fita.
"Ah'ah Amarsu ina za kije yanzu ko kin manta cewa amare ba sa fitane bare ma in za su fita sai da izinin mai gida ko?"
Lantana ta tabe baki za ta yi kuka, "Ni Wallahi zan je, ni Wallahi in ba ka barni na je ba, ba ma ruwana da kai, kuma kai ba Angona ba ne, kuma fa in ban je ba su Jiddatu ba za su zo su koyamin girkin yan birni ba."
Ummaru ya ce, "Dan Allah ki yi hakuri kar ki sa a zata wani abin na ke mi ki, yi shiru za ki je, ai ko Dan girkin birni ma na barki ki je, kin ga yau na fadawa su Adamu da Mustapha har ma da Lawandi su zo, su kwashi girkin yan birni."
Lantana ta yi tsalle ta na, "Yauwa Angon lantana, shiyasa na ke son Ka fa."
Ummaru ya ce, "Allah ko?"
Lantana ta ce, "Eh ma na irin Son yan birni ma na ke ma, me ma suke cewa? Kamar Jidda ta koyamin Yauwa, Lilivi lovi yoh."
Ta karasa fada ta na rufe fuska.
Ummaru ya sa hannu a kirji, "Aradu har kin sa na ji kifiyar so da kaunarki ta cekeni a kirji, yanzu to fa ko wanka bakiyi ba ko sai kin dawo ne."
Ta na wani fari da Ido ta ce, "Eh mana."
Ummaru ya ce, "To ai karki tafi da yunwa bara in karbo ma na shayi da burodi mu ci ko."
Lantana ta ce, "Yauwa daman rabona da burodi tin ran Sallah da Jidda ta sammana."
Cikin Murmushi Ummaru ya ce,"yau kam zakici har ma sai ya ginsheki."
Zuwa ya yi, ya siyo ma su, kan kici me lantana har ta kusa cinye biredin.
Ummaru dai ya siyo Abu Amman ya fi karfin shi haka ya yi hakuri har su Ka kammala.
Lantana ta tashi , "To ni natafi Ka gyara gidan Ka yi wanke-wanken ko?"
Ummaru ya ce, "Angama Amarya Amman mu je in fara rakaki ko?"
Lantana ta ce,"To mu je."
Suna fita sun fara tafiya kenan sai ga su Jidda da Indo.
Indo ta ce,"Yauwa sai mu hice makarantar ai daman gidan ki mu Ka nufa."
Ummaru ya ce,"To ai hikenan mu je in Dan taka ma ku. "
Jidda ta galla mi shi harara, "To bayan ma ko rikye ma ta hannu ba kayi ba wannan ai kauyancine."
Ta yo gabansu ta daga hannun Lantana da na Ummaru ta hada ta na, "Yauwa kunga yanzu kowa ya ganku ya San amarene."
Sai da suka isa kofar skul din kan Ummaru ya jiyo da niyar komawa gida.
Da karfi lantana ke magana, "Kar Ka manta da wanke-wanke fa kaji ko."
Ummaru ya ce,"Yanzu ma kuwa Amarya."
Suna shiga ana dukan wa inda suka makara Jidda ta ce, "Lallai Yau in malamin nan ya ta ba ni zai ga masifa."
Indo ta ce, "Allah sarki ita kam lantana Yanzu ba mai dukanta kamar yadda ba a dukan su Sha'awa."