Sashe 13
Matar Police Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
_*Matar Police kirkirarren labarine mai cike da barkwanci, fadakarwa,nishadantarwa tare da sabon salo na mussaman domin farantawa masoya littafaina*_
_*LABARI DA RUBUTAWA*_
_*AISHA MOHAMMED SANI (Xayyeesherthul-humaerath)*_
_LITTAFAN MARUBUCIYAR_
1- _BABU RUWAN SO_
2- _KUCHAKAR KISHIYA_
3- _WASA DA SO_
4- _AZZAWAJUL-MUKADDAR_
5- _JAMEEL (Nafseen)_
6- _KWADAYI 2020_
AND NOW *MATAR POLICE*
_LITTAFINA NA KUDINE INDAI KI NA SON CIGABAN ZA KI TURO KATIN 200 KACAL TA WANNAN NUMBER 08103080717 SANNAN KI YI SCREENSHOT DOMIN TUROMIN DA SHEDAR BIYA_
_*BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM*_
*_FREE PAGE 28/29_*
****************
************
******************
Hajiya Iyatu ana jin tsoro da kyar aka Iya cewa, "Ayya D'ana adan barta ta shirya da kan ta."
KHALEEL ya ce, "To."
Wata irin shegiyar dafaffiyar doguwar Riga Jidda ta sa, ko hijabi babu sai wani fingilin Dan kwali ta fito ta na, "Na gama."
Wata irin tsawa KHALEEL ya ma ta wadda sai da ta ra zana ya ce, "wannan wani irin kaya ne? Dalla jeki cire kuma ki dauko hijabi ba na son iskanci fa."
Murguda mi shi baki ta tsaya yi, "To ai ni sauran kayan sallah na ne."
KHALEEL ya ce, "Kin san Allah ko ki chanja kayan nan ko na baki mamaki ta ke awajen nan."
Komawa daki ta yi ta na un'uni daga karshe sai ga ta fito cikin wata atamfa mai Dan kyau dai-dai gwarwado, Amman ba hijab.
Cikin fushi KHALEEL ya ce, "Ina hijabin?"
Tebe baki Jidda ta yi, "Ni ban da shi."
Kallon Mariya ya yi ya ce, "Ki ba ta Aron hijabi ta sa Dan bazan tafi da mai sufar slinda tsirara ba."
Da sauri Mariya ta dauko ta na, "Amman fa ya mata yawa nasan har kasa zai kai mata ma."
KHALEEL ya karba ya mi ki mata, "Eh tasa hakan."
Fita sukayi KHALEEL na sauri ya shige wajan driving ita ko ta tsaya chak kallonta ya yi sannan ya ce, "Bazaki shiga ba ne ko sai na mammakeki awajen kazamiyar banza da wofi."
Murguda baki ta yi ta ce, "Ni dai ba kazamiya bace kuma ni ban Iya budewa ba."
Tsaki ya yi yana, "Bagidajiya sai rashin kunya Amman ba abin da aka Iya." Fincikarta ya yi ya bude kofar ya na hankadata kamar mai tura kura.
Zama ta yi tana, "Allah ya isan min wallahi, kuma sai na fadawa Babana, mugu kawai."
Kallonta ya yi sannan ya ce, "In baki min shiru ba wallahi yanzu zan Ciro bindiga in harbeki haba yarinya sai ka ce yar Aljanu."
Tunda Jidda ta yi maganar bindiga ta ta gama razana hadda rikye baki ta kasa motsawa, ji tai cikinta ya fara murdawa, sai tusa bumbubum da karfinta ga bala'in wari.
Tsaki KHALEEL ya yi ya na, "Miye haka wannan wani irin iskanci ne da salon kazanta."
Da ya yi kokarin to she hancinsa da hannunsa ya ga dai abin ba da sauri ya nemi waje domin yin parking ya fice ya na rikye ciki,ba iyaka hanci ba, har cikin cikinsa ya Ke jin warin tusar Jidda da ke kokarin galabaitar da shi.
Ita ko Jidda ban da dariya ba abin da take hadda ya rikye ciki.
Ga KHALEEL da kyankyami duk ya bi ya tsargu ban da yawu ba abin da ya ke zubarwa.
Tunawa Yayi da turaren da ke cikin motar da sauri ya koma ya feshe motar da turaren kan ya shiga ya zauna, "Wallahi in kika Kara min tsinanniyar tusarnan sai na jefarki waje, kazamiya kawai ke bazaki Iya cemin zakiyi tusa ba in tsaya ki fita kawai Dan iskanci sai ki min amot....
Ba karasa ba kawai shima sai ga tusa wadda ta fi ta Jidda ma kara illa banbanci da ita ba tai wari ba.
Kyakyallewa da dariya Jidda ta yi ta na, " Wayyo garde ya yi tusa, hhhhhh kai meyasa baka fita ka yi awajen ba? Ai da ka gwada fita mun gani."
Har cikin ranshi ba karamin kunya ya ji ba, Amman ya daure tare da fadin, "Ki min shiru ko na harbeki Wallahi."
Azuciyarsa ya na mai takaici tare da fadin, "Ni dai na hadu da jangwamgwam ko na yi shiru sai tasan yadda ta yi sani yin magana dole Anya wannan yarinya ba Aljana ba ce in ma ko ba aljana bace to tana da aljanu ajikin Amman zan yi maganinta insha Allah."
Suna isa kofar makarantar da sauri ya bude ma ta kofa ya na, "Maza ni ki yi sauri duk adalilinki na makara wajen aiki."
Jidda ta chuno baki ta na, "Eh dai eh dai na ji dadinta ma ni dai ni karamace Amman kai kato da kai kana tusa."
Tsaki ya yi kawai, ya cigaba da tafiya.
Suna shiga office din da ya ke headmastern ya abokin Khalil ne ya ce, "Ah abokina ai na zata ma ka fasa kawotan ne sai gobe."
Khalil ya girgiza kai"Aa dai gata nan ko play class amaka ta Dan zubin kauyece."
Dariya Umar ya yi, "Lallai abokina ba ka da dama kana ganin katuwar budurwa ka ce asata a ajin wasa, ba ma nan ba, ya naga kaman Ku daya ta ma fi kama da kai fiye da Amir da Amira ko daman yan uku ne?"
Tsaki ya yi, "Aa fa ni ka bar hadani da kwailar nan, yar Mamanace."
Karaf Jidda ta ce, "Ni Wallahi na fishi kyau kaf garin mu ma ansan ni kyakkyawace shi da ya ke tu.........
Mari ta ji ya sauka afuskarta , gudun kar ta mai baram barama ya sa shi saurin marinta domin karshen maganar ba ta huce na tusa ba.
Kuka ta fara ta na, " Mugu azzalumi kawai, ni Allah ya isana."
KHALEEL ya ce, "Iyee rashin kunyarki har anan ma ko lallai zanyi maganin...
Bai karasa ba wayarsa ta fara ringing ya na dagawa ya yi saurin dagawa Umar hannu zan tafi kawai ka yi abin da ya dace.
Ko da Umar ya sa aka ma ta interview ya ji matukar mamaki domin ba yadda ake tsammani ba ne, hakan ya sa shi kai ta ajinsu Amir da Amira kawai primary three.
Ko da ya kai ta bancin su Amira ya ajeta ya na, " To Amira ka kawarki nan kuma yar uwarki."
Da sauri Amira ta ce, "Ke ce Jidda ko? Daman Yaya da Mama sun fadamin za akawoki makarantar mu."
Jidda ta ce, "Eh mana Amman yayankin nan mugu ne fa, ni wallahi na tsaneshi ko yanzu ma sai da ya mareni."
Amira ta ce, "Laa Yaya Khalil din? Ni dai ba ruwana."
Malami na shigowa kowa ya mikye ya gaidasa ban da Jidda da ke zaune hankali kwance.
Lekowa ya yi ya na wace gwanarce zauna ba ta shi ba, cikin harshen turanci.
Wata baiwa Jidda na jin duk abinda za afada ma ta da turanci amsa ce dai ba ta Iya ba dawa ba.
Ta yike tasan da ita ya ke cewa ta yi, "Na me Na Jidda I no go tsayawa walle, sabida in Our gari an ce ba kyau."
Tsabar salo na turancin Jidda daga yan ajin har malamin ban da dariya ba abin da suke, daga karshe ma kawai cewa ya yi kowa ya zauna.
Lokacin yin drowing ne ya yi, shi su ke da a time table hakan ya sa Malam Ahmad yin drawing din kuliya, tare da rubutu a kasa THIS IS A CAT.
Bayan ya gama rubutawa Ya ce, "Wacece ko waye zai karanta min? Jidda ta Riga kowa daga hannu, hakan ya sa Uncle Ahmad zabanta ya ce, " Oya Jidda muna saurarenki."
Da karfin ta cike da karfin gwiwa ta ce, "This is a kuliya, mis mis kuliya."
Ilahirin Ajin ba su San sanda suka tsinci kan su da yin dariya ba, Jidda kuwa tsalle ta yi ta na, "Yeee to atafamin mana, mu fa a garin mu ana tafawa."
Uncle Ahmad cikin dariya ya ce, "Oya clap for her."
Tun daga ranar Uncle Ahmad ya ji Jidda ta shiga ranshi komai ta yi kawai birgeshi ta ke.
Ko da aka tashi driver ne ya zo ya dauke su, Amira ta ce, "Jidda ina gidan mu zakije?"
Jidda ta ce, "Aa ni akai ni gidanmu bazani gidanku yayanku mai tusa, yata dukana ko ya harbeni ba. "
Haka kuwa akayi Jidda aka fara kai wa gida kan aka kai su Amira da Amir.
Jidda na shiga gida kuwa ta tarar da Mumy (Hajiya maryam) ta zo suna ta hira da Hajiya Iya.
Mumy ta ce, "Kakata andawo kenan, ya baki bi su Amira da ba, ai da anjima driver ya dawo da ke."
Jidda ta ce, "Ni Um-un bana son gidanki Wannan Yayan dukana ya ke, dazu ma ya min wanka fa tab."
Murmushi Mumy ta yi ta ce, "Ayya Sorry Kakata ki yi shiru kinji ko, in kara dukan ki ni zan rama miki da kai na."
Jidda ta ce, "Yawwa, ni yunwa Nakeji iyatu abincina, wayyo cikina."
Mumy ta ce, "Je ki gun Antynki Mariya ki karbo abincin ina jin ai ta kammala."
Da gudu Jidda ta shige kicin , "Anty Mariya Yunwa na ke ji mai aka dafa."
Mariya ta ce, "Taliyace ga tanan in zuba mi ki ne?"
Nan ta ke ba magana Jidda ta baje a kicin din kasa ta fara kuka, "Wallahi bazan ci taliyar ba, ni tuwo zanci ni innaci taliyar zukyemin jini ta ke, wayyo Allah na."
Da sauri Iya da Mumy su ka nufi kicin ba shiri, hatta Mama da ke daki ma sai da ta fito, sun zata wani Abu ne ya same ta.
Suna shiga Mariya ta ce, "wai ba za ta ci taliyar ba."
Iya ta fara surfen masifa, "Ai daman wannan salon mugunta ne kawai ace safe taliya rana taliya taya abinci zai zauna acikin mutum to Wallahi tun wuri adafa ma ta tuwo yanzun nan ko kuma ni na shiga kicin din in dafa."
Da sauri Mama ta shige ta na, "Bara in daura Mariya ki min jajjjage."
Jidda kuwa tashi ta yi ta fice waje abinta.
Ta na fita ta ga yaron makota na wasa ta ce, "Kai zonan."
Yaron ya zo da akalla bai zarce shekara biyu ba.
Ta ce, "Mamanka ta ma wanka kuwa ?
Ya ce, " Aa."
_*LABARI DA RUBUTAWA*_
_*AISHA MOHAMMED SANI (Xayyeesherthul-humaerath)*_
_LITTAFAN MARUBUCIYAR_
1- _BABU RUWAN SO_
2- _KUCHAKAR KISHIYA_
3- _WASA DA SO_
4- _AZZAWAJUL-MUKADDAR_
5- _JAMEEL (Nafseen)_
6- _KWADAYI 2020_
AND NOW *MATAR POLICE*
_LITTAFINA NA KUDINE INDAI KI NA SON CIGABAN ZA KI TURO KATIN 200 KACAL TA WANNAN NUMBER 08103080717 SANNAN KI YI SCREENSHOT DOMIN TUROMIN DA SHEDAR BIYA_
_*BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM*_
*_FREE PAGE 28/29_*
****************
************
******************
Hajiya Iyatu ana jin tsoro da kyar aka Iya cewa, "Ayya D'ana adan barta ta shirya da kan ta."
KHALEEL ya ce, "To."
Wata irin shegiyar dafaffiyar doguwar Riga Jidda ta sa, ko hijabi babu sai wani fingilin Dan kwali ta fito ta na, "Na gama."
Wata irin tsawa KHALEEL ya ma ta wadda sai da ta ra zana ya ce, "wannan wani irin kaya ne? Dalla jeki cire kuma ki dauko hijabi ba na son iskanci fa."
Murguda mi shi baki ta tsaya yi, "To ai ni sauran kayan sallah na ne."
KHALEEL ya ce, "Kin san Allah ko ki chanja kayan nan ko na baki mamaki ta ke awajen nan."
Komawa daki ta yi ta na un'uni daga karshe sai ga ta fito cikin wata atamfa mai Dan kyau dai-dai gwarwado, Amman ba hijab.
Cikin fushi KHALEEL ya ce, "Ina hijabin?"
Tebe baki Jidda ta yi, "Ni ban da shi."
Kallon Mariya ya yi ya ce, "Ki ba ta Aron hijabi ta sa Dan bazan tafi da mai sufar slinda tsirara ba."
Da sauri Mariya ta dauko ta na, "Amman fa ya mata yawa nasan har kasa zai kai mata ma."
KHALEEL ya karba ya mi ki mata, "Eh tasa hakan."
Fita sukayi KHALEEL na sauri ya shige wajan driving ita ko ta tsaya chak kallonta ya yi sannan ya ce, "Bazaki shiga ba ne ko sai na mammakeki awajen kazamiyar banza da wofi."
Murguda baki ta yi ta ce, "Ni dai ba kazamiya bace kuma ni ban Iya budewa ba."
Tsaki ya yi yana, "Bagidajiya sai rashin kunya Amman ba abin da aka Iya." Fincikarta ya yi ya bude kofar ya na hankadata kamar mai tura kura.
Zama ta yi tana, "Allah ya isan min wallahi, kuma sai na fadawa Babana, mugu kawai."
Kallonta ya yi sannan ya ce, "In baki min shiru ba wallahi yanzu zan Ciro bindiga in harbeki haba yarinya sai ka ce yar Aljanu."
Tunda Jidda ta yi maganar bindiga ta ta gama razana hadda rikye baki ta kasa motsawa, ji tai cikinta ya fara murdawa, sai tusa bumbubum da karfinta ga bala'in wari.
Tsaki KHALEEL ya yi ya na, "Miye haka wannan wani irin iskanci ne da salon kazanta."
Da ya yi kokarin to she hancinsa da hannunsa ya ga dai abin ba da sauri ya nemi waje domin yin parking ya fice ya na rikye ciki,ba iyaka hanci ba, har cikin cikinsa ya Ke jin warin tusar Jidda da ke kokarin galabaitar da shi.
Ita ko Jidda ban da dariya ba abin da take hadda ya rikye ciki.
Ga KHALEEL da kyankyami duk ya bi ya tsargu ban da yawu ba abin da ya ke zubarwa.
Tunawa Yayi da turaren da ke cikin motar da sauri ya koma ya feshe motar da turaren kan ya shiga ya zauna, "Wallahi in kika Kara min tsinanniyar tusarnan sai na jefarki waje, kazamiya kawai ke bazaki Iya cemin zakiyi tusa ba in tsaya ki fita kawai Dan iskanci sai ki min amot....
Ba karasa ba kawai shima sai ga tusa wadda ta fi ta Jidda ma kara illa banbanci da ita ba tai wari ba.
Kyakyallewa da dariya Jidda ta yi ta na, " Wayyo garde ya yi tusa, hhhhhh kai meyasa baka fita ka yi awajen ba? Ai da ka gwada fita mun gani."
Har cikin ranshi ba karamin kunya ya ji ba, Amman ya daure tare da fadin, "Ki min shiru ko na harbeki Wallahi."
Azuciyarsa ya na mai takaici tare da fadin, "Ni dai na hadu da jangwamgwam ko na yi shiru sai tasan yadda ta yi sani yin magana dole Anya wannan yarinya ba Aljana ba ce in ma ko ba aljana bace to tana da aljanu ajikin Amman zan yi maganinta insha Allah."
Suna isa kofar makarantar da sauri ya bude ma ta kofa ya na, "Maza ni ki yi sauri duk adalilinki na makara wajen aiki."
Jidda ta chuno baki ta na, "Eh dai eh dai na ji dadinta ma ni dai ni karamace Amman kai kato da kai kana tusa."
Tsaki ya yi kawai, ya cigaba da tafiya.
Suna shiga office din da ya ke headmastern ya abokin Khalil ne ya ce, "Ah abokina ai na zata ma ka fasa kawotan ne sai gobe."
Khalil ya girgiza kai"Aa dai gata nan ko play class amaka ta Dan zubin kauyece."
Dariya Umar ya yi, "Lallai abokina ba ka da dama kana ganin katuwar budurwa ka ce asata a ajin wasa, ba ma nan ba, ya naga kaman Ku daya ta ma fi kama da kai fiye da Amir da Amira ko daman yan uku ne?"
Tsaki ya yi, "Aa fa ni ka bar hadani da kwailar nan, yar Mamanace."
Karaf Jidda ta ce, "Ni Wallahi na fishi kyau kaf garin mu ma ansan ni kyakkyawace shi da ya ke tu.........
Mari ta ji ya sauka afuskarta , gudun kar ta mai baram barama ya sa shi saurin marinta domin karshen maganar ba ta huce na tusa ba.
Kuka ta fara ta na, " Mugu azzalumi kawai, ni Allah ya isana."
KHALEEL ya ce, "Iyee rashin kunyarki har anan ma ko lallai zanyi maganin...
Bai karasa ba wayarsa ta fara ringing ya na dagawa ya yi saurin dagawa Umar hannu zan tafi kawai ka yi abin da ya dace.
Ko da Umar ya sa aka ma ta interview ya ji matukar mamaki domin ba yadda ake tsammani ba ne, hakan ya sa shi kai ta ajinsu Amir da Amira kawai primary three.
Ko da ya kai ta bancin su Amira ya ajeta ya na, " To Amira ka kawarki nan kuma yar uwarki."
Da sauri Amira ta ce, "Ke ce Jidda ko? Daman Yaya da Mama sun fadamin za akawoki makarantar mu."
Jidda ta ce, "Eh mana Amman yayankin nan mugu ne fa, ni wallahi na tsaneshi ko yanzu ma sai da ya mareni."
Amira ta ce, "Laa Yaya Khalil din? Ni dai ba ruwana."
Malami na shigowa kowa ya mikye ya gaidasa ban da Jidda da ke zaune hankali kwance.
Lekowa ya yi ya na wace gwanarce zauna ba ta shi ba, cikin harshen turanci.
Wata baiwa Jidda na jin duk abinda za afada ma ta da turanci amsa ce dai ba ta Iya ba dawa ba.
Ta yike tasan da ita ya ke cewa ta yi, "Na me Na Jidda I no go tsayawa walle, sabida in Our gari an ce ba kyau."
Tsabar salo na turancin Jidda daga yan ajin har malamin ban da dariya ba abin da suke, daga karshe ma kawai cewa ya yi kowa ya zauna.
Lokacin yin drowing ne ya yi, shi su ke da a time table hakan ya sa Malam Ahmad yin drawing din kuliya, tare da rubutu a kasa THIS IS A CAT.
Bayan ya gama rubutawa Ya ce, "Wacece ko waye zai karanta min? Jidda ta Riga kowa daga hannu, hakan ya sa Uncle Ahmad zabanta ya ce, " Oya Jidda muna saurarenki."
Da karfin ta cike da karfin gwiwa ta ce, "This is a kuliya, mis mis kuliya."
Ilahirin Ajin ba su San sanda suka tsinci kan su da yin dariya ba, Jidda kuwa tsalle ta yi ta na, "Yeee to atafamin mana, mu fa a garin mu ana tafawa."
Uncle Ahmad cikin dariya ya ce, "Oya clap for her."
Tun daga ranar Uncle Ahmad ya ji Jidda ta shiga ranshi komai ta yi kawai birgeshi ta ke.
Ko da aka tashi driver ne ya zo ya dauke su, Amira ta ce, "Jidda ina gidan mu zakije?"
Jidda ta ce, "Aa ni akai ni gidanmu bazani gidanku yayanku mai tusa, yata dukana ko ya harbeni ba. "
Haka kuwa akayi Jidda aka fara kai wa gida kan aka kai su Amira da Amir.
Jidda na shiga gida kuwa ta tarar da Mumy (Hajiya maryam) ta zo suna ta hira da Hajiya Iya.
Mumy ta ce, "Kakata andawo kenan, ya baki bi su Amira da ba, ai da anjima driver ya dawo da ke."
Jidda ta ce, "Ni Um-un bana son gidanki Wannan Yayan dukana ya ke, dazu ma ya min wanka fa tab."
Murmushi Mumy ta yi ta ce, "Ayya Sorry Kakata ki yi shiru kinji ko, in kara dukan ki ni zan rama miki da kai na."
Jidda ta ce, "Yawwa, ni yunwa Nakeji iyatu abincina, wayyo cikina."
Mumy ta ce, "Je ki gun Antynki Mariya ki karbo abincin ina jin ai ta kammala."
Da gudu Jidda ta shige kicin , "Anty Mariya Yunwa na ke ji mai aka dafa."
Mariya ta ce, "Taliyace ga tanan in zuba mi ki ne?"
Nan ta ke ba magana Jidda ta baje a kicin din kasa ta fara kuka, "Wallahi bazan ci taliyar ba, ni tuwo zanci ni innaci taliyar zukyemin jini ta ke, wayyo Allah na."
Da sauri Iya da Mumy su ka nufi kicin ba shiri, hatta Mama da ke daki ma sai da ta fito, sun zata wani Abu ne ya same ta.
Suna shiga Mariya ta ce, "wai ba za ta ci taliyar ba."
Iya ta fara surfen masifa, "Ai daman wannan salon mugunta ne kawai ace safe taliya rana taliya taya abinci zai zauna acikin mutum to Wallahi tun wuri adafa ma ta tuwo yanzun nan ko kuma ni na shiga kicin din in dafa."
Da sauri Mama ta shige ta na, "Bara in daura Mariya ki min jajjjage."
Jidda kuwa tashi ta yi ta fice waje abinta.
Ta na fita ta ga yaron makota na wasa ta ce, "Kai zonan."
Yaron ya zo da akalla bai zarce shekara biyu ba.
Ta ce, "Mamanka ta ma wanka kuwa ?
Ya ce, " Aa."