Sashe 17
Matar Police Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mama ta yi Murmushi kan ta ce, "Mamana sun tafi kenan ba za su dawo ba, nima zan bi su, ki yafemin kinji, nima na yafe mi ki, ki rage tsokana kinji, ki zama yar kirki jiddana."
Jidda na kuka ta ce, "Dan Allah Mama ke ma kirki tafi ki tsaya, mamana ki tsaya Dan Allah."
Mama ta ce, "Yayanki Hamza da Mummy na nan har ma da Yayanki KHALEEL, ina son ki Jidda."
Kuka kawai Jidda ta ke ta ma rasa abin fadi.
Mama ta fara salati nan da nan Allah ya dauki ranta, dai dai lokacin Da mumy ta shigo kenan.
Kuka kawai daga Mumy har jiddan su ke, sai da Khalil da Hamza su ka zo suka fara rarrashinsu.
Jidda ta fita ahaiyacinta gaba daya har akayi ukun su mama da Baba.
Mumy ce ta dauketa ta dawo da ita gidanta, shi kuwa hamza ma ya koma makaranta.
Uncle kuma ya na nan ya na surkullen da zai yi ganin cewa an ba shi Jidda ya aura domin ya yi alwashin ba zai tashi abanza ba, batare da yaci gadon Alhaji Ibrahim ba.
Jidda ta ma daina magana kwata-kwata arayuwarta sai ciwo da ta ke faman yi ko makaranta ba ta samun damar zuwa , abincin ma da ta ke kururuwar ci ba dama bata ma son ga ni bare ta ci.
Zaune ta ke ta kifa kan ta akan kafafuwanta karaf sai ga sallama sak irin muryan Babanta.
Nan ta ke Jidda ta, tashi taje ta rugumeshi ta na kuka.
Mumy da Dady na fitowa....
Urs Xayyeesherth
[11/28, 11:50 PM] Xayyeesherthul-humaerath🥰: °°°°°° _*MATAR POLICE*_ °°°°°°
29November 2020
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*🤝
__________________________________________________________
_We Are Here To Educate,Motivate, And Entertain Our Readers._
__________________________________________________________
_*Matar Police kirkirarren labarine mai cike da barkwanci, fadakarwa,nishadantarwa tare da sabon salo na mussaman domin farantawa masoya littafaina*_
_*LABARI DA RUBUTAWA*_
_*AISHA MOHAMMED SANI (Xayyeesherthul-humaerath)*_
_LITTAFAN MARUBUCIYAR_
1- _BABU RUWAN SO_
2- _KUCHAKAR KISHIYA_
3- _WASA DA SO_
4- _AZZAWAJUL-MUKADDAR_
5- _JAMEEL (Nafseen)_
6- _KWADAYI 2020_
AND NOW *MATAR POLICE*
_LITTAFINA NA KUDINE INDAI KI NA SON CIGABAN ZA KI TURO KATIN 200 KACAL TA WANNAN NUMBER 08103080717 SANNAN KI YI SCREENSHOT DOMIN TUROMIN DA SHEDAR BIYA_
_*BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM*_
*_FREE PAGE 36/37_*
****************
************
******************
Suka tarar da Alhaji Adamu ne, Dan Uwan Alhaji Ibrahim da mu kai bayaninsa abaya.
Dady ya ce, "Alhaji kai ne agidan na mu?"
Alhaji Adamu ya washe baki, "Eh Wallahi ni ne, zuwa ya kamani, banji rasuwar ta su ba ai sai jiya cikin dare, hakan ya sani gaggawan zuwa."
Dady ya ce, "Ayya kai ya yi zafi Wallahi, shiyasa ma ni kai na ban sami damar kirinka ba, ga wajen zama nan bismillahi."
Alhaji Adamu ya zauna tare da kakako hawayen gulma, "Allah sarki Jidda, Yanzu saura min ke kadai sai Hamza adangina, ba Hajiyarmu, ba Ibrahim da iyalinsa, wannan lamari ya matukar tadamin hankali."
Dady ya zauna kusa da shi ya na fadin, "haka Allah ya tsara lamarinsa Wanda ba Wanda ya isa ya kauce ma sa, Abu daya yanzu kawai suke bukata daga garemu Addu'a."
Alhaji Adamu na face hancin ya na, "Hakane kam shiyasa na zo in tafi da diyata ko da ta dinga dibemin kewa ta zauna Chan cikin yan uwanta, ina ganin hakan zai fi, shima hamzan zan biya ta makarantarsu in sanar da shi komai ake ciki, daman munyi alkawarin aurawa ya'yanmu Juna, kuma Alhamdulillah ga Jidda nan insha Allah sai mun cikawa Hajiya Iyah burinta, zan tafi da Jidda in aura ma ta yayanta Sulaiman."
Tun da Alhaji Adamu ya fara jawabi ya zo gabar Dauke Jidda nan da nan gaban Momy ya fadi, domin har ga Allah ta San cewa ba abin da Alhaji Adamu ya shirya illa mugunta da son rai.
Dady ya ce, "To Ina ganin ai anzama daya, bai kamata ka raba mu da Jidda ba a yanzu tunda ga Yayar mahaifiyarta, da kuma Yayanta ina ganin ai ba matsala, maganar aure kuma ai kana da iko a kanta ko da ma ba Dan ka bane ka isa ka badata bare danka to Amman aganina Jidda tai yarinta da aure a yanzu kam dai, yakamata ace ka bari ta Dan kara tasowa yanzu fa take cikin shekara ta Tara, to me za aurar, ita ba girman jiki ba, bare ace."
Sai da Alhaji Adamu ya numfasa kan ya ce, "Alhamdulillah naji dadi ka ce inada iko da ita, Dan haka ba fa zan barta ba, sannan ba fa zan bar maganar auren nan ba."
Tsabar takaici Mumy batasan sanda hawaye ya fara zubowa daga idanuwanta ba.
Dady ya kalleta sannan ya kau da kai izuwa duban Alhaji Adamu ya ce, "Alhaji Dan Allah ka tsaya mu yi magana ta fahimta, ina ganin bai kamata ace wannan maganar har ta zama Babba ba, ka dubi yar uwar mahaifiyar ta mana, kaga irin halin da ta shiga, da zaka taimaka da ka bar mana Jidda har lokacin da zakai ma ta auren."
Tashi Alhaji Adamu ya yi, yana kwallawa Jidda kira,"Ke Jidda ina kike fito za mu tafi, inna biye ta mutanen nan zasu batamin lokaci. "
Mumy ce ta durkusa gareshi ta na, "Dan Allah Alhaji kar ka min haka, wallahi ina yiwa Jidda So fiye da 'ya'yan da na Haifa domin ita din tamkar yar uwata daya tilo da na rasa ne Dan Allah karka rabani da ita."
Fitowa Jidda ta yi da gudu Alhaji ya rikye mata hannu tare da tsaki ya ja ta suka bar gidan.
Ahanyar fitansu su kai kicibis da KHALEEL ya na shigowa.
Abin ya bawa KHALEEL mamaki Amman ya basar, Jidda ce ta kalli Khaleel tare da yi mi shi gwalo.
Kallonta ya yi, ya yi tsaki tare da kau da kai, kan ya nufi cikin gidan.
KHALEEL na shiga ya tarar da Mumy na kuka Dady sai faman ba ta hakuri ya ke.
Karasawa ya yi yana, "Lafiya dai kuwa?"
Mumy ta ce, "KHALEEL sun rabani da Jidda Dan Allah ka kar bomin ita, wallahi jinta na ke tamkar yar uwata."
KHALEEL ya ce, "Haba Mumy akan wannan yarinyar zaki tada hankalinki? To miye ma yata tafiyan da ita ai sai me, mu daman ba nema mu ke ba, ni wallahi daman ma na tasan....
Cikin tsawa Mumy ta dakatar da shi, "ba ita ka tsana ba ni ka tsana, domin duk abin da kayiwa Jidda kamar kaiwa Amir da Amira, Yanzu yarinyar nan abar tausayice ba abin da take bukata fiye da taimako, wannan mutum ban da son duniya ba abin da ya sa agaba, ni nasan ba Dan Allah ya ke son komawar Jidda da hamza garesa ba, dukiyarsu kawai ya ke so, ni dama ace dukiyar zai ci kadai da sauki in zai bar ma na su, Amman ni nasani cewa Jidda wahala zata sha itace abar tausayi, domin ni nasan ya tsaneta, sanadiyarta su ka fara samun matsala da Hajiya Iyah."
KHALEEL ya yi shiru ya ma rasa abin fadi.
Dady ya ce, "ni ban damu da maganar Hamza ba daman maganar Jidda ne ya dameni kuma ma na aure Yanzu, ki jibeta yar karamar yarinya kawai abata ma yarinya karama rayuwa."
Mumy ta ce, "Hmm kai ma ka Fada dai, Yanzu yazama dole mu nemo mafitar da zamu bi domin taimakon yarinyar nan karta Fada Ga mummunan yanayin da ke bibiyarta."
Dady ya ce, "Wannan ya zama dole in sha Allah zan yi iyaka bakin kokarina."
************Alhaji Adamu Ba inda ya nufi Da Jidda sai cikin garin Katsina inda iyalansa su ke da zama.
Tunda daga shiga cikin gidan Jidda ta fara fuskantar sabuwar rayuwa, mai cike da al'ajabi tare kaddara.
MATAR gidan ce zaune wadda ake yiwa lakabi da Ammie ta taso ta yiwa Jidda wani mummanan kallo tare da fadin, "Alhamdulillah ,Allah dai ya yi wai kishiyar Tsohuwa ta haihu."
Alhaji Adamu ya kyalkyale da dariya, "Ai fa kam lamari ya tabbata ko ince ya kusa, domin wannan shine farko."
Karewa jidda kallo tai sama da katsa tai tsaki tare da fadin, "Ke Fatima, zo ki dau yar shilar nan Ku bata abinci ta ci, sannan ta na gamawa daman washing machine din mu ya sami matsala ki Ciro ma ta wankin nan ta yi."
Fatima ta ce to tare da kallon Jidda da harara ta ce, "Mu je."
Sai da Ammie ta lekya tare da tabbatar wa su Jidda sun shige cikin kan ta fara magana kasa-kasa, "Fatan dai ka kwamuso mana dukiyar?"
Dariya ya yi yana, "Ke kin cika azarzababi walle, yaushe Yanzu zan fara maganar kudi, ke baki San komai kan tsari ake ba ne? So na ke sai na Aurawa waccer matsiyaciyar yarinyar sulaiman, shi kuma hamza yadawo kan afara maganar dukiya, in ba haka ba ina farawa yanzu ai za su gano mu, su fahimci inda mu ka dosa, Yanzu ma ba ki San yadda na sha fama da mutanen nan ba ne Wallahi."
Ammie tayi shewa ta ce, "hihi na dai kusa zama Hajiyar gaske, Wallahi ni har ma na zaku ayi ayi aure."
"Ke dai kiyi shiru kawai akan maganar auren nan ma sai da na ya fito karyar cewa munyi alkawarin aura wa ya'yanmu juna, ni dama na tsani yarinyar da ta sa Iyah ta fita sabgata ni mai zai kani gareta in ba kaddara ba, hmm Wallahi ana samun kudin nan sakesu zamuyi subi duniya, Chan ta matse ma su, daga ita har Dan uwan na ta ba damuwata ba ne."
Cewar Alhaji Adamu.
Ammie ta ce, "Ai fa kam shiyasa tun yau ma zata fara aikatuwa, kaga ma bara na shiga daga ciki in taci abinci Yanzu zata fara duty."
Dariyar mugunta Alhaji ya yi ya na, "Hajiya ba ki da dama."
Ta na shiga ciki ta tarar da Jidda ta yi tsili-tsilli da ido ta ci abinci bai isheta ba tana Neman kari Amman tsoro ya ha na ta magana.
Tsawa ta ma ta ta na, "Ke nan gidan fa ba na lalaci ba ne, na Fada miki, kima daina wani zare min ido, Inda cen kin saba iskanci agidan Ku to nan ba zan dauka ba, Dan haka maza tashi kije ki wanke min kayan nan tas, kuma ba na son ganin datti ko kadan ajiki."
Jidda na kuka ta ce, "Dan Allah Mama ke ma kirki tafi ki tsaya, mamana ki tsaya Dan Allah."
Mama ta ce, "Yayanki Hamza da Mummy na nan har ma da Yayanki KHALEEL, ina son ki Jidda."
Kuka kawai Jidda ta ke ta ma rasa abin fadi.
Mama ta fara salati nan da nan Allah ya dauki ranta, dai dai lokacin Da mumy ta shigo kenan.
Kuka kawai daga Mumy har jiddan su ke, sai da Khalil da Hamza su ka zo suka fara rarrashinsu.
Jidda ta fita ahaiyacinta gaba daya har akayi ukun su mama da Baba.
Mumy ce ta dauketa ta dawo da ita gidanta, shi kuwa hamza ma ya koma makaranta.
Uncle kuma ya na nan ya na surkullen da zai yi ganin cewa an ba shi Jidda ya aura domin ya yi alwashin ba zai tashi abanza ba, batare da yaci gadon Alhaji Ibrahim ba.
Jidda ta ma daina magana kwata-kwata arayuwarta sai ciwo da ta ke faman yi ko makaranta ba ta samun damar zuwa , abincin ma da ta ke kururuwar ci ba dama bata ma son ga ni bare ta ci.
Zaune ta ke ta kifa kan ta akan kafafuwanta karaf sai ga sallama sak irin muryan Babanta.
Nan ta ke Jidda ta, tashi taje ta rugumeshi ta na kuka.
Mumy da Dady na fitowa....
Urs Xayyeesherth
[11/28, 11:50 PM] Xayyeesherthul-humaerath🥰: °°°°°° _*MATAR POLICE*_ °°°°°°
29November 2020
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*🤝
__________________________________________________________
_We Are Here To Educate,Motivate, And Entertain Our Readers._
__________________________________________________________
_*Matar Police kirkirarren labarine mai cike da barkwanci, fadakarwa,nishadantarwa tare da sabon salo na mussaman domin farantawa masoya littafaina*_
_*LABARI DA RUBUTAWA*_
_*AISHA MOHAMMED SANI (Xayyeesherthul-humaerath)*_
_LITTAFAN MARUBUCIYAR_
1- _BABU RUWAN SO_
2- _KUCHAKAR KISHIYA_
3- _WASA DA SO_
4- _AZZAWAJUL-MUKADDAR_
5- _JAMEEL (Nafseen)_
6- _KWADAYI 2020_
AND NOW *MATAR POLICE*
_LITTAFINA NA KUDINE INDAI KI NA SON CIGABAN ZA KI TURO KATIN 200 KACAL TA WANNAN NUMBER 08103080717 SANNAN KI YI SCREENSHOT DOMIN TUROMIN DA SHEDAR BIYA_
_*BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM*_
*_FREE PAGE 36/37_*
****************
************
******************
Suka tarar da Alhaji Adamu ne, Dan Uwan Alhaji Ibrahim da mu kai bayaninsa abaya.
Dady ya ce, "Alhaji kai ne agidan na mu?"
Alhaji Adamu ya washe baki, "Eh Wallahi ni ne, zuwa ya kamani, banji rasuwar ta su ba ai sai jiya cikin dare, hakan ya sani gaggawan zuwa."
Dady ya ce, "Ayya kai ya yi zafi Wallahi, shiyasa ma ni kai na ban sami damar kirinka ba, ga wajen zama nan bismillahi."
Alhaji Adamu ya zauna tare da kakako hawayen gulma, "Allah sarki Jidda, Yanzu saura min ke kadai sai Hamza adangina, ba Hajiyarmu, ba Ibrahim da iyalinsa, wannan lamari ya matukar tadamin hankali."
Dady ya zauna kusa da shi ya na fadin, "haka Allah ya tsara lamarinsa Wanda ba Wanda ya isa ya kauce ma sa, Abu daya yanzu kawai suke bukata daga garemu Addu'a."
Alhaji Adamu na face hancin ya na, "Hakane kam shiyasa na zo in tafi da diyata ko da ta dinga dibemin kewa ta zauna Chan cikin yan uwanta, ina ganin hakan zai fi, shima hamzan zan biya ta makarantarsu in sanar da shi komai ake ciki, daman munyi alkawarin aurawa ya'yanmu Juna, kuma Alhamdulillah ga Jidda nan insha Allah sai mun cikawa Hajiya Iyah burinta, zan tafi da Jidda in aura ma ta yayanta Sulaiman."
Tun da Alhaji Adamu ya fara jawabi ya zo gabar Dauke Jidda nan da nan gaban Momy ya fadi, domin har ga Allah ta San cewa ba abin da Alhaji Adamu ya shirya illa mugunta da son rai.
Dady ya ce, "To Ina ganin ai anzama daya, bai kamata ka raba mu da Jidda ba a yanzu tunda ga Yayar mahaifiyarta, da kuma Yayanta ina ganin ai ba matsala, maganar aure kuma ai kana da iko a kanta ko da ma ba Dan ka bane ka isa ka badata bare danka to Amman aganina Jidda tai yarinta da aure a yanzu kam dai, yakamata ace ka bari ta Dan kara tasowa yanzu fa take cikin shekara ta Tara, to me za aurar, ita ba girman jiki ba, bare ace."
Sai da Alhaji Adamu ya numfasa kan ya ce, "Alhamdulillah naji dadi ka ce inada iko da ita, Dan haka ba fa zan barta ba, sannan ba fa zan bar maganar auren nan ba."
Tsabar takaici Mumy batasan sanda hawaye ya fara zubowa daga idanuwanta ba.
Dady ya kalleta sannan ya kau da kai izuwa duban Alhaji Adamu ya ce, "Alhaji Dan Allah ka tsaya mu yi magana ta fahimta, ina ganin bai kamata ace wannan maganar har ta zama Babba ba, ka dubi yar uwar mahaifiyar ta mana, kaga irin halin da ta shiga, da zaka taimaka da ka bar mana Jidda har lokacin da zakai ma ta auren."
Tashi Alhaji Adamu ya yi, yana kwallawa Jidda kira,"Ke Jidda ina kike fito za mu tafi, inna biye ta mutanen nan zasu batamin lokaci. "
Mumy ce ta durkusa gareshi ta na, "Dan Allah Alhaji kar ka min haka, wallahi ina yiwa Jidda So fiye da 'ya'yan da na Haifa domin ita din tamkar yar uwata daya tilo da na rasa ne Dan Allah karka rabani da ita."
Fitowa Jidda ta yi da gudu Alhaji ya rikye mata hannu tare da tsaki ya ja ta suka bar gidan.
Ahanyar fitansu su kai kicibis da KHALEEL ya na shigowa.
Abin ya bawa KHALEEL mamaki Amman ya basar, Jidda ce ta kalli Khaleel tare da yi mi shi gwalo.
Kallonta ya yi, ya yi tsaki tare da kau da kai, kan ya nufi cikin gidan.
KHALEEL na shiga ya tarar da Mumy na kuka Dady sai faman ba ta hakuri ya ke.
Karasawa ya yi yana, "Lafiya dai kuwa?"
Mumy ta ce, "KHALEEL sun rabani da Jidda Dan Allah ka kar bomin ita, wallahi jinta na ke tamkar yar uwata."
KHALEEL ya ce, "Haba Mumy akan wannan yarinyar zaki tada hankalinki? To miye ma yata tafiyan da ita ai sai me, mu daman ba nema mu ke ba, ni wallahi daman ma na tasan....
Cikin tsawa Mumy ta dakatar da shi, "ba ita ka tsana ba ni ka tsana, domin duk abin da kayiwa Jidda kamar kaiwa Amir da Amira, Yanzu yarinyar nan abar tausayice ba abin da take bukata fiye da taimako, wannan mutum ban da son duniya ba abin da ya sa agaba, ni nasan ba Dan Allah ya ke son komawar Jidda da hamza garesa ba, dukiyarsu kawai ya ke so, ni dama ace dukiyar zai ci kadai da sauki in zai bar ma na su, Amman ni nasani cewa Jidda wahala zata sha itace abar tausayi, domin ni nasan ya tsaneta, sanadiyarta su ka fara samun matsala da Hajiya Iyah."
KHALEEL ya yi shiru ya ma rasa abin fadi.
Dady ya ce, "ni ban damu da maganar Hamza ba daman maganar Jidda ne ya dameni kuma ma na aure Yanzu, ki jibeta yar karamar yarinya kawai abata ma yarinya karama rayuwa."
Mumy ta ce, "Hmm kai ma ka Fada dai, Yanzu yazama dole mu nemo mafitar da zamu bi domin taimakon yarinyar nan karta Fada Ga mummunan yanayin da ke bibiyarta."
Dady ya ce, "Wannan ya zama dole in sha Allah zan yi iyaka bakin kokarina."
************Alhaji Adamu Ba inda ya nufi Da Jidda sai cikin garin Katsina inda iyalansa su ke da zama.
Tunda daga shiga cikin gidan Jidda ta fara fuskantar sabuwar rayuwa, mai cike da al'ajabi tare kaddara.
MATAR gidan ce zaune wadda ake yiwa lakabi da Ammie ta taso ta yiwa Jidda wani mummanan kallo tare da fadin, "Alhamdulillah ,Allah dai ya yi wai kishiyar Tsohuwa ta haihu."
Alhaji Adamu ya kyalkyale da dariya, "Ai fa kam lamari ya tabbata ko ince ya kusa, domin wannan shine farko."
Karewa jidda kallo tai sama da katsa tai tsaki tare da fadin, "Ke Fatima, zo ki dau yar shilar nan Ku bata abinci ta ci, sannan ta na gamawa daman washing machine din mu ya sami matsala ki Ciro ma ta wankin nan ta yi."
Fatima ta ce to tare da kallon Jidda da harara ta ce, "Mu je."
Sai da Ammie ta lekya tare da tabbatar wa su Jidda sun shige cikin kan ta fara magana kasa-kasa, "Fatan dai ka kwamuso mana dukiyar?"
Dariya ya yi yana, "Ke kin cika azarzababi walle, yaushe Yanzu zan fara maganar kudi, ke baki San komai kan tsari ake ba ne? So na ke sai na Aurawa waccer matsiyaciyar yarinyar sulaiman, shi kuma hamza yadawo kan afara maganar dukiya, in ba haka ba ina farawa yanzu ai za su gano mu, su fahimci inda mu ka dosa, Yanzu ma ba ki San yadda na sha fama da mutanen nan ba ne Wallahi."
Ammie tayi shewa ta ce, "hihi na dai kusa zama Hajiyar gaske, Wallahi ni har ma na zaku ayi ayi aure."
"Ke dai kiyi shiru kawai akan maganar auren nan ma sai da na ya fito karyar cewa munyi alkawarin aura wa ya'yanmu juna, ni dama na tsani yarinyar da ta sa Iyah ta fita sabgata ni mai zai kani gareta in ba kaddara ba, hmm Wallahi ana samun kudin nan sakesu zamuyi subi duniya, Chan ta matse ma su, daga ita har Dan uwan na ta ba damuwata ba ne."
Cewar Alhaji Adamu.
Ammie ta ce, "Ai fa kam shiyasa tun yau ma zata fara aikatuwa, kaga ma bara na shiga daga ciki in taci abinci Yanzu zata fara duty."
Dariyar mugunta Alhaji ya yi ya na, "Hajiya ba ki da dama."
Ta na shiga ciki ta tarar da Jidda ta yi tsili-tsilli da ido ta ci abinci bai isheta ba tana Neman kari Amman tsoro ya ha na ta magana.
Tsawa ta ma ta ta na, "Ke nan gidan fa ba na lalaci ba ne, na Fada miki, kima daina wani zare min ido, Inda cen kin saba iskanci agidan Ku to nan ba zan dauka ba, Dan haka maza tashi kije ki wanke min kayan nan tas, kuma ba na son ganin datti ko kadan ajiki."