Sashe 2
Matar Police Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Iya ta yi tsaki ta tashi ta na, "Yo kyaji dashi dai."
Fita tayi tana tsalle tsallenta tare wakar , "Jiddatu Tauraruwar mata nan gani nan bari dumamen mayya, Jiddatu Dompol kon."
Hankalinta kwance ta na ta wakyenta wani yaro ta gani ahanya ya na tallen gyada ta ce, "Kai Mudi zo nan."
Tawowa ya yi gareta.
Daffafiyar gyadace hakan ya sa fara dubawa ta na, "Wannan gyadar ta Ku ma ai duk ruwa-ruwane ka ga ni ba zan siya ba sai na dandana naji ko zan iya ci."
Mudi ya ce, "Eh ki dandana guda biyu."
Zaman dursham Jiddatu ta yi ta janyo mudi ma ya zauna, gyadar ta fara ci ta na to far da yawu, "Kai Wallahi Wannan ruwa-ruwa bara na gwada wa su."
Da haka haka har ta kusan cinyewa.
Abin ka da yaro mai wayo ya ce, "Taf kin fa kusa cinyewa to wallahi ki bani kudina daman na Muttala biyarne kuma kin cinye na muttala uku."
Jiddatu ta mikye ta na gyara jikinta ta ce, "Iye? Ruwa ruwan zan siya wallahi ba zan biya ko ficika ba."
Mudi ya rikyeta kamar zai yi kuka.
Fincike shi ta yi ajikinta ta fara dukanshi ta na, "Ku ji min yaro da rainin wayo ni yaushe naci gyadar da zan biya ka zauna ka cinye abin ka za ka min sharri to Wallahi ba ka isa ba."
Da taga yana kokarin fara rama dukan da gudu ta zura ta na yi mishi gwalo shi ko Mudi kuka kawai ya fara awajen ya tuna irin masifar ta mahaifiyarshi da zai tarar.
Gidan su Indo ta gutsa aguje, Innar Indo ya daka sai da ta hankade ta daga ita har turmin sai ga su akasa, maimakon ta tausayama mata ko ta ce ma ta sannu sai Jiddatu ta bige da dariya ta na, "Wayyo Allah na Ga Innar Indo a kasa, Indo fito kiga innarki tin kan ta tashi."
Rikye ciki tai ta na dariya abinta hankali kwance.
Zura ma ta Ido kawai Innar Indo ta yi ta na, "Allah ya shiryeki Jiddatu ki Yarda ni kuma ki bige da yi min dariya."
Tsuru-tsuru Indo ta yi domin tasan ta na yin dariya innarta ta za fara jibgarta ita ko Jidda tasan ana tabata an taba bala'i.
*****Mudi kuwa gida ya nu fa ya na kuka ya sanar da Mahaifiyarshi Kande masifa ai ko tuni ta fara balbalin masifarta ta ja shi gun mai gari domin tasan ko taje gun Iya sai dai ta gama masifar ta Amman ba abin da za ta iya yiwa Jiddatu.
Mai gari ya sa Mudi ya je ya nuna inda Jiddatu ta yi, ai ko ya nuna gidan su Indo.
Sallama waziri ya yi Baffan Indo ya fito a ka sanar da shi Jiddatu ake bida bai yi mamaki ba domin yasan Jiddatu ba Wanda ta bari a karkararnan.
Jiddatu na jin cewa mai gari na nemanta tasan cewa Kande masifa ce ta kai kararta ba karamin tsorata ta yi ba da ka ganta zakasan cewa a tsorace ta ke jijiyoyin wuyan nan duk awaje, Tuni ta fara fitsari tana tafiya ya na kwarara, Domin Da kyar Baffan Indo ya fito Da ita daga ban daki.
Suna zuwa fada ta fara kuka ta na ni fa sharri ya min na fada ma Ku sharri mudi ya min ni ko cin gyadarshi ma ban yi ba, kuma gyadar ma duk ruwa-ruwa ne, na fada ma Ku Wallahi ban ci ba mai gari ka min rai."
Tsawa mai gari ya ma ta Wanda sai da ya sata kara yin wani fitsarin nan ta ke ya ce, "Hauwa'u waye ne wai bai San halinki ba duk karkarar nan , nasan za ki iya abinda ya fi haka ma akkala in ba akawomin kararki arana sau goma ba to za akawo sau biyar, Amman ina daga miki kafa sabida Kakarki hakan bai miki ba to wallahi yau ba Wanda ya isa ya hanani ladabtar da ke domin rigimarki ta yi yawa kowa akauyen nan bai da matsalar da ta wuce ta ki."
Rawa jikin Jiddatu ya fara.
Mai gari ya sa aka kirawo Mai hukunci da zabgegiyar dorinarsa.
Ganin wannan dorinar ya sa ta tuna wani labari da Iyarta ta taba bata na Karyar Aljanu, sannan kuma ta kara tunawa fa ba abin da mai gari ya tsana fiye da mutuwa.
Faduwa awajen ta yi ta na birgima, " *Diyar mu ce karku taba ma na ita duk wanda ya taba jiddatu ya tabo bala'iiiiii, masifaaaa, jaza'iiiii."*
Mai gari ya yi tsaki kan ya ce, "Wannan ai iskanci ne Sarkin Hukunci hukunta min ita ai ni nawa aljanun ma sun fi karfin na ta."
Jiddatu ta kara kwarara wani ihu da sai da ya ba za ilahirin karkarar ta ce, "Karku tabata in kuna so Ku tsira da rayuwarku, na fada ma Ku karku taba Jiddatu mai gari rayuwarka ta na cikin hatsari kana daf da barin duniya barin Jiddatu tai abin da ta ke so shine kadai zai kawo tsira ga rayuwarka, maigari Wallahi sai mun kashe ka Indai ka taba diyar mu baxamu lamunta ba Daren Yau za ka bar duniya, yuuuui,hiuuiu,woooo, wiii Wallahi sai ka mutu ma kawai."
Sai ga maigari na zufa ya cire rawani tare da saukowa kasa ya na, "Dan Allah Ku yi hakuri Ku bar ni da rayuwata Wallahi ba na son mutuwa ko kadan gashi na zalinci yan karkarar nan ban nemi yafiyarsu ba Dan Allah ku yi hakuri daga yau bazan kara ko kallon hanyar da Diyarku ta bi ba bare in kulata na tuba Ku yafeni."
maigari Hadda guntun hawaye ya na rokon Jiddatu ta barshi da rayuwarshi.
Wata irin dariya ta fara ta fasa ta na fadin, "karaso nan na ce ma ka zo." Cikin tsawa ta ke maganar.
Jiki asanyaye ya karasa gareta kai akasa.
Shafa kan shi ta farayi sannan ta dago da fuskarshi ta na ja mi shi gemu ta ce, "Wuiii wiii Allah ka zaunar da tsohon nan aduniya har sai lokacinsa yayi, Amman da zaran rana daya ya taba mana diyar mu ko da kuwa bata mata rai ya yi ba makawa wannan ce ranar shi ta karshe aduniya."
Jiki na rawa ya ce, "Insha Allah hakan ma ba zai faru ba nidai Dan Allah Ku bar ni da raina."
Kwatsam sai ga Iya burun-bururun sai masifa ta ke ta na fadin, "Wallahi Yau sai in tsinewa maigarin nan, in tsinewa babanshi, in tsinewa kankanshi kai har ma da kakan kakanshi wai mu za agwadawa iskanci atabamin jiki azauna lafiya, to wallahi sai in sallah in roki Allah ya sa adaina ruwa agarinnan na shekara guda."
Da sauri maigari ya isa gareta yana, "Iya Wallahi ba mu mata komai ba mutanenta ne sukazo yanzu ki tayani ba su hakuri."
Kallo Daya Iya ta yiwa Jiddatu tasan cewa wannan iya shegene kawai daya daga cikin Wanda ta ke koya ma ta.
Tsaki ta yi ta na, "Yo ai kai ka ja daman mu har ma za akoya mana iskanci ne ai sai dai mu mukoyar in ka na son zaman lafiya to ka fada wa yan garin nan kaf su fita harkar jikata ko ko nai Addu'ar rashin ruwa."
Daura hannu ya yi akan shi ya na fadin, "Wa innahu sulaimanu wa innahu sulaimanu Ashe dangin Aljanu mu ke tare da su ni kam dai Dan Allah Ku yafemin nadaina daga yau andaina wallahi."
Iya ce ta karasaga Jiddatu ta na tafo ma ta yawo tare da surutan da ita kan ta batasan me ta ke fadi ba.
Jiddatu ta yi wata attishawa ta na fadin, "Dan Allah kar Ku dakeni ni banci ba fa."
_*hhhhhh lallai ma Jiddatu ku ga iya shege tamkar ba ita ba.*_
Iya ta kafta ma ta I do ta na fadin, "Yo ma ba na tsine ma su ba, tashi abinki kinji mu tahi gida."
Suna tafiya mai gari na binsu ya na Jiddatu ta yafe mishi, wayencewa ta yi kamar batasan me ake ba ta ce, "Iya wai menene? Ni fa ba na son ganin tsohon nan kice mi shi ya tafi."
Iya ta ce, "Maigari karkaji komai ai ka tsira tafi kawai tin kan ta birkice."
Da gudu maigari ya bar wajen ya koma fada ya hana haki sai zufa fifita kawai ake yi mishi ya na hamdalal Allah ya taimake shi.
Jiddatu da Iya na shiga gida.......
Urs Xayyeesherth
[11/13, 1:57 PM] Xayyeesherth: °°°°°° _*MATAR POLICE*_ °°°°°°
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*🤝
__________________________________________________________
_We Are Here To Educate,Motivate, And Entertain Our Readers._
__________________________________________________________
_*Matar Police kirkirarren labarine mai cike da barkwanci, fadakarwa,nishadantarwa tare da sabon salo na mussaman domin farantawa masoya littafaina*_
_*LABARI DA RUBUTAWA*_
_*AISHA MOHAMMED SANI (Xayyeesherthul-humaerath)*_
_LITTAFAN MARUBUCIYAR_
1- _BABU RUWAN SO_
2- _KUCHAKAR KISHIYA_
3- _WASA DA SO_
4- _AZZAWAJUL-MUKADDAR_
5- _JAMEEL (Nafseen)_
6- _KWADAYI 2020_
AND NOW *MATAR POLICE*
_LITTAFINA NA KUDINE INDAI KI NA SON CIGABAN ZA KI TURO KATIN 200 KACAL TA WANNAN NUMBER 08103080717 SANNAN KI YI SCREENSHOT DOMIN TUROMIN DA SHEDAR BIYA_
_*BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM*_
*_FREE PAGE 3/4_*
****************
************
******************
Kan su shiga ciki Jidda ta ce, "Ke tsaya in sauka anan, bari kiga yadda za mu na tafiya, kun San ni dai ban son raini, Dan haka dole muna tafiyar yan matan birni, bari kuga Yadda Mamana a birni ta ke tafiya."
Tafiya Jidda ta farayi tana harde kafa kamar agwagwa sai wani rangwada ta ke tana fari da ido abin ka da mutum kamar tsinke ta na tafiyar kaman za ta fadi,
Ta cigaba da fadin, "muna daga daki ni da Iya muna lekyota in fada mu Ku har wani rangode kai ta ke fa."
Indo ta ce, "Ke kan kinji Dadi Mamanki yar birni, Jidda mu ma yaushe za ki kai mu gidanku na birni."
Jidda ta yi tsaki, "Tab ni ai bazan kara zuwa ba, bayan dukana Mama ta ke ga masifa tab Ni ko bikin Anty Mariya ma ban zuwa duk yan gidan fa masifaffu ne."
Lantana ta ce, "ni kam dama nice ai tuntuni zan koma can da zama."
Jidda ta ce, "Ai sai kuyi ta yi ni nan ya fi min dadi, kunga kuzo mu fara tafiyar nan tin kan na manta."
Fita tayi tana tsalle tsallenta tare wakar , "Jiddatu Tauraruwar mata nan gani nan bari dumamen mayya, Jiddatu Dompol kon."
Hankalinta kwance ta na ta wakyenta wani yaro ta gani ahanya ya na tallen gyada ta ce, "Kai Mudi zo nan."
Tawowa ya yi gareta.
Daffafiyar gyadace hakan ya sa fara dubawa ta na, "Wannan gyadar ta Ku ma ai duk ruwa-ruwane ka ga ni ba zan siya ba sai na dandana naji ko zan iya ci."
Mudi ya ce, "Eh ki dandana guda biyu."
Zaman dursham Jiddatu ta yi ta janyo mudi ma ya zauna, gyadar ta fara ci ta na to far da yawu, "Kai Wallahi Wannan ruwa-ruwa bara na gwada wa su."
Da haka haka har ta kusan cinyewa.
Abin ka da yaro mai wayo ya ce, "Taf kin fa kusa cinyewa to wallahi ki bani kudina daman na Muttala biyarne kuma kin cinye na muttala uku."
Jiddatu ta mikye ta na gyara jikinta ta ce, "Iye? Ruwa ruwan zan siya wallahi ba zan biya ko ficika ba."
Mudi ya rikyeta kamar zai yi kuka.
Fincike shi ta yi ajikinta ta fara dukanshi ta na, "Ku ji min yaro da rainin wayo ni yaushe naci gyadar da zan biya ka zauna ka cinye abin ka za ka min sharri to Wallahi ba ka isa ba."
Da taga yana kokarin fara rama dukan da gudu ta zura ta na yi mishi gwalo shi ko Mudi kuka kawai ya fara awajen ya tuna irin masifar ta mahaifiyarshi da zai tarar.
Gidan su Indo ta gutsa aguje, Innar Indo ya daka sai da ta hankade ta daga ita har turmin sai ga su akasa, maimakon ta tausayama mata ko ta ce ma ta sannu sai Jiddatu ta bige da dariya ta na, "Wayyo Allah na Ga Innar Indo a kasa, Indo fito kiga innarki tin kan ta tashi."
Rikye ciki tai ta na dariya abinta hankali kwance.
Zura ma ta Ido kawai Innar Indo ta yi ta na, "Allah ya shiryeki Jiddatu ki Yarda ni kuma ki bige da yi min dariya."
Tsuru-tsuru Indo ta yi domin tasan ta na yin dariya innarta ta za fara jibgarta ita ko Jidda tasan ana tabata an taba bala'i.
*****Mudi kuwa gida ya nu fa ya na kuka ya sanar da Mahaifiyarshi Kande masifa ai ko tuni ta fara balbalin masifarta ta ja shi gun mai gari domin tasan ko taje gun Iya sai dai ta gama masifar ta Amman ba abin da za ta iya yiwa Jiddatu.
Mai gari ya sa Mudi ya je ya nuna inda Jiddatu ta yi, ai ko ya nuna gidan su Indo.
Sallama waziri ya yi Baffan Indo ya fito a ka sanar da shi Jiddatu ake bida bai yi mamaki ba domin yasan Jiddatu ba Wanda ta bari a karkararnan.
Jiddatu na jin cewa mai gari na nemanta tasan cewa Kande masifa ce ta kai kararta ba karamin tsorata ta yi ba da ka ganta zakasan cewa a tsorace ta ke jijiyoyin wuyan nan duk awaje, Tuni ta fara fitsari tana tafiya ya na kwarara, Domin Da kyar Baffan Indo ya fito Da ita daga ban daki.
Suna zuwa fada ta fara kuka ta na ni fa sharri ya min na fada ma Ku sharri mudi ya min ni ko cin gyadarshi ma ban yi ba, kuma gyadar ma duk ruwa-ruwa ne, na fada ma Ku Wallahi ban ci ba mai gari ka min rai."
Tsawa mai gari ya ma ta Wanda sai da ya sata kara yin wani fitsarin nan ta ke ya ce, "Hauwa'u waye ne wai bai San halinki ba duk karkarar nan , nasan za ki iya abinda ya fi haka ma akkala in ba akawomin kararki arana sau goma ba to za akawo sau biyar, Amman ina daga miki kafa sabida Kakarki hakan bai miki ba to wallahi yau ba Wanda ya isa ya hanani ladabtar da ke domin rigimarki ta yi yawa kowa akauyen nan bai da matsalar da ta wuce ta ki."
Rawa jikin Jiddatu ya fara.
Mai gari ya sa aka kirawo Mai hukunci da zabgegiyar dorinarsa.
Ganin wannan dorinar ya sa ta tuna wani labari da Iyarta ta taba bata na Karyar Aljanu, sannan kuma ta kara tunawa fa ba abin da mai gari ya tsana fiye da mutuwa.
Faduwa awajen ta yi ta na birgima, " *Diyar mu ce karku taba ma na ita duk wanda ya taba jiddatu ya tabo bala'iiiiii, masifaaaa, jaza'iiiii."*
Mai gari ya yi tsaki kan ya ce, "Wannan ai iskanci ne Sarkin Hukunci hukunta min ita ai ni nawa aljanun ma sun fi karfin na ta."
Jiddatu ta kara kwarara wani ihu da sai da ya ba za ilahirin karkarar ta ce, "Karku tabata in kuna so Ku tsira da rayuwarku, na fada ma Ku karku taba Jiddatu mai gari rayuwarka ta na cikin hatsari kana daf da barin duniya barin Jiddatu tai abin da ta ke so shine kadai zai kawo tsira ga rayuwarka, maigari Wallahi sai mun kashe ka Indai ka taba diyar mu baxamu lamunta ba Daren Yau za ka bar duniya, yuuuui,hiuuiu,woooo, wiii Wallahi sai ka mutu ma kawai."
Sai ga maigari na zufa ya cire rawani tare da saukowa kasa ya na, "Dan Allah Ku yi hakuri Ku bar ni da rayuwata Wallahi ba na son mutuwa ko kadan gashi na zalinci yan karkarar nan ban nemi yafiyarsu ba Dan Allah ku yi hakuri daga yau bazan kara ko kallon hanyar da Diyarku ta bi ba bare in kulata na tuba Ku yafeni."
maigari Hadda guntun hawaye ya na rokon Jiddatu ta barshi da rayuwarshi.
Wata irin dariya ta fara ta fasa ta na fadin, "karaso nan na ce ma ka zo." Cikin tsawa ta ke maganar.
Jiki asanyaye ya karasa gareta kai akasa.
Shafa kan shi ta farayi sannan ta dago da fuskarshi ta na ja mi shi gemu ta ce, "Wuiii wiii Allah ka zaunar da tsohon nan aduniya har sai lokacinsa yayi, Amman da zaran rana daya ya taba mana diyar mu ko da kuwa bata mata rai ya yi ba makawa wannan ce ranar shi ta karshe aduniya."
Jiki na rawa ya ce, "Insha Allah hakan ma ba zai faru ba nidai Dan Allah Ku bar ni da raina."
Kwatsam sai ga Iya burun-bururun sai masifa ta ke ta na fadin, "Wallahi Yau sai in tsinewa maigarin nan, in tsinewa babanshi, in tsinewa kankanshi kai har ma da kakan kakanshi wai mu za agwadawa iskanci atabamin jiki azauna lafiya, to wallahi sai in sallah in roki Allah ya sa adaina ruwa agarinnan na shekara guda."
Da sauri maigari ya isa gareta yana, "Iya Wallahi ba mu mata komai ba mutanenta ne sukazo yanzu ki tayani ba su hakuri."
Kallo Daya Iya ta yiwa Jiddatu tasan cewa wannan iya shegene kawai daya daga cikin Wanda ta ke koya ma ta.
Tsaki ta yi ta na, "Yo ai kai ka ja daman mu har ma za akoya mana iskanci ne ai sai dai mu mukoyar in ka na son zaman lafiya to ka fada wa yan garin nan kaf su fita harkar jikata ko ko nai Addu'ar rashin ruwa."
Daura hannu ya yi akan shi ya na fadin, "Wa innahu sulaimanu wa innahu sulaimanu Ashe dangin Aljanu mu ke tare da su ni kam dai Dan Allah Ku yafemin nadaina daga yau andaina wallahi."
Iya ce ta karasaga Jiddatu ta na tafo ma ta yawo tare da surutan da ita kan ta batasan me ta ke fadi ba.
Jiddatu ta yi wata attishawa ta na fadin, "Dan Allah kar Ku dakeni ni banci ba fa."
_*hhhhhh lallai ma Jiddatu ku ga iya shege tamkar ba ita ba.*_
Iya ta kafta ma ta I do ta na fadin, "Yo ma ba na tsine ma su ba, tashi abinki kinji mu tahi gida."
Suna tafiya mai gari na binsu ya na Jiddatu ta yafe mishi, wayencewa ta yi kamar batasan me ake ba ta ce, "Iya wai menene? Ni fa ba na son ganin tsohon nan kice mi shi ya tafi."
Iya ta ce, "Maigari karkaji komai ai ka tsira tafi kawai tin kan ta birkice."
Da gudu maigari ya bar wajen ya koma fada ya hana haki sai zufa fifita kawai ake yi mishi ya na hamdalal Allah ya taimake shi.
Jiddatu da Iya na shiga gida.......
Urs Xayyeesherth
[11/13, 1:57 PM] Xayyeesherth: °°°°°° _*MATAR POLICE*_ °°°°°°
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*🤝
__________________________________________________________
_We Are Here To Educate,Motivate, And Entertain Our Readers._
__________________________________________________________
_*Matar Police kirkirarren labarine mai cike da barkwanci, fadakarwa,nishadantarwa tare da sabon salo na mussaman domin farantawa masoya littafaina*_
_*LABARI DA RUBUTAWA*_
_*AISHA MOHAMMED SANI (Xayyeesherthul-humaerath)*_
_LITTAFAN MARUBUCIYAR_
1- _BABU RUWAN SO_
2- _KUCHAKAR KISHIYA_
3- _WASA DA SO_
4- _AZZAWAJUL-MUKADDAR_
5- _JAMEEL (Nafseen)_
6- _KWADAYI 2020_
AND NOW *MATAR POLICE*
_LITTAFINA NA KUDINE INDAI KI NA SON CIGABAN ZA KI TURO KATIN 200 KACAL TA WANNAN NUMBER 08103080717 SANNAN KI YI SCREENSHOT DOMIN TUROMIN DA SHEDAR BIYA_
_*BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHIM*_
*_FREE PAGE 3/4_*
****************
************
******************
Kan su shiga ciki Jidda ta ce, "Ke tsaya in sauka anan, bari kiga yadda za mu na tafiya, kun San ni dai ban son raini, Dan haka dole muna tafiyar yan matan birni, bari kuga Yadda Mamana a birni ta ke tafiya."
Tafiya Jidda ta farayi tana harde kafa kamar agwagwa sai wani rangwada ta ke tana fari da ido abin ka da mutum kamar tsinke ta na tafiyar kaman za ta fadi,
Ta cigaba da fadin, "muna daga daki ni da Iya muna lekyota in fada mu Ku har wani rangode kai ta ke fa."
Indo ta ce, "Ke kan kinji Dadi Mamanki yar birni, Jidda mu ma yaushe za ki kai mu gidanku na birni."
Jidda ta yi tsaki, "Tab ni ai bazan kara zuwa ba, bayan dukana Mama ta ke ga masifa tab Ni ko bikin Anty Mariya ma ban zuwa duk yan gidan fa masifaffu ne."
Lantana ta ce, "ni kam dama nice ai tuntuni zan koma can da zama."
Jidda ta ce, "Ai sai kuyi ta yi ni nan ya fi min dadi, kunga kuzo mu fara tafiyar nan tin kan na manta."