Sashe 5
Kaifi Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"ok to shikenan dama nace bari inzo in duba ka..." daga haka mommy din ta juya ta fita taja masa ƙofa, kashe wayar sa yayi saboda damunsa da yaya Aliyu keta faman yi da kira, bai kunna wayar tashi ba sai bayan magrib nan ya kula da sakon da Aliyun ya turo masa tun da safe bayan ya baro office din anty Mimi, kudine har 5m, dafe kansa yayi wanda yaji ya sara masa,
"shi kuma wannan kudin duk na menene?" ya tambayi kansa hankalinsa na sake dugunzuma, gaskiya Aliyu ya takurawa rayuwarsa haka kuma ya na neman hana shi sukuni, yayin da shi kuma Aliyun ke can yana ji acikin ransa da kuma jikinsa cewa Afeef din shine kadai zai iya yi masa abinda ya dace dan Mimi bata wasa dashi shima kuma baida lokacinta dan haka ya san baza asamu matsala ba komai zai tafi yadda ya dace kuma ya shirya ba tare da wata tangarda ba.
Tsawon kwanaki biyu shi dai Afeef ya kasa gane kansa ma dan ya rasa yaya zai yi da matsalar yaya Aliyu da anty Mimi, kullum cikin takura masa da kira Aliyun yake har hakan yasa yaki zuwa family house dan bama ya son su hadu acan, kwana yake yana sake sake cikin ransa dan ya rasa a inda mafita take. Yau ya jima yana bacci kamar yadda ya saba dan kwana biyu baya samun bacci sosai, sai after 1 sannan ya tashi, wayar shi ya dauka ya kunna yana kunnawa massages din Aliyu suka yi ta shigowa duk na roko ne da magiyar ya taimaka musu ya ceto rayuwar su shi da Mimi saboda idan bai taimake su ba komai zai iya faruwa, bai kai ga karanta massages dinba gaba daya kiran Aliyu ya shigo, dauka yayi a hankali yace,
"hello yaya haidar.....nima yanzu nake cewa zan kiraka fa sai gashi ka kirani"
"A'a Afeef wannan ba gaskiya bane.... Kwana nawa wayarka a kashe"
Murmushi yayi tare da cewa "ehh wallahi yaya..... Dama zan kira ne in fada maka na amince sannan dan Allah wannan kudin da ka turo min zan dawo maka dashi ai ba sai ka biyani ba akan wannan..... We are one family...."
"No Afeef ka barshi ka dauka kawai wata yar karamar kyauta ce daga yaya zuwa kaninsa...."
"A'a yaya wallahi ba zan karɓa ba indai har kana son inyi maka abinda kake bukata.... Bana son inji araina kudi ka biyani dan yi maka wani abu wanda zan iya yi maka koda baka biyani ba saboda karfin zumuncin dake tsakaninmu...."
"to shikenan Afeef na gode Allah ya bar zumunci, yanzu ya za ayi?"
"babu matsala yaya komai zai tafi daidai insha Allah..... But ka jawa anty Mimi kunne Allah karta yarda ta sake ce min jariri...." dariya Aliyu yayi yace,
"insha Allah, gata nan ma tana jinka ai ina office dinta...."
Katse wayar yayi sannan ya tashi ya fita zuwa part din mommy.
Kallon Mimi Aliyu yayi bayan sun gama waya da Afeef, ajiyar zuciya ya sauke jin Afeef din ya amince da kyar,
"ban tsammaci yaron nan zai amince ba.... Kawai na yi tunanin sai dai mu nemi wani..."
Shuru yaji tayi bata amsa ba saboda bata san me zata ce ba ko me zata kira wannan abun ba, ance dai auren kisan wuta to amma a rasa da wa zasu yi auren kisan wuta sai da Afeef?
" My love baki ce komai ba.... You didn't say anything.... "
" to wai me zance Aliyu? Yanzu a rasa da wanda zamuyi auren kisan wuta sai da Afeef?"
"calm down my love.... Shifa RUWAN KASHE GOBARA ba sai mai kyau ba.... Bukatar mu in dai zata biya bamu da damuwar koma waye shi.... Kiyi hakuri..... Kar wannan ya dameki...."
"Ai duk Kaine ka janyo...... Ka rinka abu kamar wani mai shaye shaye ko tabin hankali yanzu ga abinda ka janyo mana nan.... Zaka sa inyi auren kisan wuta da kanin bayana...." daga haka ta dauki wasu files ta fita ta barshi cikin office din, babu abinda yake bata mata rai irin yanda idan ta tuna cewa Afeef ne zai zame mata mijin auren kisan wuta wannan wacce irin lalacewa ce, sai dai amma idan kuma ta tuna da cewa auren na ɗan wucin gadi ne zasu koma su hade da yaya Aliyu sai ta ɗan ji sanyi cikin ranta dan tana mutukar sonsa da kaunarsa haka kuma tana ta faman missing dinshi kamar yadda kullum shima yake yi mata korafin cikin missing dinta yake, to da su cigaba da wannan zaman lalurar wanda shaidan zai iya cin nasara a kansu gara asamu a ganganɗa da Afeef din har bukata ta biya.......
Hmmmmm masu karatu wannan cakwakiya ta ɗaure min kai, please comment what you think.....
Next chapter loading✍🏻
KAIFI ƊAYA... ✨
*When the world called her “useless”… he called her “mine.”*💘
_KAIFI ƊAYA_ is not just a love story. It’s the story of Mimi - a doctor whose name was dragged through scandal, whose body was broken by fate… 💔
And Afeef - the man who chose to stay when everyone told him to leave. 😥
They won the fight against the world.
But can they win the fight for each other, when silence is louder than lies, and love is tested by things neither of them chose? 🥺
*One blade. One choice. One love that refuses to break.*❤️
_Kaifi Daya_ - because true love doesn’t walk away when you can’t walk anymore..😥
It's available now 07044644433
Your heart will not be the same after the last page🥰✍🏻✍🏻
#Kaifi ɗaya#
#lovetriangle
#EmotionalRomance
#DrMimiAndAfeef
_*Ummi Shatu*_👌🏻
[7/18, 8:56 AM] Oum Jasrah: https://www.arewapen.com/book?id=6a50f2f571e75baab6622006
KAIFI ƊAYA....
_A story of scandal, sacrifice and a love that refused to break, a love that says am still here._
NA
UMMI A'ISHA
4
***Cike da kasala da damuwar da yake ta boyewa cikin ranshi ya shiga part din mommy, babu kowa cikin part din kamar yadda gidan ya saba kasancewa dan ita Manal ta tafi makaranta ita kuma mommy ta fita aikinta kamar yadda ta saba, table a shirye shiyasa kawai zama yayi ya fara zuba breakfast din da yaga mommy ta ajiye masa, yana cin abincin yana tunani cikin ransa yanzu ta ina ya dace ya fara sannan wa ya kamata ya tunkara da wannan maganar ta yana son a daura musu aure da anty Mimi?
Har ya gama breakfast din bai tsayar da magana guda daya a cikin ransa ba kawai ya san ayau dole sai ya magantu ko ayi ko a ƙi yi, fata yaji yana yi acikin ransa ma Allah yasa iyayen nasu suki amincewa inyaso shikenan kowa ma ya huta sannan shi yaya haidar din ba zai zarge shi da yaƙi yi masa taimakonba kamar yadda yake ta fadar taimako taimako,
Part dinsa ya koma ya samu wuri ya zauna bakin gadonsa yana bin dukkan cikin bedroom din nasa da kallo, katafaren gado ne babba kirar Turkiyya fari tas komai tsaf tsaf kuma fes fes babu wasu tarukuce masu yawa aciki dan daga gadon sai wardrobe da mirror sai bedside drawers sai shoe rack shikenan komai a kammale kuma a tsare, kowanne lungu da saƙo na cikin ɗakin ƙamshi ne mai daɗi ke tashi na turaren oad,
Gani yayi zaman shurun ba zai kai shi ba shiyasa kawai ya tashi ya nufi cikin toilet ya sakarwa kanshi shower, bai wani jima cikin bathroom dinba ya fito daure da towel, cikin kankanin lokaci ya shirya sannan yayi salatul duha raka'a biyu kafin ya dauki key din motar shi ya fita, yana driving yana tunanin ta inda ya dace ya bullowa wannan lamari da haka har ya isa family house, bai shiga ko ina ba sai wurin Hajiya tana zaune cikin bedroom dinta tana gurza goro jikin wata yar karamar greater ta roba, zama yayi kusa da ita,
"Hajiya kaka wai dama har yanzu baki hakura da cin wannan goron bane....."
"to sarkin iyayi da sa ido..... Ban daina ba sai kuma yaya?"
Dariya yayi ya girgiza kansa yace 'babu komai..... Allah ya baki hakuri.... "
" amin..... Ɗan neman sababi "
" to ai maganar ta wuce nace kiyi hakuri...... Ashe hajiya auren anty Mimi ya mutu?"
Tamkar ya sosa mata inda yake yi mata ciwo yaji tayi kwafa kafin cikin takaici tace,
" Aurenta ya mutu mana Mai sunan malam, ai wannan shashashan yayan naku baida ta ido sam..... Ya kasa riketa kullum cikin saki har sai da igiyar auren ta kare kowa ma ya huta...... Yar uwarka cikin ku ɗaya amma ka gagara riketa..... Wallahi takaicin mutuwar auren nan da nake ji mai sunan malam takaicin ya isa.... Tsakanina da Aliyu sai dai ince Allah ya isa... "
" subhanallahi Haba hajiya menene kuma abin yi masa Allah ya isa? Dan Allah kiyi hakuri ki cire bacin ran daga cikin zuciyarki.... Ai shi aure rai gareshi fa, ki dauka kawai dama zaman auren nasu ya kare Kinga dole a rabu idan ma saki bai raba ba sai ki ga wani aciki ya mutu... To Kinga da mutuwar ai gara ace auren ne ya mutu ko..... "
" Hakane lele..... Ai sakarai ne wannan yayan naku... "
" a dai yi hakuri Hajjaju..... Ni yanzu wata magana na zo muyi dake ta sirri idan har kin amince... "
" ina jinka ɗan lele na... "
Tankwashe kafafuwansa yayi ya sake gyara zamansa a gabanta kamar mai shirin daukar karatu,
" cewa nayi tunda auren anty Mimi ya mutu Hajiya.... Ni ina son zan aure ta "
Fasa hambada goron da yake hannunta zuwa bakin ta tayi ta tsaya tana kallonsa bayan ta gyara zaman gilashin ta sosai,
"mai sunan malam..... Kai ma ka fara irin wannan shaye shayen na zamani ko?"
Girgiza kai yayi yana kokarin danne dariyar sa,
"me kuma ya kawo maganar shaye shaye Hajjaju na?"
"to idan ba shaye shaye kake yiba Afeef ina kai ina auren Mimi?"
"saboda me kika ce haka? Ke ya dace ince ko kin fara gigine?"
"Mimi sa'ar ka ce? Shekaru nawa ta baka? Dan raini ko me?"
"shi kuma wannan kudin duk na menene?" ya tambayi kansa hankalinsa na sake dugunzuma, gaskiya Aliyu ya takurawa rayuwarsa haka kuma ya na neman hana shi sukuni, yayin da shi kuma Aliyun ke can yana ji acikin ransa da kuma jikinsa cewa Afeef din shine kadai zai iya yi masa abinda ya dace dan Mimi bata wasa dashi shima kuma baida lokacinta dan haka ya san baza asamu matsala ba komai zai tafi yadda ya dace kuma ya shirya ba tare da wata tangarda ba.
Tsawon kwanaki biyu shi dai Afeef ya kasa gane kansa ma dan ya rasa yaya zai yi da matsalar yaya Aliyu da anty Mimi, kullum cikin takura masa da kira Aliyun yake har hakan yasa yaki zuwa family house dan bama ya son su hadu acan, kwana yake yana sake sake cikin ransa dan ya rasa a inda mafita take. Yau ya jima yana bacci kamar yadda ya saba dan kwana biyu baya samun bacci sosai, sai after 1 sannan ya tashi, wayar shi ya dauka ya kunna yana kunnawa massages din Aliyu suka yi ta shigowa duk na roko ne da magiyar ya taimaka musu ya ceto rayuwar su shi da Mimi saboda idan bai taimake su ba komai zai iya faruwa, bai kai ga karanta massages dinba gaba daya kiran Aliyu ya shigo, dauka yayi a hankali yace,
"hello yaya haidar.....nima yanzu nake cewa zan kiraka fa sai gashi ka kirani"
"A'a Afeef wannan ba gaskiya bane.... Kwana nawa wayarka a kashe"
Murmushi yayi tare da cewa "ehh wallahi yaya..... Dama zan kira ne in fada maka na amince sannan dan Allah wannan kudin da ka turo min zan dawo maka dashi ai ba sai ka biyani ba akan wannan..... We are one family...."
"No Afeef ka barshi ka dauka kawai wata yar karamar kyauta ce daga yaya zuwa kaninsa...."
"A'a yaya wallahi ba zan karɓa ba indai har kana son inyi maka abinda kake bukata.... Bana son inji araina kudi ka biyani dan yi maka wani abu wanda zan iya yi maka koda baka biyani ba saboda karfin zumuncin dake tsakaninmu...."
"to shikenan Afeef na gode Allah ya bar zumunci, yanzu ya za ayi?"
"babu matsala yaya komai zai tafi daidai insha Allah..... But ka jawa anty Mimi kunne Allah karta yarda ta sake ce min jariri...." dariya Aliyu yayi yace,
"insha Allah, gata nan ma tana jinka ai ina office dinta...."
Katse wayar yayi sannan ya tashi ya fita zuwa part din mommy.
Kallon Mimi Aliyu yayi bayan sun gama waya da Afeef, ajiyar zuciya ya sauke jin Afeef din ya amince da kyar,
"ban tsammaci yaron nan zai amince ba.... Kawai na yi tunanin sai dai mu nemi wani..."
Shuru yaji tayi bata amsa ba saboda bata san me zata ce ba ko me zata kira wannan abun ba, ance dai auren kisan wuta to amma a rasa da wa zasu yi auren kisan wuta sai da Afeef?
" My love baki ce komai ba.... You didn't say anything.... "
" to wai me zance Aliyu? Yanzu a rasa da wanda zamuyi auren kisan wuta sai da Afeef?"
"calm down my love.... Shifa RUWAN KASHE GOBARA ba sai mai kyau ba.... Bukatar mu in dai zata biya bamu da damuwar koma waye shi.... Kiyi hakuri..... Kar wannan ya dameki...."
"Ai duk Kaine ka janyo...... Ka rinka abu kamar wani mai shaye shaye ko tabin hankali yanzu ga abinda ka janyo mana nan.... Zaka sa inyi auren kisan wuta da kanin bayana...." daga haka ta dauki wasu files ta fita ta barshi cikin office din, babu abinda yake bata mata rai irin yanda idan ta tuna cewa Afeef ne zai zame mata mijin auren kisan wuta wannan wacce irin lalacewa ce, sai dai amma idan kuma ta tuna da cewa auren na ɗan wucin gadi ne zasu koma su hade da yaya Aliyu sai ta ɗan ji sanyi cikin ranta dan tana mutukar sonsa da kaunarsa haka kuma tana ta faman missing dinshi kamar yadda kullum shima yake yi mata korafin cikin missing dinta yake, to da su cigaba da wannan zaman lalurar wanda shaidan zai iya cin nasara a kansu gara asamu a ganganɗa da Afeef din har bukata ta biya.......
Hmmmmm masu karatu wannan cakwakiya ta ɗaure min kai, please comment what you think.....
Next chapter loading✍🏻
KAIFI ƊAYA... ✨
*When the world called her “useless”… he called her “mine.”*💘
_KAIFI ƊAYA_ is not just a love story. It’s the story of Mimi - a doctor whose name was dragged through scandal, whose body was broken by fate… 💔
And Afeef - the man who chose to stay when everyone told him to leave. 😥
They won the fight against the world.
But can they win the fight for each other, when silence is louder than lies, and love is tested by things neither of them chose? 🥺
*One blade. One choice. One love that refuses to break.*❤️
_Kaifi Daya_ - because true love doesn’t walk away when you can’t walk anymore..😥
It's available now 07044644433
Your heart will not be the same after the last page🥰✍🏻✍🏻
#Kaifi ɗaya#
#lovetriangle
#EmotionalRomance
#DrMimiAndAfeef
_*Ummi Shatu*_👌🏻
[7/18, 8:56 AM] Oum Jasrah: https://www.arewapen.com/book?id=6a50f2f571e75baab6622006
KAIFI ƊAYA....
_A story of scandal, sacrifice and a love that refused to break, a love that says am still here._
NA
UMMI A'ISHA
4
***Cike da kasala da damuwar da yake ta boyewa cikin ranshi ya shiga part din mommy, babu kowa cikin part din kamar yadda gidan ya saba kasancewa dan ita Manal ta tafi makaranta ita kuma mommy ta fita aikinta kamar yadda ta saba, table a shirye shiyasa kawai zama yayi ya fara zuba breakfast din da yaga mommy ta ajiye masa, yana cin abincin yana tunani cikin ransa yanzu ta ina ya dace ya fara sannan wa ya kamata ya tunkara da wannan maganar ta yana son a daura musu aure da anty Mimi?
Har ya gama breakfast din bai tsayar da magana guda daya a cikin ransa ba kawai ya san ayau dole sai ya magantu ko ayi ko a ƙi yi, fata yaji yana yi acikin ransa ma Allah yasa iyayen nasu suki amincewa inyaso shikenan kowa ma ya huta sannan shi yaya haidar din ba zai zarge shi da yaƙi yi masa taimakonba kamar yadda yake ta fadar taimako taimako,
Part dinsa ya koma ya samu wuri ya zauna bakin gadonsa yana bin dukkan cikin bedroom din nasa da kallo, katafaren gado ne babba kirar Turkiyya fari tas komai tsaf tsaf kuma fes fes babu wasu tarukuce masu yawa aciki dan daga gadon sai wardrobe da mirror sai bedside drawers sai shoe rack shikenan komai a kammale kuma a tsare, kowanne lungu da saƙo na cikin ɗakin ƙamshi ne mai daɗi ke tashi na turaren oad,
Gani yayi zaman shurun ba zai kai shi ba shiyasa kawai ya tashi ya nufi cikin toilet ya sakarwa kanshi shower, bai wani jima cikin bathroom dinba ya fito daure da towel, cikin kankanin lokaci ya shirya sannan yayi salatul duha raka'a biyu kafin ya dauki key din motar shi ya fita, yana driving yana tunanin ta inda ya dace ya bullowa wannan lamari da haka har ya isa family house, bai shiga ko ina ba sai wurin Hajiya tana zaune cikin bedroom dinta tana gurza goro jikin wata yar karamar greater ta roba, zama yayi kusa da ita,
"Hajiya kaka wai dama har yanzu baki hakura da cin wannan goron bane....."
"to sarkin iyayi da sa ido..... Ban daina ba sai kuma yaya?"
Dariya yayi ya girgiza kansa yace 'babu komai..... Allah ya baki hakuri.... "
" amin..... Ɗan neman sababi "
" to ai maganar ta wuce nace kiyi hakuri...... Ashe hajiya auren anty Mimi ya mutu?"
Tamkar ya sosa mata inda yake yi mata ciwo yaji tayi kwafa kafin cikin takaici tace,
" Aurenta ya mutu mana Mai sunan malam, ai wannan shashashan yayan naku baida ta ido sam..... Ya kasa riketa kullum cikin saki har sai da igiyar auren ta kare kowa ma ya huta...... Yar uwarka cikin ku ɗaya amma ka gagara riketa..... Wallahi takaicin mutuwar auren nan da nake ji mai sunan malam takaicin ya isa.... Tsakanina da Aliyu sai dai ince Allah ya isa... "
" subhanallahi Haba hajiya menene kuma abin yi masa Allah ya isa? Dan Allah kiyi hakuri ki cire bacin ran daga cikin zuciyarki.... Ai shi aure rai gareshi fa, ki dauka kawai dama zaman auren nasu ya kare Kinga dole a rabu idan ma saki bai raba ba sai ki ga wani aciki ya mutu... To Kinga da mutuwar ai gara ace auren ne ya mutu ko..... "
" Hakane lele..... Ai sakarai ne wannan yayan naku... "
" a dai yi hakuri Hajjaju..... Ni yanzu wata magana na zo muyi dake ta sirri idan har kin amince... "
" ina jinka ɗan lele na... "
Tankwashe kafafuwansa yayi ya sake gyara zamansa a gabanta kamar mai shirin daukar karatu,
" cewa nayi tunda auren anty Mimi ya mutu Hajiya.... Ni ina son zan aure ta "
Fasa hambada goron da yake hannunta zuwa bakin ta tayi ta tsaya tana kallonsa bayan ta gyara zaman gilashin ta sosai,
"mai sunan malam..... Kai ma ka fara irin wannan shaye shayen na zamani ko?"
Girgiza kai yayi yana kokarin danne dariyar sa,
"me kuma ya kawo maganar shaye shaye Hajjaju na?"
"to idan ba shaye shaye kake yiba Afeef ina kai ina auren Mimi?"
"saboda me kika ce haka? Ke ya dace ince ko kin fara gigine?"
"Mimi sa'ar ka ce? Shekaru nawa ta baka? Dan raini ko me?"