Sashe 15
Kaifi Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Aliyu baka da mutunci ko? Bance kar ka sake magana ba? To duka ku bude kunnen ku gaba daya ku jini da kyau, daga yau daga yanzu ban sake yarda irin wannan ta sake faruwa ba, kuna yan uwa ciki daya kuna fada har da dambe, ke mimi kar na sake ji ko gani ko da wasa kin shiga motar Aliyu tunda mijin ki baya so sannan ban yarda ki sake wata magana dashi ba a waya..... Idan kika sake kuma ban yafe miki ba...... Kai kuma Aliyu daga yau babu kai babu ita ban yarda in sake jin wani abu ba makamancin wannan... Afeef shine mijinta a yanzu kuma duk dokar da ya kafa dole ta bita........ "
Kuka kawai anty Mimi ta fashe dashi ta tashi ta koma upstairs yayin da shi kuma yaya haidar ya cika fam ya kawo har wuya, mintuna kadan da zartar da wannan hukuncin da Abba yayi Aliyun ya tashi ya fita yana yiwa Afeef kallon zamu gamu ne, a fusace ya figi motar sa yabar gidan wanda har su Abba na jiyo kugin motar tasa, gudu kawai yake shararawa zuciyarsa na tafarfasa sai zancen zuci yake, yazo kan wani junction suka yi taho mu gama da wata babbar mota tirela,
Su Abba na kokarin shiga sallar ishah aka kira wayar yaya faruk, bai fada musu abinda yake faruwa ba kawai ya shiga mota ya fita da sauri, motar haidar din tayi kwatsa kwatsa haka shima yaji raunuka sosai har an wuce dashi asibiti mafi kusa, sai bayan da suka fito daga masallaci sannan yaya faruk ya kira Abba ya sanar dashi, gaba daya gidan suka dunguma suka tafi asibiti domin duba shi inda yake emergency, duk da abinda ya faru hakan bai hana Afeef bin Irfan ba suka tafi tare, yana kwance yana ta bacci lokacin da suka je duk jikinsa raunuka amma anyi sa'a babu karaya, misalin karfe 11 na dare duk aka tattafi sai iya umma mahaifiyarsa da Janan sune zasu zauna a wurinsa.
Anty Mimi tamkar zata yi hauka saboda hukuncin da taji Abba ya yanke a kanta ita da Aliyu, yanzu shikenan Afeef ya samu nasarar raba su da haidar? Wannan wacce irin mugunta ce da cuta mai girma? Kuka take kamar ranta zai fita haka ta kwana bayan gari ya waye kuma Suhana ta shigo bedroom din nata dauke da breakfast dan babu kowa agidan duk suna asibiti hatta hajiya ma ta tafi, tana kwance cikin bargo kamar marar lafiya,
"Anty Mimi ina kwana? Ga breakfast dinki inji Ammi...."
"Abba ya fita?" shine kawai tambayar da ta yiwa Suhana,
"ehh duk sun tafi asibiti wurin yaya Aliyu...."
"me ya samu yaya Aliyun?" ta fada bakinta na rawa sannan wuf ta tashi zaune tana son jin amsar da suhana zata bata,
"baki san yayi accident ba jiya da daddare?"
"innalillahi wa inna ilaihir rajiun......" ta fada tare da dafe kanta, cikin zuciyar ta kuma cewa take "Allah ya isa tsakanina dakai Afeef.... Allah ya isa"
"nima zanje in shirya.... Ga breakfast din nan"
Da kallo tabi suhana har ta wuce ta fita daga cikin bedroom din, yanzu shikenan ko duba shi ta san ba zata samu damar zuwa ba tunda ga sharadin da Abba ya gindaya mata shima kuma ta san wannan bakin cikin hukuncin na Abba ne yasa har yayi accident dinnan,wayarta ta dauka ta fara kiran number Afeef, bacci yake yi abinsa hankalinsa kwance amma yana son idan ya tashi zaije hospital ya dubo yaya Aliyun, ɗaukar wayar yayi yaga Mimi ce ke kiran sa, bai dauki kiran ba ya mayar da wayar ya ajiye yaci gaba da baccinsa har tayi kiran ta gaji, cikin bakin ciki ta ajiye wayar kafin daga bisani ta sake dauka ta kira hajiya tana dauka ta fara tambayar ta ya jikin Aliyu hajiya tace da sauki yana bacci har yanzu bai farka ba, katse wayar tayi ranta na yi mata wani irin suya.
Bayan Afeef ya tashi daga bacci ya yi breakfast yayi wanka asibiti ya tafi dan kusan kowa yana can in banda su Abba da suka tafi aiki bayan sun duba shi, shima bai jima sosai ba yacewa Irfan bari yaje gida yaga anty Mimi ta kirashi dazu ta yuyu ko tana neman sa ne, tare suka tafi da suhana ya sauketa itama a gida zata ɗora girki, part din hajiya ya shiga inda anan ne anty mimin take, tana zaune bakin gado daure da jan towel ta fito daga wanka idanuwan ta jajur saboda kukan da ta sha, knocking yayi tace "come in..." saboda duk tunanin ta hajjo ce ko kuma ɗaya daga cikin hadiman gidan, har ya shiga cikin dakin bata san shi ne ba dan gaba daya tunani ya cika kwakwalwarta, tsaye yayi yana kallonta wanda ita sai da taji shurun yayi yawa sannan ta kai dubanta hanyar ƙofa nan taga ya zuba mata ido ko ƙiftawa baya yi......✍️
KAIFI ƊAYA.. ✨
What happens after “happily ever after” gets broken? 💔
After the scandal fades.💔
After the accident steals her steps.💔
After a mother whispers, “Marry another.” 💔
There’s still a man who brings tea at 2 AM. 🩷
There’s still a woman who learns to stand in new ways.😥
There’s still a love called _Kaifi Daya_ - One Blade.❤️
Sharp enough to cut through gossip.
Strong enough to hold two people together. 🫂
If you believe love is not about perfection, but about presence…
This book was written for you. 🤝🗣️
_KAIFI ƊAYA_ - Read it with tissue in one hand, hope in the other........🤪
Available now 07044644433
#Kaifiɗaya
#lovetriangle
#EmotionalRomance
#AliyuHaidar
#DrMimiAndAfeef
_*Ummi Shatu*_👌🏻
[7/18, 9:03 AM] Oum Jasrah: https://www.arewapen.com/book?id=6a50f2f571e75baab6622006
_A story of scandal, sacrifice and a love that refused to break, a love that says am still here._
KAIFI ƊAYA.....!
NA
UMMI A'ISHA
12
To my old fans, the ones that reads me years ago❤️, it's been a while since I heard from you and honestly I miss you, i miss us, am back with KAIFI ƊAYA a story of love pain and hope to heal. If u still think of me, come meet Dr Mimi & Afeef their story will touch your hearts. I need ur opinions like before, i miss chatting with you in the comment, please come back let's start again together, thank you for being with me from the beginning, I love you all. 💙
Dear Rahama, thank you for the gift you sent me yesterday, the coffee was delicious..... Tnx alot!
***Tsantsar tsanar da ta bayyana ƙarara akan fuskartace tasa ya dauke idanuwansa daga gareta ya kalli gefe, tamkar ta tashi taje ta rufe shi da duka haka take ji saboda irin bakin cikin da ya ƙunsa mata, wani irin nauyi take jin ƙirjinta da numfashinta sunyi mata,
"Naga miss calls dinki any problem?" ya fada idanuwansa na kallon wani wuri,
"kai wanne irin macuci ne mayaudari azzalumi maci amana? Mun shirya abu da kai rimi rimi amma daga karshe kana kokarin mayar damu kananan yara....... Soo listen and listen good, ko mazan duniya sun kare babu abinda zanyi da kai da sunan miji, tun wuri kaje ka warware abinda ka sarƙa domin wallahi tallahi bazai yi mana kyau ba gaba dayanmu.... Idan har baka warware wannan abun da ka kulla ba you will see the other side of me that even me never knew its existing...... "
" wallahi tallahi Anty Mimi banyi muku haka da niyyar in saka ku cikin matsala ko fushin iyaye ko wani abu mai kama da haka ba, ni kawai nayi hakane dan in tseratar daku daga faɗawa halaka da kuma fushin ubangiji........ Na san yanzu ba zaki fahimta ba amma wata rana ina yi muku fatan ku fahimci tsantsar soyayyata da kaunata gareku, banda mugun nufi akanku Allah shine shaida, maganar yaya Aliyu kiyi hakuri ki manta dashi ki cireshi daga cikin ranki ki dauka Allah gata yayi miki shiyasa ya canja miki dani wanda idan kin karɓa da kyakkyawar niyya zai zame miki mafi alkhairi fiye da auren Aliyu....... Insha Allah zamu rayu tare har gaban abada..... "
Gaba ɗaya wannan maganganun nasa jinsu take kamar yana watsa mata wuta shiyasa bata san lokacin da ta tashi daga inda take zaune ba ta nufe shi tana zuwa ta wanke shi da mari zuciyar ta kamar zata buga dan ɓacin rai,
" ƙarya kake yi ni bazan taɓa rayuwa dakai ba maci amana makaryaci mayaudari.... Wanne aure ne kake maganar zai yi albarka? Auren da aka gina shi da ƙarya da yaudara da cin amana da kuma zalunci? Idan har ka san ba zaka sake niba meyasa tun farko baka fito ka fada mana ba ka nuna mana zaka yi yanda muke so? Ba zan taɓa rayuwa dakai ba idan ma wannan shine plan dinka wallahi ni nafi karfin ka...... "
" Anty Mimi ki fahimceni...."
Kunnuwanta ta toshe ta kurma ƙara tamkar mai aljanu babu shiri ya fita daga cikin dakin yana jiyo ihunta kamar wata karamar yarinya, yana fita daga cikin part din hajiya yaci karo da suhana tana kokarin shiga, motar shi kawai ya shiga yabar gidan ya koma asibiti wurin Irfan,
Kayan kwalliyar ta dake jere reras gaban mirror taje ta fara watsi da su tana ƙara saboda tsabar bakin cikin da take ciki kenan ma bashi da niyyar rabuwa da ita ko sakinta? Shiga cikin bedroom din suhana tayi a kidime tana shiga ta rike ta,
"Anty Mimi me yake faruwa? Me kike yi haka?"
"suhana ba zan iya zama da wannan yaron ba..... Akan me? Saboda me?" ta karasa maganar cikin ƙara,
"ya isa anty Mimi, calm down...... Yi hakuri, zo ki zauna..... Yi hakuri..... Yi shuru.... Zauna" suhana ta fada cikin lallabawa, kama hannunta tayi suka je bakin gado ta zauna tana haki,
"Haba anty Mimi komai yayi zafi fa maganin sa Allah, wannan abun da kike yi kamar karamar yarinya bai dace dake ba..... Kiyi hakuri ki nutsu...."
Shuru Anty Mimi tayi tana mayar da numfashi idanuwanta a runtse, ta san duk yanda zata yiwa suhana bayani ba zata fahimceta ba tunda ba wai zata fito ne fili ta sanar da ita yanda abin ya faro ko kuma ya samo asali ba,
Kuka kawai anty Mimi ta fashe dashi ta tashi ta koma upstairs yayin da shi kuma yaya haidar ya cika fam ya kawo har wuya, mintuna kadan da zartar da wannan hukuncin da Abba yayi Aliyun ya tashi ya fita yana yiwa Afeef kallon zamu gamu ne, a fusace ya figi motar sa yabar gidan wanda har su Abba na jiyo kugin motar tasa, gudu kawai yake shararawa zuciyarsa na tafarfasa sai zancen zuci yake, yazo kan wani junction suka yi taho mu gama da wata babbar mota tirela,
Su Abba na kokarin shiga sallar ishah aka kira wayar yaya faruk, bai fada musu abinda yake faruwa ba kawai ya shiga mota ya fita da sauri, motar haidar din tayi kwatsa kwatsa haka shima yaji raunuka sosai har an wuce dashi asibiti mafi kusa, sai bayan da suka fito daga masallaci sannan yaya faruk ya kira Abba ya sanar dashi, gaba daya gidan suka dunguma suka tafi asibiti domin duba shi inda yake emergency, duk da abinda ya faru hakan bai hana Afeef bin Irfan ba suka tafi tare, yana kwance yana ta bacci lokacin da suka je duk jikinsa raunuka amma anyi sa'a babu karaya, misalin karfe 11 na dare duk aka tattafi sai iya umma mahaifiyarsa da Janan sune zasu zauna a wurinsa.
Anty Mimi tamkar zata yi hauka saboda hukuncin da taji Abba ya yanke a kanta ita da Aliyu, yanzu shikenan Afeef ya samu nasarar raba su da haidar? Wannan wacce irin mugunta ce da cuta mai girma? Kuka take kamar ranta zai fita haka ta kwana bayan gari ya waye kuma Suhana ta shigo bedroom din nata dauke da breakfast dan babu kowa agidan duk suna asibiti hatta hajiya ma ta tafi, tana kwance cikin bargo kamar marar lafiya,
"Anty Mimi ina kwana? Ga breakfast dinki inji Ammi...."
"Abba ya fita?" shine kawai tambayar da ta yiwa Suhana,
"ehh duk sun tafi asibiti wurin yaya Aliyu...."
"me ya samu yaya Aliyun?" ta fada bakinta na rawa sannan wuf ta tashi zaune tana son jin amsar da suhana zata bata,
"baki san yayi accident ba jiya da daddare?"
"innalillahi wa inna ilaihir rajiun......" ta fada tare da dafe kanta, cikin zuciyar ta kuma cewa take "Allah ya isa tsakanina dakai Afeef.... Allah ya isa"
"nima zanje in shirya.... Ga breakfast din nan"
Da kallo tabi suhana har ta wuce ta fita daga cikin bedroom din, yanzu shikenan ko duba shi ta san ba zata samu damar zuwa ba tunda ga sharadin da Abba ya gindaya mata shima kuma ta san wannan bakin cikin hukuncin na Abba ne yasa har yayi accident dinnan,wayarta ta dauka ta fara kiran number Afeef, bacci yake yi abinsa hankalinsa kwance amma yana son idan ya tashi zaije hospital ya dubo yaya Aliyun, ɗaukar wayar yayi yaga Mimi ce ke kiran sa, bai dauki kiran ba ya mayar da wayar ya ajiye yaci gaba da baccinsa har tayi kiran ta gaji, cikin bakin ciki ta ajiye wayar kafin daga bisani ta sake dauka ta kira hajiya tana dauka ta fara tambayar ta ya jikin Aliyu hajiya tace da sauki yana bacci har yanzu bai farka ba, katse wayar tayi ranta na yi mata wani irin suya.
Bayan Afeef ya tashi daga bacci ya yi breakfast yayi wanka asibiti ya tafi dan kusan kowa yana can in banda su Abba da suka tafi aiki bayan sun duba shi, shima bai jima sosai ba yacewa Irfan bari yaje gida yaga anty Mimi ta kirashi dazu ta yuyu ko tana neman sa ne, tare suka tafi da suhana ya sauketa itama a gida zata ɗora girki, part din hajiya ya shiga inda anan ne anty mimin take, tana zaune bakin gado daure da jan towel ta fito daga wanka idanuwan ta jajur saboda kukan da ta sha, knocking yayi tace "come in..." saboda duk tunanin ta hajjo ce ko kuma ɗaya daga cikin hadiman gidan, har ya shiga cikin dakin bata san shi ne ba dan gaba daya tunani ya cika kwakwalwarta, tsaye yayi yana kallonta wanda ita sai da taji shurun yayi yawa sannan ta kai dubanta hanyar ƙofa nan taga ya zuba mata ido ko ƙiftawa baya yi......✍️
KAIFI ƊAYA.. ✨
What happens after “happily ever after” gets broken? 💔
After the scandal fades.💔
After the accident steals her steps.💔
After a mother whispers, “Marry another.” 💔
There’s still a man who brings tea at 2 AM. 🩷
There’s still a woman who learns to stand in new ways.😥
There’s still a love called _Kaifi Daya_ - One Blade.❤️
Sharp enough to cut through gossip.
Strong enough to hold two people together. 🫂
If you believe love is not about perfection, but about presence…
This book was written for you. 🤝🗣️
_KAIFI ƊAYA_ - Read it with tissue in one hand, hope in the other........🤪
Available now 07044644433
#Kaifiɗaya
#lovetriangle
#EmotionalRomance
#AliyuHaidar
#DrMimiAndAfeef
_*Ummi Shatu*_👌🏻
[7/18, 9:03 AM] Oum Jasrah: https://www.arewapen.com/book?id=6a50f2f571e75baab6622006
_A story of scandal, sacrifice and a love that refused to break, a love that says am still here._
KAIFI ƊAYA.....!
NA
UMMI A'ISHA
12
To my old fans, the ones that reads me years ago❤️, it's been a while since I heard from you and honestly I miss you, i miss us, am back with KAIFI ƊAYA a story of love pain and hope to heal. If u still think of me, come meet Dr Mimi & Afeef their story will touch your hearts. I need ur opinions like before, i miss chatting with you in the comment, please come back let's start again together, thank you for being with me from the beginning, I love you all. 💙
Dear Rahama, thank you for the gift you sent me yesterday, the coffee was delicious..... Tnx alot!
***Tsantsar tsanar da ta bayyana ƙarara akan fuskartace tasa ya dauke idanuwansa daga gareta ya kalli gefe, tamkar ta tashi taje ta rufe shi da duka haka take ji saboda irin bakin cikin da ya ƙunsa mata, wani irin nauyi take jin ƙirjinta da numfashinta sunyi mata,
"Naga miss calls dinki any problem?" ya fada idanuwansa na kallon wani wuri,
"kai wanne irin macuci ne mayaudari azzalumi maci amana? Mun shirya abu da kai rimi rimi amma daga karshe kana kokarin mayar damu kananan yara....... Soo listen and listen good, ko mazan duniya sun kare babu abinda zanyi da kai da sunan miji, tun wuri kaje ka warware abinda ka sarƙa domin wallahi tallahi bazai yi mana kyau ba gaba dayanmu.... Idan har baka warware wannan abun da ka kulla ba you will see the other side of me that even me never knew its existing...... "
" wallahi tallahi Anty Mimi banyi muku haka da niyyar in saka ku cikin matsala ko fushin iyaye ko wani abu mai kama da haka ba, ni kawai nayi hakane dan in tseratar daku daga faɗawa halaka da kuma fushin ubangiji........ Na san yanzu ba zaki fahimta ba amma wata rana ina yi muku fatan ku fahimci tsantsar soyayyata da kaunata gareku, banda mugun nufi akanku Allah shine shaida, maganar yaya Aliyu kiyi hakuri ki manta dashi ki cireshi daga cikin ranki ki dauka Allah gata yayi miki shiyasa ya canja miki dani wanda idan kin karɓa da kyakkyawar niyya zai zame miki mafi alkhairi fiye da auren Aliyu....... Insha Allah zamu rayu tare har gaban abada..... "
Gaba ɗaya wannan maganganun nasa jinsu take kamar yana watsa mata wuta shiyasa bata san lokacin da ta tashi daga inda take zaune ba ta nufe shi tana zuwa ta wanke shi da mari zuciyar ta kamar zata buga dan ɓacin rai,
" ƙarya kake yi ni bazan taɓa rayuwa dakai ba maci amana makaryaci mayaudari.... Wanne aure ne kake maganar zai yi albarka? Auren da aka gina shi da ƙarya da yaudara da cin amana da kuma zalunci? Idan har ka san ba zaka sake niba meyasa tun farko baka fito ka fada mana ba ka nuna mana zaka yi yanda muke so? Ba zan taɓa rayuwa dakai ba idan ma wannan shine plan dinka wallahi ni nafi karfin ka...... "
" Anty Mimi ki fahimceni...."
Kunnuwanta ta toshe ta kurma ƙara tamkar mai aljanu babu shiri ya fita daga cikin dakin yana jiyo ihunta kamar wata karamar yarinya, yana fita daga cikin part din hajiya yaci karo da suhana tana kokarin shiga, motar shi kawai ya shiga yabar gidan ya koma asibiti wurin Irfan,
Kayan kwalliyar ta dake jere reras gaban mirror taje ta fara watsi da su tana ƙara saboda tsabar bakin cikin da take ciki kenan ma bashi da niyyar rabuwa da ita ko sakinta? Shiga cikin bedroom din suhana tayi a kidime tana shiga ta rike ta,
"Anty Mimi me yake faruwa? Me kike yi haka?"
"suhana ba zan iya zama da wannan yaron ba..... Akan me? Saboda me?" ta karasa maganar cikin ƙara,
"ya isa anty Mimi, calm down...... Yi hakuri, zo ki zauna..... Yi hakuri..... Yi shuru.... Zauna" suhana ta fada cikin lallabawa, kama hannunta tayi suka je bakin gado ta zauna tana haki,
"Haba anty Mimi komai yayi zafi fa maganin sa Allah, wannan abun da kike yi kamar karamar yarinya bai dace dake ba..... Kiyi hakuri ki nutsu...."
Shuru Anty Mimi tayi tana mayar da numfashi idanuwanta a runtse, ta san duk yanda zata yiwa suhana bayani ba zata fahimceta ba tunda ba wai zata fito ne fili ta sanar da ita yanda abin ya faro ko kuma ya samo asali ba,