← Book details Kaifi Daya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 21

Sashe 14

Kaifi Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

" Aliyu..... Haba ya haka? Kai Afeef sake shi, ku bari mana.... Haba Haidar ya kake fada da ƙanin ƙanin bayanka..... Afeef har nawa yake da zaka rinka kokarin fada dashi?" yaya faruk ya fada cike da mamaki, ita dai anty Mimi kuka ta saka ta shige cikin sashen hajiya da gudu,

" wannan yaron ɗan iska ne bashi da mutunci faruk, da ka barni naci ubansa...."

"Ka fadi duk abinda zaka fada amma daga yau ban yarda ka sake kula mata ta ba bare har ka dauko ta acikin motar ka......"

"Afeef ya isa haka jeka ka tafi abin ka, kar na sake jin bakinka...." yaya faruk ya fada har lokacin shi dai yana cike da mamaki sai yanzu ya fahimci abinda watakila shine musabbabin fadan nasu ta yuyu kishi Afeef yake yi saboda Aliyu ya dauko mimi a mota shiyasa har ta kai su ga haka,

" Ɗan ƙwaya..... Dama idan banda ƙwaya da neman mata ku sojoji me kuka iya..... Ka sha tana karanta maka hauka ko..... Zanyi maganin ka"

Shi dai Afeef bai sake kula shi ba saboda maganar da yaya faruk yayi masa ya wuce cikin motarsa yama fasa shiga wurin hajiyan ya fita daga cikin gidan ransa a ɓace, wannan kallon da yawancin mutane ke yi musu su sojoji yana ɓata masa rai, ai a ko ina akwai ɓata gari kuma akwai mutanen kirki ba duk soja ne ke wannan harkar ba,

Bayan tafiyar Afeef yaya faruk kama hannun yaya Aliyu yayi har zuwa cikin runfa,

"Haba Aliyu me yasa zaka biyewa Afeef bayan ka san shi yaro ne, ai bai kamata ba a ce ka tsaya kana fada dashi sai kace wani sa'anka...... Idan akan matarsa ne ka rabu dashi kar ka sake bata lift shikenan, duk da na san yar uwarka ce amma hanyar lafiya sai abita da shekara "

Shuru yaya Aliyu yayi saboda baya jin zai iya fadawa faruk gaskiyar abinda ke faruwa duk da shine abokin shawarar shi kuma babban amininshi........✍️

KAIFI ƊAYA... ✨

*When the world called her “useless”… he called her “mine.”*💘

_KAIFI ƊAYA_ is not just a love story. It’s the story of Mimi - a doctor whose name was dragged through scandal, whose body was broken by fate… 💔
And Afeef - the man who chose to stay when everyone told him to leave. 😥

They won the fight against the world.
But can they win the fight for each other, when silence is louder than lies, and love is tested by things neither of them chose? 🥺

*One blade. One choice. One love that refuses to break.*❤️
_Kaifi Daya_ - because true love doesn’t walk away when you can’t walk anymore..😥

It's available now 07044644433

Your heart will not be the same after the last page🥰✍🏻✍🏻

#Kaifiɗaya
#lovetriangle
#EmotionalRomance
#DrMimiAndAfeef

_*Ummi Shatu*_👌🏻
[7/18, 9:03 AM] Oum Jasrah: https://www.arewapen.com/book?id=6a50f2f571e75baab6622006

_A story of scandal, sacrifice and a love that refused to break, a love that says am still here._

KAIFI ƊAYA......!

NA
UMMI A'ISHA

11

***Duk bayanin da yaya faruk ke yi masa baya fahimtar su dan gaba ɗaya hankalinsa da tunaninsa da kuma nutsuwarsa basa tare dashi he was out of his sense, baƙin ciki da wani irin radadi sune suka lullube zuciyarsa suka hana shi tuna komai a wannan hali wani abu mai nauyi ya sauka ya dirar masa akan ƙirjinsa even his breath was heavy, wai shi Afeef ya dubi tsabar idonsa yace zai tare da Mimi acikin gidansa, lallai ta tabbata wannan yaron bai shiryawa zaman lafiya ba sannan bai so a rabu lafiya ba he don't want peace,

Ganin babu abinda zai fahimta ko kuma zai gane kawai yasa ya yiwa Yaya Faruk sallama ya figi motar sa ya fita, ganin ya fita yasa yaya faruk shiga ɓangaren hajiya wadda duk gidajensu guda uku babu wanda yasan abinda yake faruwa, kitso ya tarar ana yiwa hajiyan bai zauna ba ya nufi bedroom din anty Mimi dake can upstairs, tana kwance tana sharar hawaye kamar koda yaushe cikin yan kwanaki nan,

"Mimi..... Tashi..." taji yaya faruk ya fada bayan ya shigo har cikin bedroom din nata, tashi zaune tayi tana sharar hawaye,

"Mimi me yasa zaki rinka shiga motar Faruk da sunan lift? Yes na san dan uwa ki ne ko babu aure, amma tunda mijin ki ya nuna baya so to ina baki shawarar ki hakura da hakan, kibi umarnin mijinki....."

Wasu hawaye masu ƙuna da raɗaɗi taji sun fara tsere kan kumatunta, wannan kuma wacce irin masifa ce?

" Dan Allah ki kiyaye kar na sake jin wani abu ya faru makamancin haka please..... "

Zubawa faruk ido kawai tayi tana hawaye bakin ciki ya hana ta magana koda yake bata da abinda zata fada daidai wannan lokaci, shiyasa har ya ƙaraci fadansa cikin nasiha ya gama ya fita bata ce uffan ba, wani tashin hankali take ji irin wanda bata taɓa jinsa ba, Afeef ya cuci rayuwar su sannan ya yaudare su, bayan fitar yaya faruk kwanciya ta koma ta sake yi tana zubar da hawaye.

Baƙin cikin maganar da Afeef ya faɗawa yaya Aliyu itace ta tsaye masa a rai ya kasa zaune ya kasa tsaye kuma ya kasa ci ya kasa sha sannan bacci ya kauracewa idanuwansa, wai har shi wannan dan tatsitsin yaron zai saka a gaba yana fadawa magana any how? Ƙudurcewa yayi a ransa duk ranar da Allah ya sake hada shi da Afeef sai anyi ɓacacciya sai yayi masa mugun duka irin duka na mutuwa.

Afeef gida ya koma ransa a ɓace kuma a jagwalgwale, yana shiga Irfan ya kirashi a waya kamar ba zai dauka ba amma ya daure ya dauka yana kokarin saisaita kansa,

"Naje family house ban same ka ba, gashi har na dawo gida ma...."

"ok shine ba zaka jirani ba?"

"zan sake dawowa an jima...."

Daga haka ya katse wayar yana nazari, dole ya dauki mataki akan anty Mimi da yaya Aliyu, ba zai zuba musu ido suna wulakantashi ba sun mayar dashi kamar wani soko ko kuma dolo, baya jin ƙarfin jikinsa dan kamar ciwon sa na kokarin tashi shiyasa ya wuce part din mommy ya hada coffee mai zafi tafasasshe ya sha amma duk da haka bai ji shi daidai ba, part dinshi ya koma ya hada ruwan zafi sosai sannan ya shiga cikin bahon wankan ya kwanta yana jin zafin ruwan yana ratsa kowacce kafa ta jikinsa yana gasuwa, ya jima ciki yana juyi daga bisani ya fito ya saka kaya ya zauna saboda ya dan ji dama dama, a duk lokacin da yake irin wannan ciwon nashi anty Mimi ke kulawa dashi dan wani lokacin ma can family house din yake tattarawa ya koma har sai yaji sauki sannan ya dawo gida. Bai sake fita ba sai bayan magriba lokacin ne ya tafi family house dan yana son ya samu iyayen su maza gaba ɗaya kamar yadda ya tsara cikin ransa,

Yaga motar yaya faruk da ta yaya Aliyu wannan ya bashi tabbacin suna cikin gidan gaba ɗayansu, kamar koda yaushe suna zagaye da hajiya kaka yayanta da jikokinta anata hira ana raha,

Da sallama a bakinsa ya shiga cikin falon nan gaba daya hankalin kowa ya dawo kansa aka fara yi masa sannu da zuwa dan da yawa basu ganshi ba tun dawowarsa sai yanzu, ya gaida kowa ya amsa banda yaya Aliyu da ko kallonsa bai yiba in banda harara da yake aika masa, kusa da Afeef yaje ya zauna suka fara gaisawa, zuwa can ya matsa kusa da kaka yace,

"Hajiya ina son Magana dasu Abba...."

"ya isa.... Sha lele yana son magana da iyayensa.... Lele na me ya faru?" hajiya ta fada cikin kulawa,

"Hajiya akan maganar auren mu da anty Mimi ne...... So nake ayi mana tsakani da yaya Aliyu daga yau babu shi babu ita....." ai tun kafin ya rufe bakinsa Aliyu yayi kukan kura ya cakumo shi ya fara kifa masa mari nan wani fadan ya kaure a tsakanin su Irfan da yaya Faruk suka tashi suna kokarin raba su yayin da su kuma iyayen su maza kowa ya fara daka tsawa,

" Kai har ka isa...... Dan kutumar ubanka nawa kake....."

"innalillahi wa inna ilaihir rajiun....... Wai me yake faruwa haka? Kai Aliyu me ya hadaka dashi?" hajiya ta fada cikin tashin hankali, shi dai Daddy wato mahaifin Afeef bai ce komai ba saboda ganin yayyensa na nan wato Abba fari da Abba baƙi, wata tsawa Abba fari ya dakawa Aliyu,

"Aliyu you must be very stupid, Idan na sake jin bakinka Haidar sai naci mutuncinka..... Ashe dama baka da mutunci? Kai Irfan kira min Mimi...." cikin sauri Irfan ya tashi ya haura upstairs bedroom din anty Mimi inda take kwance tun bayan da ta idar da sallar magrib,

"Anty Mimi Abba yana kiran ki..... Kiyi sauri ki zo dan a fusace yake he's upset" daga haka ya juya ya fita dan yasan halin Abba idan ransa ya baci bai da sauki,

"Abba gata nan zuwa...."

Tun daga nesa gabanta ke faduwa tana kallonsu daya bayan daya, idonta ne ya sauka kan Afeef da ke zaune cikin fushi hancinsa duk jini wanda gashi nan har ya zuba a gaban rigar sa ya ɓata,

Tsugunnawa tayi ta durkusa daga nesa dasu kadan,

" Abba ina yininku?"

Bai amsa gaisuwar ta ba ya juya ya kalli Afeef yace,

"Afeef me kace akan mimi da Aliyu?"

"Abba so nake ayi mana tsakani da yaya Aliyu daga yau babu shi babu ita, ban yarda ya sake daukar ta ko acikin motar sa ba ko ya kirata a waya, gaisuwa kadai na yarda ta hada su...."

"saboda Kaine wa? Kai ka isa ka raba ni da ita? Who do you think you are?" ya Aliyu ya fada yana kokarin sake tashi faruk yana rike shi,
Chapter 14 · 0% Book details