Sashe 16
Kaifi Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
" Breakfast din da na kawo miki baki ci ba anty Mimi why?" suhana ta tambaya tana duba warmers din da ta ajiye mata tunda safe,
"bana jin yunwa..... Am no hungry"
"daurewa zaki yi anty please....."
"zanci idan ina jin yunwa"
Tashi suhana tayi ta gyara mata kan mirror dinta ta tattare wanda suka fashe ta fita.
Tun daga wannan ranar bata sake saka shi cikin idanuwanta ba ko taji motsin shi duk da cewa time to time yana zuwa gidan, kwanan yaya haidar biyar a asibiti ta tambayi hajiya tana son taje ta duba shi amma hajiya tace ba zata je ba tayi masa fatan samun sauki daga gida Allah zai amsa ba sai taje ba, duk da tana son zuwa dole tana ji tana gani haka ta hakura domin bayan hanatan da hajiya tayi harda sake fadawa Abba nan shima ya hana yace koda wasa kar yaji ta je duba Aliyu idan kuma ta matsu da dole sai taje to ta kira mijinta suje tare, ta rasa yaya zata yi da bakin cikin da take dawainiya dashi cikin zuciyarta.
Yaya Aliyu tunda yake kwance gadon asibiti bai san wanda ke kansa ba sai yau da ya farfaɗo har ya samu bakin magana, Umma mahaifiyar shi dake tare dashi ya kalla sai janan kanwarshi cikin bakin cikin da yake jin har ya koma ga Allah bazai bar cikin zuciyarsa ba yace da umma,
"umma Mimi ta zo?"
"Mimi bata zo ba Haidar amma kowa yazo ya duba ka, ka koma ka kwanta ka daina magana...."
"umma Abban anty Mimi bai kyauta min ba, abinda yayi min ko bare ba zai yimin ba, ya zabi Afeef sama dani, he takes Afeefs side......."
Haushi, ɓacin rai da damuwa umma ta shiga bayan Aliyu ya gama rattaba mata duk abubuwan da suka faru wanda sune suka ja har yayi wannan accident din, umma cika tayi tai fam shiyasa da daddare bayan magriba kowa yana zuwa ganin haidar ana ta murnar ya fara magana yana gane kowa da Afeef yazo umma kicin kicin tayi da fuska ta hade rai kamar bata taɓa dariya ba haka kuma da kyar ta amsa gaisuwar shi ita kuwa janan ko gaishe shi bata yi ba dan gaba daya haushinsa suke ji bama shi kadai ba har da iyayen anty Mimi da ita Mimin, ita laifin ta wai bata zo ta duba shi ba, su kuma Abba da Ammi laifinsu sun fifita Afeef akan Haidar, shi dai Afeef bai kawo komai cikin ransa ba ya juya ya fita duk da cewa Aliyun bai amsa gaisuwar shi ba, yana fita Abba ƙarami ya shigo wato Abba baƙi mahifin su Aliyu, har lokacin umma a turɓune take,
"Ya mai jikin? Ya dan ci abincin kuwa?"
"Au dama ka damu dashi ne? Ai na zaci kai baka damu dashi ba yanda sauran mutane suka damu da ƴayan su...."
Kallonta Abba yayi cike da mamaki,
"ban fahimce ki ba.... Ban gane abinda kike fada ba.... Duk me ya kawo wannan maganar?"
"Ai bazaka fahimta ba dama, kowa ya nuna nasa yake so sai kaine baka son naka, kowa ya koma daga bayan ɗansa ya goyi bayansa amma kai banda kai, to idan kai baka son sa ni ina son sa saboda yanda kowanne ɗa ya tsaga jikin uwarsa ya fito nima haka ya tsaga jikina ya fito, wallahi bazan taɓa ƙin ɗana ba akan na wani.. " gaba ɗaya maganganun nan na umma ɗaurewa Abba kai suka yi saboda a iya saninsa abinda ya faru bai wani kai ya kawo ba, sannan hukuncin da ɗan uwansa ya yanke akan wannan saɓanin da su haidar suka samu yayi daidai dan ko shine irinsa zai yanke, ya san idan ya tsaya yi mata bayani ba lallai ta fahimta ba sannan nan asibiti ne bai kamata su zauna suna hayaniya ba akan marar lafiya da girman su da komai dan haka ya juya ya fita kawai ba tare da ya zauna ba, duk da ya fita din umma bata iya yin shuru ba haka ta cigaba da fadar duk abinda yazo bakinta. Washe gari kamar yadda Ammi ta saba da kanta ta shiga kitchen ta hada abinci wanda za a kai asibiti dan tunda ya kwanta kullum ita ke kai musu abinci safe rana dare sannan ana kaiwa daga bangaren hajiya kaka ma, yau harda kunun tsamiya ta yiwa Aliyu saboda shi masoyin kunun tsamiya ne, tare da suhana suka tafi Irfan ya kai su, tun shigar su cikin dakin da Aliyu yake Ammi taga kamar fuskar umma babu walwala sannan ta canja, zama tayi tana tambayar ya mai jikin umma ta amsa ciki ciki,
"Allah ya bashi lafiya, ga kunun tsamiya nan da na iyo masa idan ya tashi sai ya sha..."
"Ai da ma kin barshi kawai, wanda akayi a baya ma ya isa amma wannan yanzu ku koma dashi kawai mun gode...."
Shuru Ammi tayi tana nazarin maganar da umma ta fada amma sai taga bai dace tayi shuru ba gara koma menene su warware shi a yanzu,
"umman janan me yake faruwa? Yanzu dan na kawowa Aliyu abinci ai ba wani abu bane, ba duk ɗaya bane..."
"ba ɗaya bane, ada shine ake ɗaya amma yanzu kowa nasa yake so.... Banda haka me zai saka ku amince ku yarda ku aurar da Mimi ga Afeef bayan Aliyu ne ya aureta ai ana barin halal dan kunya, sannan kun fi kowa sanin so muke mu haɗa Afeef da janan aure tun suna ƙanana, tun janan tana jaririya da aka haife ta muka kuduri niyyar aurawa Afeef, amma saboda kowa kansa ya sani kuma nasa ya sani shine kuka murde magana kuka karkatar da ita kuka bawa Afeef Mimi, idan har akwai zumunci da kaunar juna ya dace Aliyu ya saki mata Afeef ya aura? Idan har akwai kara da kunya ya dace ku bawa Afeef yar ku bayan Aliyu ne ya taɓa auren ta? Idan ma zaton ku Aliyu ne baya haihuwa shiyasa kuka dage har sai da kuka raba su kuka kashe auren yanzu kuka aurawa Afeef to ɗana lafiyar sa ƙalau kuma bashi da matsalar haihuwa dama ai maza basu cika zama juya ba sai mata ne ke zama juya..... "
" Yanzu duk akan wannan umman janan kika kullace mu har kike irin wadannan maganganun a gaban yara? Ai da Aliyu da Mimi da Afeef ni duk daya ne awurina.... "
" wallahi karya kike yi ba ɗaya bane, daga ke har mijinki iya kanku kuke so.... Kuma anyi walkiya "
" Ammi tashi mu tafi... " suhana ta faɗa cikin dacin rai, wannan wacce irin masifa ce daga zuwan su shikenan kamar dama ana jira?
" A'a suhana bari tukunna ta gama fadar duk abinda take son ta fada, ni bani na hada auren Afeef da Mimi ba nima ina zaune aka kawo min goro haka bani naje na raba auren mimi da haidar ba shine dan radin kansa ya saketa to yayi mata saki ɗai ɗai ɗai har uku ya zamuyi da su? Ai dole a hakura ta auri wani tunda ba a garin mahaukata muke ba.... "
" ai shiyasa kuka aura mata kanin bayansa wanda suka fito tsatso daya saboda babu kunya bare kara.... "
Tashi suhana tayi ta fice daga cikin dakin bayan ta dauki basket din dake dauke da abincin da suka zo da shi, tana fita ta hango hajiya da Afeef da ya kawota sun nufo dakin Irfan yana gefen su....✍🏻
KAIFI ƊAYA... ✨
*When the world called her “useless”… he called her “mine.”*💘
_KAIFI ƊAYA_ is not just a love story. It’s the story of Mimi - a doctor whose name was dragged through scandal, whose body was broken by fate… 💔
And Afeef - the man who chose to stay when everyone told him to leave. 😥
They won the fight against the world.
But can they win the fight for each other, when silence is louder than lies, and love is tested by things neither of them chose? 🥺
*One blade. One choice. One love that refuses to break.*❤️
_Kaifi Daya_ - because true love doesn’t walk away when you can’t walk anymore..😥
It's available now 07044644433
Your heart will not be the same after the last page🥰✍🏻✍🏻
#Kaifiɗaya
#lovetriangle
#EmotionalRomance
#DrMimiAndAfeef
*_Ummi Shatu_*👌🏻
[7/18, 9:02 AM] Oum Jasrah: https://www.arewapen.com/book?id=6a50f2f571e75baab6622006
_A story of scandal, sacrifice and a love that refused to break, a love that says am still here._
KAIFI ƊAYA....!
NA
UMMI A'ISHA
13
***Yanda umma ke magana a zafafe cikin zafin rai shine yafi komai bawa Ammi mamaki, to ko umma ta manta irin zazzafar soyayyar dake tsakanin Haidar da Ammi ne? Itace fa ta raineshi tun daga yaye ta hada su da Faruk ta raina har suka girma suka kai minzalin aure, shi Aliyun ma sai bayan da ya girma sannan ya gane ba sune iyayen sa ba su umma ne saboda a hannun Ammi ya taso,
"Wadannan maganganun da kike yi ummansu sai nake ji a raina kamar dama can akwai wani miki acikin zuciyarki ko kuma akwai wani kulli da kika ajiye...."
"babu abinda na kullata acikin raina, kawai dai gani nayi lokaci yayi wanda zamu fadawa kawunanmu gaskiya tunda kowa yanzu nasa shine nasa sannan iya nasa yake so...."
Suhana tana tsaye ranta idan yayi dubu a bace yake su hajiya suka ƙaraso, babu wanda ta iya buda baki ta yiwa magana tana ji suna tambayar ta har sun fito zasu tafi ne?
" ku kyale ƴar jakar uba, tana ji ana yi mata magana.... " inji Hajiya ita dai Suhana bata tanka ba tana ganin su suka shiga ɗakin da yaya Aliyu yake kuma suna shiga suka ji Ammi na cewa,
"maganar fa kowa Nasa yake so bata taso ba dan kece kika fahimci abin ahaka sannan kika juya shi izuwa hakan shiyasa kike kallon kamar yanzu kowa bayan nasa yake bi, ni har gobe Aliyu matsayin ɗa yake awurina, baida banbanci da yaran da na haifa dan duk ɗaya nake kallon su... "
" wallahi ƙarya kike wannan maganar ba har zuciyarki ba..... Da ɗaya kike kallonsu da yayanki kamar yadda kika fada ai da baki goyi bayan a rusa rayuwar sa ba.... Auren cin amana auren ɓata zumunci "
"bana jin yunwa..... Am no hungry"
"daurewa zaki yi anty please....."
"zanci idan ina jin yunwa"
Tashi suhana tayi ta gyara mata kan mirror dinta ta tattare wanda suka fashe ta fita.
Tun daga wannan ranar bata sake saka shi cikin idanuwanta ba ko taji motsin shi duk da cewa time to time yana zuwa gidan, kwanan yaya haidar biyar a asibiti ta tambayi hajiya tana son taje ta duba shi amma hajiya tace ba zata je ba tayi masa fatan samun sauki daga gida Allah zai amsa ba sai taje ba, duk da tana son zuwa dole tana ji tana gani haka ta hakura domin bayan hanatan da hajiya tayi harda sake fadawa Abba nan shima ya hana yace koda wasa kar yaji ta je duba Aliyu idan kuma ta matsu da dole sai taje to ta kira mijinta suje tare, ta rasa yaya zata yi da bakin cikin da take dawainiya dashi cikin zuciyarta.
Yaya Aliyu tunda yake kwance gadon asibiti bai san wanda ke kansa ba sai yau da ya farfaɗo har ya samu bakin magana, Umma mahaifiyar shi dake tare dashi ya kalla sai janan kanwarshi cikin bakin cikin da yake jin har ya koma ga Allah bazai bar cikin zuciyarsa ba yace da umma,
"umma Mimi ta zo?"
"Mimi bata zo ba Haidar amma kowa yazo ya duba ka, ka koma ka kwanta ka daina magana...."
"umma Abban anty Mimi bai kyauta min ba, abinda yayi min ko bare ba zai yimin ba, ya zabi Afeef sama dani, he takes Afeefs side......."
Haushi, ɓacin rai da damuwa umma ta shiga bayan Aliyu ya gama rattaba mata duk abubuwan da suka faru wanda sune suka ja har yayi wannan accident din, umma cika tayi tai fam shiyasa da daddare bayan magriba kowa yana zuwa ganin haidar ana ta murnar ya fara magana yana gane kowa da Afeef yazo umma kicin kicin tayi da fuska ta hade rai kamar bata taɓa dariya ba haka kuma da kyar ta amsa gaisuwar shi ita kuwa janan ko gaishe shi bata yi ba dan gaba daya haushinsa suke ji bama shi kadai ba har da iyayen anty Mimi da ita Mimin, ita laifin ta wai bata zo ta duba shi ba, su kuma Abba da Ammi laifinsu sun fifita Afeef akan Haidar, shi dai Afeef bai kawo komai cikin ransa ba ya juya ya fita duk da cewa Aliyun bai amsa gaisuwar shi ba, yana fita Abba ƙarami ya shigo wato Abba baƙi mahifin su Aliyu, har lokacin umma a turɓune take,
"Ya mai jikin? Ya dan ci abincin kuwa?"
"Au dama ka damu dashi ne? Ai na zaci kai baka damu dashi ba yanda sauran mutane suka damu da ƴayan su...."
Kallonta Abba yayi cike da mamaki,
"ban fahimce ki ba.... Ban gane abinda kike fada ba.... Duk me ya kawo wannan maganar?"
"Ai bazaka fahimta ba dama, kowa ya nuna nasa yake so sai kaine baka son naka, kowa ya koma daga bayan ɗansa ya goyi bayansa amma kai banda kai, to idan kai baka son sa ni ina son sa saboda yanda kowanne ɗa ya tsaga jikin uwarsa ya fito nima haka ya tsaga jikina ya fito, wallahi bazan taɓa ƙin ɗana ba akan na wani.. " gaba ɗaya maganganun nan na umma ɗaurewa Abba kai suka yi saboda a iya saninsa abinda ya faru bai wani kai ya kawo ba, sannan hukuncin da ɗan uwansa ya yanke akan wannan saɓanin da su haidar suka samu yayi daidai dan ko shine irinsa zai yanke, ya san idan ya tsaya yi mata bayani ba lallai ta fahimta ba sannan nan asibiti ne bai kamata su zauna suna hayaniya ba akan marar lafiya da girman su da komai dan haka ya juya ya fita kawai ba tare da ya zauna ba, duk da ya fita din umma bata iya yin shuru ba haka ta cigaba da fadar duk abinda yazo bakinta. Washe gari kamar yadda Ammi ta saba da kanta ta shiga kitchen ta hada abinci wanda za a kai asibiti dan tunda ya kwanta kullum ita ke kai musu abinci safe rana dare sannan ana kaiwa daga bangaren hajiya kaka ma, yau harda kunun tsamiya ta yiwa Aliyu saboda shi masoyin kunun tsamiya ne, tare da suhana suka tafi Irfan ya kai su, tun shigar su cikin dakin da Aliyu yake Ammi taga kamar fuskar umma babu walwala sannan ta canja, zama tayi tana tambayar ya mai jikin umma ta amsa ciki ciki,
"Allah ya bashi lafiya, ga kunun tsamiya nan da na iyo masa idan ya tashi sai ya sha..."
"Ai da ma kin barshi kawai, wanda akayi a baya ma ya isa amma wannan yanzu ku koma dashi kawai mun gode...."
Shuru Ammi tayi tana nazarin maganar da umma ta fada amma sai taga bai dace tayi shuru ba gara koma menene su warware shi a yanzu,
"umman janan me yake faruwa? Yanzu dan na kawowa Aliyu abinci ai ba wani abu bane, ba duk ɗaya bane..."
"ba ɗaya bane, ada shine ake ɗaya amma yanzu kowa nasa yake so.... Banda haka me zai saka ku amince ku yarda ku aurar da Mimi ga Afeef bayan Aliyu ne ya aureta ai ana barin halal dan kunya, sannan kun fi kowa sanin so muke mu haɗa Afeef da janan aure tun suna ƙanana, tun janan tana jaririya da aka haife ta muka kuduri niyyar aurawa Afeef, amma saboda kowa kansa ya sani kuma nasa ya sani shine kuka murde magana kuka karkatar da ita kuka bawa Afeef Mimi, idan har akwai zumunci da kaunar juna ya dace Aliyu ya saki mata Afeef ya aura? Idan har akwai kara da kunya ya dace ku bawa Afeef yar ku bayan Aliyu ne ya taɓa auren ta? Idan ma zaton ku Aliyu ne baya haihuwa shiyasa kuka dage har sai da kuka raba su kuka kashe auren yanzu kuka aurawa Afeef to ɗana lafiyar sa ƙalau kuma bashi da matsalar haihuwa dama ai maza basu cika zama juya ba sai mata ne ke zama juya..... "
" Yanzu duk akan wannan umman janan kika kullace mu har kike irin wadannan maganganun a gaban yara? Ai da Aliyu da Mimi da Afeef ni duk daya ne awurina.... "
" wallahi karya kike yi ba ɗaya bane, daga ke har mijinki iya kanku kuke so.... Kuma anyi walkiya "
" Ammi tashi mu tafi... " suhana ta faɗa cikin dacin rai, wannan wacce irin masifa ce daga zuwan su shikenan kamar dama ana jira?
" A'a suhana bari tukunna ta gama fadar duk abinda take son ta fada, ni bani na hada auren Afeef da Mimi ba nima ina zaune aka kawo min goro haka bani naje na raba auren mimi da haidar ba shine dan radin kansa ya saketa to yayi mata saki ɗai ɗai ɗai har uku ya zamuyi da su? Ai dole a hakura ta auri wani tunda ba a garin mahaukata muke ba.... "
" ai shiyasa kuka aura mata kanin bayansa wanda suka fito tsatso daya saboda babu kunya bare kara.... "
Tashi suhana tayi ta fice daga cikin dakin bayan ta dauki basket din dake dauke da abincin da suka zo da shi, tana fita ta hango hajiya da Afeef da ya kawota sun nufo dakin Irfan yana gefen su....✍🏻
KAIFI ƊAYA... ✨
*When the world called her “useless”… he called her “mine.”*💘
_KAIFI ƊAYA_ is not just a love story. It’s the story of Mimi - a doctor whose name was dragged through scandal, whose body was broken by fate… 💔
And Afeef - the man who chose to stay when everyone told him to leave. 😥
They won the fight against the world.
But can they win the fight for each other, when silence is louder than lies, and love is tested by things neither of them chose? 🥺
*One blade. One choice. One love that refuses to break.*❤️
_Kaifi Daya_ - because true love doesn’t walk away when you can’t walk anymore..😥
It's available now 07044644433
Your heart will not be the same after the last page🥰✍🏻✍🏻
#Kaifiɗaya
#lovetriangle
#EmotionalRomance
#DrMimiAndAfeef
*_Ummi Shatu_*👌🏻
[7/18, 9:02 AM] Oum Jasrah: https://www.arewapen.com/book?id=6a50f2f571e75baab6622006
_A story of scandal, sacrifice and a love that refused to break, a love that says am still here._
KAIFI ƊAYA....!
NA
UMMI A'ISHA
13
***Yanda umma ke magana a zafafe cikin zafin rai shine yafi komai bawa Ammi mamaki, to ko umma ta manta irin zazzafar soyayyar dake tsakanin Haidar da Ammi ne? Itace fa ta raineshi tun daga yaye ta hada su da Faruk ta raina har suka girma suka kai minzalin aure, shi Aliyun ma sai bayan da ya girma sannan ya gane ba sune iyayen sa ba su umma ne saboda a hannun Ammi ya taso,
"Wadannan maganganun da kike yi ummansu sai nake ji a raina kamar dama can akwai wani miki acikin zuciyarki ko kuma akwai wani kulli da kika ajiye...."
"babu abinda na kullata acikin raina, kawai dai gani nayi lokaci yayi wanda zamu fadawa kawunanmu gaskiya tunda kowa yanzu nasa shine nasa sannan iya nasa yake so...."
Suhana tana tsaye ranta idan yayi dubu a bace yake su hajiya suka ƙaraso, babu wanda ta iya buda baki ta yiwa magana tana ji suna tambayar ta har sun fito zasu tafi ne?
" ku kyale ƴar jakar uba, tana ji ana yi mata magana.... " inji Hajiya ita dai Suhana bata tanka ba tana ganin su suka shiga ɗakin da yaya Aliyu yake kuma suna shiga suka ji Ammi na cewa,
"maganar fa kowa Nasa yake so bata taso ba dan kece kika fahimci abin ahaka sannan kika juya shi izuwa hakan shiyasa kike kallon kamar yanzu kowa bayan nasa yake bi, ni har gobe Aliyu matsayin ɗa yake awurina, baida banbanci da yaran da na haifa dan duk ɗaya nake kallon su... "
" wallahi ƙarya kike wannan maganar ba har zuciyarki ba..... Da ɗaya kike kallonsu da yayanki kamar yadda kika fada ai da baki goyi bayan a rusa rayuwar sa ba.... Auren cin amana auren ɓata zumunci "