← Book details Kaifi Daya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 21

Sashe 19

Kaifi Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kullum yake zuwa gidan kuma acan yake wuni saboda gaba daya tunaninta ya hanashi sakat bare sukuni, baya iya tuna komai sai ita haka kuma baya jin daɗin komai, amma har yanzu bai yi tozali da ita ba tsawon kwana hudu kenan, bashi kadai ba kusan kowa ma baya ganinta, yau dai tunda yaje gidan ya haura upstairs ya tsaya a kofar ɗakinta yana knocking tare da magiyar ta bude masa ƙofa,

"Anty Mimi please na roƙeki da girman Allah ba dan ni ba kiyi hakuri ki bude min in ganki koda na 1 seconds ne, dan Allah ba dan ni ba, i know i mess up but am sorry..... Kiyi hakuri"

Sama sama take jin sa saboda wani irin ciwon kai ne da zazzafan zazzabi suke rinjayarta, jiri yana ɗan ɗaukarta haka ta sauka daga kan gadonta tana dafa bango taje ta buɗe ƙofar, blue din riga ce a jikinta marar nauyi kanta babu ɗan kwali gaba ɗaya gashin kanta ya barbazu ya sauka kan shoulder dinta amma kallo ɗaya zaka yi mata zaka gane a galabaice take dan tayi bala'in fita hayyacinta,

"me ya..... Dawo.... Da.... Kai??" yaji ta faɗa sai dai yanda tayi maganar a rarrabe shine ya sake tabbatar masa da ba ƙalau take ba,

"na zo ne kawai in ganki..... Na kasa daina tunaninki acikin zuciyata...... You are always on my mind.... I didn't stop thinking about you"

Baki yaga ta bude amma sai ta gagara magana kawai yaga ta dafe kanta sannan ta tafi luuuhhhh zata faɗi, cikin sauri kuma cikin zafin nama ya tarota ta faɗa jikinsa sharafff, gani yayi kamar bata numfashi cikin tashin hankali ya soma jijjigata,

" Mimi...... Mimi..... Mimi...." ya fara kiran sunanta cikin ƙaraji daidai lokacin Dr jalila ta hawo upstairs din,

"what's wrong with her? Me yake faruwa?"

"kawai faduwa naga tayi nima ban sani ba..... Bari in dauketa a kai ta hospital..."

"no ba sai ka kaita hospital ba..... Muje ciki"

Cikin sauri ya dauketa zuwa cikin bedroom dinta ya ajiyeta saman gado duk ya birkice kamar ba soja ba gani yake kamar cewa za ayi ta mutu, handbag dinta yaga Dr jalilan ta bude ta ciro joter da pen ta dan yi rubutu, mika mishi tayi tace,

"fita ka samo mana wannan......" cikin sauri ya karɓa ya fita jikinsa yana rawa, ai bai bi ta kan kowa ba yawuce ya fita zuwa pharmacy duk hankalinsa yana can gareta, tsoro yake ji sosai wanda bai san ko na menene ba, gani yake idan ya koma za ace masa ta rasu,

Zuciyar shi na bugawa ya koma gidan bayan ya siyo abunda Dr tace masa wanda drip ne wurin guda shida manya da kanana sai allurai, lokacin da ya koma samu yayi dakin nata cike dasu hajiya da Ammi, suhana, Irfan harda yaya faruk, tana numfashi amma bata ko motsi, shi kam lokacin da ta fadi ma ai kamar numfashinta ɗaukewa yayi haka ya gani, karɓar ledar hannun shi Dr jalila tayi tace su jira su awaje babu matsala insha Allah zata samu lafiya, firfita suka yi gaba dayansu aka barta ta fara kokarin saka mata drip.

Bayan wani dogon lokaci biyu Dr jalila ta fito daga cikin bedroom din, Afeef ta gani yana ta faman kaiwa da kawowa,yana ganin ta fito ya karasa wurinta,

"Dr how is she?"

"she feels better...... A samu dai taci abinci ko babu yawa......"

"thank you....." daga haka ya shiga cikin bedroom din, da kyar ta iya ɗaga kanta ta kalleshi lokacin da ya shiga kananan kaya ne a jikinsa jeans da t shirt wanda suka yi mutukar karɓarshi, gefen gadon ya ƙarasa ya zauna har jikinsa na haduwa da nata, hannunta ya kamo ta fincike da dan guntun karfin da take dauke dashi,

"sannu..... Ya jikin naki?"

Banza yaji tayi masa, a hankali ya kai hannunsa saman goshinta wanda yake zafi ɗau, hannun nashi ta ture, yana kokarin yin magana yaji knocking daga bakin ƙofa, bada izni yayi cewar a shigo nan suhana da Irfan suka shigo harda hajiya tana biye dasu,

" sannu yajiki?" gaba daya suka tambayeta,

"da sauki..... Abinci dai za a kawo mata taci...." ya fada yana kallonta tare da kai hannunsa kan nata ya hada ya riƙe,

"ni bana jin yunwa...." ta fada tana kawar da kanta gefe fuskar ta a daure,

"anty rabon ki da abinci fa tun kafin abin nan ya faru.... Please ki daure kici wani abu" jin abinda suhana ta fada yasa hajiya fadin "zo muje ki kawo mata abinci.... Ai dole taci abinci, haka zata yi ta zama da nufinta?"

Fita suka yi gaba ɗaya suka bar ta da iya Afeef kadai, fuskar ta ya zubawa ido yana ta kallo kamar yau ne ya fara ganin ta wanda tana jin hakan a jikinta...........✍🏻

KAIFI ƊAYA.. ✨
What happens after “happily ever after” gets broken? 💔

After the scandal fades.💔
After the accident steals her steps.💔
After a mother whispers, “Marry another.” 💔

There’s still a man who brings tea at 2 AM. 🩷
There’s still a woman who learns to stand in new ways.😥
There’s still a love called _Kaifi Daya_ - One Blade.❤️

Sharp enough to cut through gossip.
Strong enough to hold two people together. 🫂

If you believe love is not about perfection, but about presence…
This book was written for you. 🤝🗣️

_KAIFI ƊAYA_ - Read it with tissue in one hand, hope in the other........🤪

It's available now 07044644433

#Kaifiɗaya
#lovetriangle
#emotionalromance
#DrMimiAndAfeef

_*Ummi Shatu*_👌🏻
[7/18, 9:02 AM] Oum Jasrah: https://www.arewapen.com/book?id=6a50f2f571e75baab6622006

_A story of scandal, sacrifice and a love that refused to break, a love that says am still here._

KAIFI ƊAYA...!

NA
UMMI A'ISHA

15

***Wani irin baƙon yanayi yake ji a game da ita wanda bai taɓa jin irinsa akan wani ba sai ita kaɗai, na farko jin ta yake tana yawo cikin jinin jikinsa tamkar rayuwar su na manne da juna wuri guda, na biyu kuma wani irin abu mai girma yake ji game da ita shi ba tausayi ba sannan kuma shi ba tsoro ba to menene wannan abun? Shine tambayar da yake ta faman yiwa zuciyarsa amma ya kasa gane ko menene saboda kowanne seconds da awanni jin abun yake yana sake girma, hannunta yaji ta fincike daga cikin nasa har tana kokarin fama ɗaya hannun dake ɗauke da cannula,

"yi a hankali....." ya fada yana sake bude idanuwansa a kanta, babu abinda yake tunawa sai irin yanda ta sandare masa ɗazu ta faɗi a jikinsa shi kansa yasan ba dan yana cikin firgici da tsoro ba ai da an samu matsala, fuskarshi ɗauke da murmushi ya zuba mata ido yana kallonta yayin da ita kuma ta kawar da kanta tare da juya masa baya, wani knocking din ya sake jiyo ana yi nan ya tashi yaje ya bude, suhana ya gani dauke da farfesun kayan ciki da kuma tea acikin dan madaidaicin mug,

"yawwa thank you...." ya fada bayan ya karbi farfesun da tea din, juyawa tayi ta fita shi kuma ya karasa bakin gadon anty Mimi ya zauna,

"tashi ki sha tea din gashi an kawo...."

"ni bana jin yunwa...."

"ko bakya jin yunwa ki dan daure ki sha kici wannan farfesun zaki ji dama dama please ..."

"na ƙoshi...."

"to zan jiraki har zuwa lokacin da zaki ji yunwa sai kici koda kuwa hakan na nufin zan kwana ne anan...."

Kallon sa tayi fuskarta a turbune nan ta ga yana kokarin ajiye tea din da farfesun,yunƙurawa tayi ta tashi zaune ta mika masa hannu alamar ya bata nan ya mika mata ta karɓa ta fara shan tea din tana cin farfesun duk da ba wani dadinsa take jiba dan gaba daya bata da apatite ma, ido ya zuba mata yana kallonta ko kiftawa baya yi kamar wanda yau ne ya fara ganin ta, sai da taji tana kokarin yin amai sannan ta barshi ta mika masa ta sake komawa ta kwanta, jin ana kiran sallar la'asar ya sa shi tashi ya fita zuwa masallaci ana idar da salla ya sake komawa bedroom din nata, a hanya suka yi arba da Ammi wacce itama ta fito daga wurin anty Mimin, a iya saninsa babu wata kunya ko surukanta tsakanin shi da Ammi amma sai ya ji yana dan jin nauyinta yau, har ƙasa ya durkusa ya gaisheta ta amsa cikin kulawa sannan ta wuce shi kuma ya tashi ya shiga wurin anty Mimi wacce ya tarar tana bacci suhana kuma tana gyara mata bedroom din wanda harma ta gama ta kunna turaren wuta dakin ya fara gaurayewa da kamshi mai dadi na turaren bakhoor, fita tayi ta barshi yana tsaye yana kallon anty Mimin bayan fitar suhana ya karasa gefenta ya zauna, hannunta da idan ya kama take ta faman fusgewa tana ture shi yanzun ma hannun ya kama ya riƙe cikin nasa yana murzawa a hankali bayan ya dan hada jikinsa da bayanta kaɗan hannun nata laushi tamkar na jaririn da yazo duniya yanzu fatarsa bata jima tana shan iska ba, duk tayi wani buzu buzu da ita kamar wacce ta shekara tana jinya,wayar shi ya ciro daga aljihu ya saka a silent saboda kar akira shi karar wayar ta tada ita daga wannan daddadan baccin da take yi dan Allah kadai yasan yaushe rabonta da samun bacci, yana nan zaune a gefenta bai matsa ba har sai bayan da aka kira sallar magriba sannan ya tashi ya fita ita kam har lokacin baccin ta take yi ba kakkautawa. Sun fito daga masallaci shida Irfan yaga kamar su Abba da daddynsu harda yaya faruk zasu je duba anty Mimi, bai bisu ba wuri ya samu ya zauna wurin hajiya har sai da suka fito suna maganar basu samu dubata ba ma saboda sun tarar da ita tana bacci sannan ya faki idonsu ya sulale ya koma cikin dakin,
Chapter 19 · 0% Book details